Author : Queen Mamie Category : New Hausa Novels 2026
ba,Dan tsaki yayi ya Mike ya d'auko wayarsa Murmushi yayi ganin test msg na husy. Kiranta yayi bugu wajen 3 times bata d'auka ba duk abinda yake tana satar kallonsa can sai ga kiran ya shigo ya kashe ya kira ta.
"Oh my finest ina kika shiga ne??
Kin san ina missn voice naki" Murmushi yayi love u so much babe."
Da alama yana jin dadin hirar.
Murmushi yayi tareda shafo sumarsa "finest anjima zanzo ganin ki domin samun sukuni a Mind d'ina."
Tamkar ta kurma ihu don ta gane da Husy yake waya D'ora hannu tayi aka da k'arfi ta buga bench d'in .
Waigowa yayi Mata kallon raini nan Jikinta ya saki ya dad'e suna waya San nan ya kashe.
"Ke idan bazaki iya aikin nan ba U can go bansan Matsala."
"Sorry sir"
Nan ta fara ko rabi batai ba ta d'ago "12 tayi sir time na Lucture yayi"
"Are u finished?"
"No sir."
"Okey to ya?"
Fari tayi da ido dan samun shiga "bari na k'arasa" nan ta tayi sai 12:30 ta gama ta tafi.
Tana shiga mota ta kifa kai kan sitiyari da Dan tsaki
Fushi taji mai tsanani ji take kamar ta kauda Husy tunani take yanda zata b'ullo sanda taje har an fita daga lucture daga nesa ta gano lubna janta tayi sukaje bakin bishiya.
K'awa "Handsome yak'i saurara ta plssss say Something na rasa idea."
Dariya Lubna tayi "hmm kawai ki sanar mai" Sady tace "so kike ya koreni daga office nashi?"
"Ke dalla zauna nan garin kallon ruwa.....ai abari ya wuce Shike kawo da rabon wani.Sady tace "nifa ban san hakan domin namiji yace yana sonka ma ya Allah ya cika,balle kace kana sonsa."
Lubna ta tab'e baki "nikam itace shawarata" Sady tace "Okey to ta yaya?"
"Kimai text msg tunda yanzu nasan yasan Number d'inki in kuma bai sani ba ki k'ok'arin karb'a ki kirasa ya gane kece wadda ke aiki gunsa kamar one week haka saiki samar mai."
"Good idea lubna" Dadi ne ya kamata suka tafi.
*******
K'arfe Biyar Mukatr na gidan su Hassy suna zaune kusa da flowers kan kujeru suna hira yana son tambayar ta Husy Amma ya kasa sai kallon kofa yake.
Hassy na lura dashi "yadai Muktar? yace "no problem" kurb'ar lemu yayi San nan yayi ta maza ina hussina ne?
"Tana cikin gida tana shiri.cuz bak'onta ne sai zo" dam! yaji gabansa ya fadi .
Kamar da 30 mint haka Maigadi ya wangale gate had'addiyar Motar sa ya danno ta cikin farfajiyr fitowa yayi yau yayi shigar white din jins da tshrt white sai black din shoe sai agogo black can kamar Mintuna sai ga Hussy ta fito cikin shigar Red tayi bala'in kyau wani kwantaccen Murmushi ke fita daga bakinta wushiryarta na K'ara Mata kyau.
tsayawa tayi wani kallo yabita dashi don ta rud'ashi kunyarsa taji tace ina zuwa.
Nan tayi wajen su hassy wani Mahaukacin kishi ne ya kama Muktar zuwan taa yasa ya sunkwi da kai "Tweeny ga Shuriem su gaisa da Muktar" k'ura Mata idanuwa yayi dai de Lokacin shureim ya k'araso gun ya mik'awa Muktar Hannu kamar ya naushe Shi ya keji idanuwansa sunyi ja da k'yar ya mik'a mai Hannu suka gaisa kallon Hussy yayi cikin ido ta d'auke kanta suka bar wajen.
Hassy kuwa da Mamaki take binsa da kallo kamar me domin ganin ya canja mata,cup d'in lemo ya d'auka jikinsa har wani rawa yake cup din ya fadi kasa ya fashe ,rikicewa hassy tayi wai Muktar Menene? Akaro na 2 ta tambayeshi kamar da tsawa yace ta k'yaleshi k'arshema yace zai tafi haka sukayi sallama ba yabo ba fallasa zuciyarsa na tuk'uk'i.
Hassy Asanyaye ta koma gida domin abin yayi Mata ciwo koma meye yake b'oye Mata zata sani.
Husy kuwa ranta yad'an baci duk sai Jikinta yayi sanyi.Shureim kuwa jifanta yake da mayataccen kallon sa Wanda ke d'imauta ta tana Son salon Shureim saboda ko bai Magna ba yasan yanda zai aika sakon sa cikin salo da k'warewa.
"Finest"! ta d'ago "naam"
"wai yaushe zamu zama inuwa d'aya ne ki bani dama Manya su shiga ciki mana" Dariya tasa "har yaushe daren yayi?" Murmushi yayi ashe kin iya magana haka to ai mu Soyayyarmu ta da ban ce bazamu cinye soyayyr awaje ba sai kin zama wife d'ina."
"Nida nake karatu ai sai na gama."
"Anya finest?"
K'ayataccen murmushi ta saki batace komai ba
"Gaskiya finest kina da kyau"
"Har nakai ka?"
"ina wani kyau a namji" tace "hmm haka dai kace.Amma ai kafini kyau."
Satar kallon sa tayi taga yana kallon ta tare da "Lumshe ido finest bakya iya dagowa na kalleki sai de ki ta zuban kalamai ta k'asa ko?
K'unshe kai tayi a gyalenta ta kasa d'agowa tana jin heat nata na fat -fat.
K'arar Msg ne daya shigo wayarta, ya dawo da ita daga duniyar data tafi wayar ta duba k'irjinta ne ya buga ganin abinda ya k'unsa kamar haka:
_Ki sani ba gudu ba ja da baya_
_nayi dakon sonki tun kina k'arama sai wani daga baya zai zo ya k'wacen ke domin ni nake miki true luv ayanzu hakan zan turo iyayena ayita ta k'are_
_Ur husband Muktar_
Kashe wayar tayi gaba d'aya ta d'ago suka had'a Ido da Shuriem "Subhanallah Finest meya faru! Naga idonki hawaye?
Shafawa tayi bata San sun zubo ba "Aa abune ya fad'an ido" "sorry angel" Handkerchief ya zaro ya mik'a Mata ahankali ta karb'a k'amshin sa ya bugeta taji wani sanyin dad'i ta share yace "finest bari na tafi na barki ki huta kinji?"
Tace tam wani sansa taji ya k'ara shiga ranta afuskarsa taga damuwa sai data shigar sa mota ya d'ago Mata hannu San nan ta tafi.
Bata taba sanin zata so wani bayan Muktar ba sai gashi ahankali son Shureim ke shigarta ,da gudu ta shige gida ta haye saman bene domin taga ba kowa afalon k'asa d'akunasu ta shige tayi ruf da ciki tana kuka kamar me.
Hassy ce ta shigo itama idanuwan ta yayi ja da sauri ta k'arasa "sis meye? husy ta dago "bakomi dear ke ma meyasa kike kuka" hassy tace kinga abinda Muktar yayi mani ko nikam inaga zan hk'r dashi ba dole dama wasu Mazan Mayaudara ne."
Gaban Husy ne ya fad'i "tweeny nima abinda ya sani kuka kenan domin ni dake d'aya ne abinda ya faru dake tamkar dani ya faru" Rungume juna sukayi suna kuka.
Bayan sun tsagaita
Hassy tace "sis na tafi Mum na kitchen" tace "nima gani nan."
K'arar Ringtone na wayarta ne ya buga nan d'auka ta duba taga sabuwar Nomber ce Da sallama ta amsa wayar. "Yar aikin gidan mu ki sani Karona dake bazaiyi kyau ba wlh, ko ta halin k'ak'a sai na rabaki da Handsome saboda dani ya dace wlh na dai gaya miki."
Kan tayi magana ta kashe Tabbas tasan Sady ce sai Duk barazanar da zatai bata tsoro ba,ayanda takeji bazata iya ba Shuriem ba kuma in ta rabu da Shuriem kamar ta bawa muktar k'ofa ne ga kuma Tweeny dole ta shiga damuwa wullar da wayar tayi cike da haushi domin ji take kamar tasa ihu.
*Waye Shuriem*
Shuriem d'ane a gidan Alhaji Kabeer da hajiya Khadija. Alhaji kabeer shahararren D'an kwangila ne wanda yake samu ta hakan ,inda kuma yake kasuwanci ya tab'a rik'e Muk'amai a gwabnatin tarayyya San nan yana da Company anan Abuja da sauran Jahohi ayanzu hakan yayi ritaya shureim shike gudanar da duk harkokin sa.
Shureim shine d'a na biyu a Gidan su, inda yake da yaya Mace Maryam dake Aure a lagos sai k'anwar sa Nawwara itama tana Aure anan Abujar sai Autansu Sadiq dake karatu.
Yayi karatunsa a Oxford University inda ya karanci Accounting bayan ya kammala ne sai Mahaifinsa ya bashi Ragamar komai nasa ganin ba irin nan ya karanta ba, bai San wasu kasuwancin ba, yasa yayi wani Course a uniAbuja kan Bussness.
Allah ya bashi farin jinin Mata sai de duk basi mai domin Shi bai san mace tace tana sonsa ,shiisa ma duk masu sonsa baya kulasu don basi masa ba.
'Yan Mata da yawa wasu har gida suke binsa wasu office Musamm Mata masu kwad'ayi ganin yana tashen Naira wasu kuma don kyansa.
Shuriem yana da son tsafta ga da son turare da son Fararen kaya bai da Magana sosai sai Murmushi kad'an kenan daga Shuriem.
Tunda Muktar ya koma kano yake cike da damuwa duk ya canja ganin hakan yasa yatafi Mangalu domin zuwa gun Malam don ya taimaka mai
To fa muje zuwa.
by Queen meemi👑
.
[2:04pm, 13/03/2017] 👑Meemi💋: . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜
⚜
❣ ⚜ ⚜❣
⚜
*❣RABUWA CE SANADI❣*
*_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜
❣50❣
*March 2017*
_Sadaukarwa ce Ga basher Usman Family's_
_*Wan nan page din naku ne Maman haneef ,Maryam oumey, Ameera Mahmoud,Maman rahma,Rabia Alhasan, Nana fiddausi, Muhfaz,Maryam Ahmad,nabila ladan,Maman yasmeen & Zeenat tukur. Tnz❤*_
******
*Mangalu@11am*
"Ya kamata ace kayi Aure haka Muntari" cewar Goggo "ai Goggo da Maganar nazo ma shiisa nazo ma ayita kare."
"Hakan shine dai-de Muntari gashi nan duk sa aninka da yara a ina yarinyar take ne?"
"Ai gogga kinma Santa Hansai ce fa" Goggo ta zaro ido haba idan d'a ya manta ai uwar d'a bata manta ba kamanta baya yanda mukai musu mukace bata da asali ai yanzu muka je sai ace don ance iyayenta masu kud'i ne kwad'ayi ya kaimu."
"Goggo ataimaka" suna cikin Maganar Maigari ya shigo "Aa Muntari hira kuke ne? gogg tace aifa kajimin d'a wai Hansai yakeso anema mai Aure ai da kunya mukoma."
Maigari yace "too nikam bazan shigema gaba ba sai de in wata ce Amma ai da kunya."
Kamar yayi kuka ya tashi ya fita sai gaisawa suke da tsofffin abokansa nada sai sha'awarsa suke suna dama suma sunyi karatu bai Zame ko inaba sai gidan Malam,yana k'ofar gida tsaye suna hira da wani Mutum.
Dan tsayawa yayi suka gaisa kan Mutumin ya tafi Malam yace "Muntari Kaine a gari?" "eh wlh Malam dama magana nazo da ita kan husaina."
"to wata matsalar ne?" Muntari ya sosa kai "dama Aurenta nake so akaro na biyu." murmushi Malam yayi masha Allah amma ai Muntari ai an bar Maganar tun abaya ko ka manta maigari yace Aa, ai maganar bai dace ka Taso da ita ba domin ni inada taka tsan- tsan balle yanzu ma kaga ba a guri na take ba ,ina Baka shawara ka hak'r ka nemi wata tunda kaga ba'ai Auren ba to ba Alheri duk wacce kake so zan shige ma gaba."
Tunda Malam ya fara magana Yake zufa kamar me idon sa yayi ja yace "Malam ngd Allah ya saka" akasalance ya mik'e ya tafi Malam ya bishi da kallo cike da tausayi.
*Abuja@ 4:00pm*
Tsaye Husy suke itada hassy zasu Super Market goslow ne ahanyar yasa suka tsaya da yake yau weekend duk Motoci na fita wasu zasu visiting Akusa da motar su Sady ce itada Lubna. Lubnan ce ta fara ganin su Ta nunawa Sady alokcin aka bada hand nan suka fafara Sady ta bisu abaya har sukaje Super Market d'in.
Firfitowa sukai shiga iri daya sukai nan suka shiga Sukayi side na makeup da perfumes,yana tsaye yana duba wasu lates agogwaye wajen yana gefe.
Shiya fara ganinsu wani k'ayataccen Murmushin sa yasaki.Hankulan su Husy na kan d'aukar abinda sukeso ji tayi kawai an k'arfe basket ta d'ago suka hada ido atare suka sakar wa juna Murmushi "Finest da nasan zakuzo siyayya ai Dana Zo na d'aukeki ban san kowa yana gane wan nan fuskar."
Murmushi tayi "Habibi kenan barka da yamma." "bana amsawa sai yanzu ma zaki gaidani." "Kaina bisa wuyana habibi"
Murmushi yayi ahankali yad'an sunkuyo kamar zai d'au Abu iluv u Swt finest."
Lokacin Hassy ta k'araso gurin perfumes din ta gama da Makeup site Dan dariya ta saki "Aa kice da Masoyin aka hadu."
Su Sady kuwa sai A lokacin suka k'araso suma suka shiga karaf idanuwan Sady yakai kan Handsome dake rike da Basket na husy wani Mahaukacin kishi ne ya deb'ea taje ta wanke Hussy da mari mai zafi.
'yar k'ara ta saki saboda zafi da sauri ta kalli wacce ta mareta ganin Sady yasa ta matso kan ta rama taji an wanke Sadyn da mari.
itama an bata wani dagowa tayi sukai ido hudu da Handsome yana wuci "ke kina da Mental problem ne?"
Zaki zo kimare ta d'an karamin tsaki yayi bansan problem wlh. Hassy kuwa sai harare harare suke da Sady "anji kunya ba ason mutum ya nace ."
Jan hannun lubna Sady tayi ta kalli hassy "dani kuke zancen."
har sun fita Lubna ta dawo tayi side da Shuriem yake don itama yana birgeta Amma tunda k'awarta ta rigata dole ta basar.wani kallon Shureim tayi Tace Sady me k'aunarka ce domin babu wacce takaita sonka kuma sai inda mammu ya k'are",da sauri tafita don ganin yanda yake huci.
Hanunn sa ya daka ganin yanda husy ke zubar hawaye "sorry My Queen" da k'yar ya lallasheta yayi counting suka fito sai day aga tafiyar su San nan ya shiga Motar sa ya tafi.
*Monday @ 8:09*
Da k'yar Sady ta shiga office d'in cike da tsoro burki taja domin yau shigan da yayi yafi na jiya abinda ke dada rudarta gashi kenan akwai tsafta da ado.
"Morning sir"
Bai d'ago ba sai ma D'an.Rubutunsa da yake yana waya ta dad'e a zaune ganin hakan yasa. Tayivta maza tace "sir aikin."
Wani wulak'antaccen kallo yayi Mata tare da Murmushi ta gefen Lips nasa yace "ke!
Get out of my office"
"Sorry sir wlh bazan kuma ba wlh dama tsautsayi ne wlh."
Kuka ta fara shab'e -shab'e plss sir bazan kuma ba kallonta kawai yake yana juya kujerar sa ,da mamaki fal zuciyar sa wai sonsa take sai yanzu ya gane dalilin neman aikin ta D'an tsaki yasa I said get out of my office yaune last da zan K'ara ganin ki a office na kin gane."
Jakarta ta tad'auka "pleaes sir!"
"Security"
Da sauri yazo nan Shureim ya nuna Sady "fitar da wan nan karka barta har sai kaga tabar harabar Companyna."
Da gudu ta fita Sucurity na binta ta galla mai harara "Malam sai ka k'yakeni haka ko! Tunda ba maula nazo ba" nan ta shige Motarta ta kwasa aguje.
Tana ta fiya tana kuka gefen titi ta tsaya tana dukan sitiyari tayi "wlh dole ka soni Shuriem bazan barka ba akan wan nan kile war kwanan nan zakana wulaknta ni, ke kuma husy sai kin gwammace kid'a da karatu.
*************
Kwana 2 hassy ta rage neman Muktar don Jan ajinta .yau ma suna zaune Dady ya shigo duk suka mai barka da zuwa "yawwa dama ke husaina da hasna inason sanar daku ba daku za a koma London ba saboda Na dawo da karatunku nan abuja a uniAbj saboda Suhaima kar mu tafi mu barta ita daya duk da ga Anty . Mum naku kawai zamu tafi da ita sai Arif."
Hassy kamar zata sa kuka "Dady yanzu mu kad'ai zamu zauna a wanga memen gidan nan! Yace habadai Goggo zata zo Ita zata zauna daku( k'anwar Maman sa ce)akwai dalilai ne Amma idan be muku ba sai mu tafi ke Hussyna me kikace?"
"Dady zamu zauna d'in Allah yasa hakan yafi Alheri" "Yawwa 'yar Dady."
Mum tace nima fa nafi san zaman nan Dady yayi Mata wani kallo Wanda shiyasan ma'anarsa kauda kai tayi "to my twinss ku Kula banda shirmen k'awaye ku zama masu kula kun gane?,bamu yarje muku kawo ko wane saurayi yazo zance gunku ba, illah ke Hassy Muktar ke kuma husy Shuriem su na sani suna zuwa.ban yarda ku tsaya da wasu ba bayansu suma din ku kiyaye."
Sukace "tam Mum."
Dady yace kowaccen ku level data ke shi zata cigaba ke Hassy dake level 2 nan zaki shiga haka ke Husy dake 1 Kema nan zaki shiga."
Arif dariya yasa yana musu gwalo harara suka kai mai ya gudu Dady yace "sarkin tsokna.Yanzu jibi zamu tafi Gobe Goggo zata zo ga Idi nan kun san dai amanar dake tsakanin mu dashi tamkar Dan gida duk wani babban abu da kuke so kwa bashi yana sayo muku ,zai dawo nan suna kwana a boys quaters saboda tsaro." Nan duk ya sallamesu suka haye sama.
*Washegari @12am*
Sai ga Goggo ta iso da murna suka tare ta tace kai ni karku karya ni ina kakarku" Mum tafito Aagogoji kece? Sannu da zuwa"