Author : Queen Mamie Category : New Hausa Novels 2026
Gwamma dake d'aki tace "yawwa".
Baba ya sunkwi da kai "yanzu kai bakaji kunyar gayan Maganar nan ba na ko?! ai shike nan dama ai babarka tace bata so kuma nasan ita ta kitsa ma. Amma komi Mutun yayi Shi za ayi mai.
Mudi kam wata jakar bagkoy ya d'auko, ya tsaya "ni na tafi Lagos neman kud'i baba dama yau na tsara tafiyar".
Gwamma ta fito "Yawwa mudi yau ka biyani". Baba yace "ni kam ina Umartar ka A matsayina na Mahaifinka kar kaje duk da nasan ba ka Maidani komai ba." Gwamma tace "wallahi Sayyaje". Mudi ya d'uri jaka yace acan zan hadu da Lawandi ya fice.
Gwamma tayi shewa "Ahayye yaraye nanaye"
Kuka hansai keyi saboda tausayin Baba, tace "Baba kayi hak'ur. Baba yace "bakomi Hansai ina Alfahri dake Allah ya baki miji na gari" ya tashi ya fita.
Haka Malam duk ya sanar an fasa auren nan nan gari ya hau tsogwami anata Gulmace- Gulamace ko fita Hansai tayi sai a fara ga Hansai mai bak'in Jini "da kuka take dawo wa, sai da Malam yaje yayiwa tufkar hanci ,San nan aka sakar Mata Mara.
K'anin Maigari ne dake zaune a kano yazo mai suna Alhaji Salisu, Shi ya tashi a hannun k'anin Babar su Maigari to ita abirni take Aure shiisa ta d'auke Shi ya tashi yayi Boko ,yanzu hakan yana aiki A NNPC Manager ne, yana da 'ya'ya da Mata Biyu.
Zuwansa Gidan ya tarar Ana tak'addama akan Muntari kan ya kafe bazai Auri wata Lantana da Gwoggo ta kawo ya Aura yace tunda anraba Shi da Hansai ba 'yar da zai Aura, to ganin hakan Alhaji Salis yace zai tafi dashi can Birni ya cigaba da karatu ,Jin an ambaci karatu yasa ya Amince zai bishi. bankwana .. .
*BY QUEEN MEEMI* .
[12:55pm, 21/01/2017] 👑Meemi🔸: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜
⚜
❣ ⚜ ⚜❣
⚜
*❣RABUWA CE SANADI❣*
*_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜
❣15❣