MASARAUTAR KAIZUR COMPLETE BY NUSY BEE.doc

Author :  Nusy Bee Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   3 / 11

6K to 9K   out of 31.5K words

daga idanunta

Lokaci guda zuciyar sarki Iyaad ta buga sakamakon tuna wannan asarar da ya yi,amma sai ya dake,ya dube ta cikin tausasawa,da Muryar lallashi ya fara faWin

"?ata!

Ki yi ha?uri da rayuwa,ki kasance mai yafiya da tausasawa

Mu masu jihadi ne, waWanda suke ya?i don Waukaka kalmar Allah,ashe idan haka ne mutuwa rahama ce a gare mu

Raki ne,ko na ce kai ?arar Allah,ashe a matsayin mu na musulmai sai mun yarda da cewa shahada a wajen ya?i ita ma nasara ce sannan za mu cim ma nasara?

Ba mu faWi ba, kamar yadda Allah ya faWa a Alkur'ani ba mu rasa shahidanmu ba,ciki kuwa har da Wan'uwanki

Hayat!wannan ba lokacin Waukar fansa bane, lokaci ne na godiya ga Allah,zuwa gobe za'a la?ana wa ribatattun ya?in mu kalmar shahada,muna fatan gaba Waya za su musulunta,daga wannan lokacin za muyi musu Barka da shiga musulunci ne,ba fansa za mu Wauka kamar yadda kika ce ba,in sha Allah"

Sake rissinawa ta yi,cikin girmamawa ta ce "ka gafarce ni abbana!

Tabbas na yi kuskure, don ban san da wannan tsarin da kuka yi ba,nima kamar ku ina farin cikin samun ?aruwar musulunci,sai dai Abba ina neman afuwarka

Idan bai karSi addini ba ya kamata a ?addamar masa da hukuncin kisa kamar yadda aka yiwa sauran ?an uwanshi "

Dan murmushi sarki Iyaad ya yi,ya ce"ina fatan ya karSi addinin ma, ?aruwar musulunci yana sama da komai"Wan murmushi ta yi ta ce"haka ne, Allah ya ba ka nasara abbana"

Dafa kanta ya yi yana murmushi ya ce"na bar ki lafiya ?ata"daga haka ya juya ya fice daga Wakin, kuyanginta da ke tsaye suna jiran fitowar shi suka rissina,sannan suka koma zuwa cikin Wakin






TSIBIRIN GAYUR,FADAR SARKIN ALJANU

?aton tsauni ne,mai tsawo na tsawon mil biyu, faWi kuwa ya kai mil huWu a tangamemen tsibirin na gayur,inda fadar sarkin aljanu yake mulki,wato SARKI LAIMUS






#Nusy_bee
08125952284

=????=?Q? MASARAUTAR KAIZUR =????=?Q?






'?Nusy bee
d'? Young talented writers association YOTA d'?


(Under YOTA'S AMAZING PENS)



Page 4



A kaf nahiyar aljanu shine mai ?arfin faWa a ji, saboda tarin dukiya,da tarin maya?an aljanu da yake da su

Shine Sarkin musulman aljanu,kuma limaminsu,a duk duniya babu wata masarauta ko daular kafirai da bai ya?a ya ga bayanta ba,banda Waya,wato Daular Baruda


A kowanne lokaci tsawon shekaru ashirin sarki Laimus ya kasa sukuni saboda ba?in ciki da Wacin zuciyar da yake ciki na rashin nasara,ko cika al?awarin da ya Wauka sama da shekaru Wari da goma baya, shiyasa ya yi duk iya yinshi,amma tasirin sarki Akaal a wancan lokacin ya shafe nashi,duk da kasancewar sarki Akaal mutum,amma manyan matsafan aljanun da yake tare da su daga wasu nahiyoyin na duniya sun shafe jarumtarshi

Wannan kenan!





=???

Shiru fadar ta Wauka,ana sauraren sa?on da Wan aiken sarki Laimus,wato Shabbir ya kawo, lokaci guda kuma fadar ta ruWe da sowar murna da farin ciki,sarki Laimus da annuri ya cika fuskarshi ya dubi Shabbir da fara'a ya ce"Shabbir!

Yanzu kana nufin daular Baruda ta ruguje kenan?babu sarki Akaal a raye?"

Shabbir cikin girmamawa ya ce"haka ne ya shugaba na!"

Sarki Laimus ya ce"Allahu Akbar!to ya batun sarkin ya?i Anudu da mafarauci Murad?"

Shabbir ya sake rissinawa ya ce"dukkansu sadaukin sarki Iyaad ya shafe labarin su ya shugaba na!"

Kabbara mai ?arfi ta ratsa fadar,kowa fuskarshi Wauke da murmushi,sarki ya ce"kuma da gaske ajiyarmu tana cikin garin aminci Daular Tayaar?"

Shabbir ya jinjina kai cike da girmamawa ya ce"haka ne ya shugaba na!

Sai dai akwai wani hanzari ba gudu ba"

Shiru fadar ta yi ana sauraren Shabbir,sarki Laimus ya ce"ina saurarenka amintacce na"

Shabbir ya gyara zama ya ce"a halin yanzu ajiyarmu baya addinin mu kamar yadda muka sani,kuma babu yiyuwar zai koma Win, saboda tsanar musulunci da musulmai sune abubuwa mafi girma da ake rainon duk wani Wa a daular Baruda

Sannan Kamar yadda muka san jinin SUHAIF BIN YASSAR suna da kafiya da tsatstsauran ra'ayi,to shima ajiyarmu yana da wannan gadon"

Murmushi sarki Laimus ya yi,ya dubi Shabbir ya ce"duk wannan mai sau?i ne,kuma mai wucewa ne

Na san sarki Iyaad sosai,sarki ne mai adalci,kuma a ko'ina aka samu adalci ana samun nasara,don haka mu zuba ido kawai,mu taya shi da addu'a,amma tabbas sarki Iyaad zai ?arasa abin da ya fara, kamar yadda ya yi abin da ya gagare mu a baya"

"Ina fatan haka ya shugaba na"a cewar Shabbir yana murmushi





*DAULAR TAYAAR*

washe gari ta kama juma'a, Kamar yadda ya zama al'ada a daular Tayaar sarki Iyaad ne yake jagorantar sallar juma'a ta ?arshen kowanne watan Musulunci idan ya kama,to yau ma haka ne, kasancewar yau ta kama ashirin da bakwai ga watan Safar ya zama shine zai jagoranci sallar juma'ar

Gashi kuma a yau ne za'a la?anawa ribatattun ya?in da aka kamo daga daular Baruda kalmar shahada,ga waWanda suka yi turjiya kuma a ?arar da rayuwarsu, kamar yadda yake doka a ?asar ta Tayaar

Kuma a yau ne za'a yi liyafar murna ta wannan gagarumar nasarar da aka samu,irin wadda ba'a taSa samu ba,asalima babu wata daula da ta taSa karawa da Baruda ta samu nasara,sai dai ko Baruda ta yi nasara ko a yi kunnen doki

Daidai farkon mukhtarin sallar azahar Sarki Iyaad ya fito don ya jagoranci sallar juma'a,kuma ba tare da Sata lokaci ba ya hau mumbari don fara huWubar sallar juma'a

Dakaru ne suka gabato da ribatattun ya?i zuwa gaban masallatan, waWanda suka yi ?asa da kai cikin jin ?as?anci

Ba'a Wauki dogon lokaci ba aka idar da sallar juma'a,daga nan limamin Masallacin ya gudanar da jawabai masu ratsa zuciya,a ?arshe ya tambayi ribatattun ya?in shin sun amince da Allah shi ne abin bauta?

Kuma Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama bawanshi ne?

Ba tare da Sata lokaci ba suka ce sun yarda,take liman ya la?aba musu kalmar shahada,suka maimaita,take wajen ya Wauki kabbara mai ?arfi,bayan an nutsa liman ya cigaba da jawabi

"Kamar yadda na faWa Allah Waya ake bautawa,rana da wata,da kogin Baruda da kuke bautawa dukkansu alama ce ta wanzuwar Ubangijin talikai, ayoyi ne daga ayoyinshi,ya yi su ne don mu ?ara iymani,ba don mu rasa shi ba

Muna yi muku Barka da shigowa Musulunci, Allah ya ?ara mana iymani baki Waya,ya ba mu rabo mai albarka"daga nan dakaru suka wuce da su don a koya musu al'amuran musulunci

Daga nan sai babban aiki,wato jin ra'ayin sadauki Kazuzi kan batun addinin Musulunci,wanda tunda aka kawo shi garin Tayaar har zuwa yanzu bai saka ko da ruwa a bakinshi ba,babu wanda zai iya cewa ya ga ko da ?wayar idanunshi da suka kasance a rufe a kowanne lokaci aka ziyarce shi,mutane da yawa sun ayyana hakan a matsayin borin kunya,duba da cewa ba'a taSa samun ko da kwatankwacin nasara akansa ba,kai tsaye yake ayyana dakarun da suka tunkare shi don ya?ar shi da sunan mata

Sarkin ya?i da jama'ar shi ne suka fito da shi daga Wakin hukunci,har lokacin babu wanda ya yiwa magana,babu wani yun?uri da ya yi banda abin da aka saka shi ya yi

A gaban sarki Iyaad da limamin babban masallacin daular Tayaar aka gurfanar da shi,kamar koda yaushe kanshi a ?asa,liman ya dube shi ba tare da wata shakka ko tsoro Ba ya ce

"Sadauki Kazuzi!

Muna yi maka Barka da zuwa daular Tayaar,Wauka mai cike da adalci da girmama Wan adam,muna yi maka fatan samun rabo mai girma,a don haka muke yi maka tayin shiga mafificin addini, addinin lumana,addinin zaman lafiya,wato addinin musulunci,menene ra'ayinka akan hakan?"

Shiru ya ziyarci wajen,gaba Waya jama'ar da ke wajen suka yi shiru suna jiran jin ra'ayin Kazuzi akan batun da liman ya zo masa da shi,sai dai har bayan shuWewar wasu da?i?u babu alamun zai yi magana,wanda hakan ya kaWa hanjin wasu daga cikin jama'ar, liman ya sake dubanshi cikin sarewa,amma ya dake ya ce"kai muke saurare Kazuzi!"

Nan ma dai shiru babu amsa, Sarkin ya?i ya dubi Sarki Iyaad don jin ra'ayinshi,sarki Iyaad ya Wan girgiza kai ya ce"a sake ba shi lokaci,duk da cewa ba mu san abin da ya saka shi yin shirun ba,amma nan gaba muna fatan ya magantu,kuma mu ji alkhairi daga gare shi

Da haka taron ya watse ran jama'a da yawa babu daWi,don wasu sun so ya musulunta,wasu kuma sun so an ?arar da rayuwarshi, cikinsu har da Hayat wadda ta koma cikin turakar ta a fusace,ta kori dukan kuyanginta ,ta fizge lulluSinta ya jefar,sannan ta haye gadonta tana hargitsa dogon gashinta

Mi?ewa ta yi a fusace, ba tare da tunanin komai ba ta fito daga Wakin, kuyanginta suka rufa mata baya,kai tsaye ta nufi inda keken dokinta yake,ta shiga, kuyanginta suka bi ta,kai tsaye ta nufi Wakin hukunci

A fusace ta ?arasa inda dakarun suke,ganin yadda ta zo a fusace suka yi azamar buWe mata ?ofa ba tare da ta yi magana ba,kai tsaye ta afka Wakin a tsananin fusace

Yana zaune a inda ya saba zama,sai dai yau saSanin koyaushe yana zaune a jikin bango Ya jinginar da kanshi, hannayenshi da ?afafunshi Waure da manyan sar?o?in da har yanzu ba'a raba shi da su ba,tana zuwa ba tare da tunanin komai ba ta cafki gashin kanshi ta shiga jijjiga kan nashi da ?arfin tsiya,tana haWa kan nashi da bangon Wakin da yake jingine,amma ko buWe idanun nashi bai yi ba ballantana ya nuna ya san abin da take yi

Sai da ta yi mai isar ta sannan ta hankaWa shi,kanshi ya sake dukan bango ya bayar da wani sauti,su kansu kuyangin nata da dakarun da suka biyo ta sun tsorata da wannan fusatar tata,ta fara magana a kausashe

"Baka jin magana?

Har yanzu kana jin kanka a wata tsiya bayan duk wani alkadari naka ya karye?

Ka yi faWuwar ba?ar tasa!daga yadda kake jin kanka a matsayin Sadauki zuwa bawa,bawan ma ?as?antacce?har yanzu kana jin kana da wani tasiri?"shiru ta yi tana jan numfashi a fusace,a yayin da Wakin ya yi shiru kamar ruwa ya cinye su

"Na ba ka nan da gobe da za'a sake jin ra'ayinka!ka amsa cewa ka musulunta,ko kuma ni da kaina na raba kanka da gangar jikinka!!!

So nake ka ji cewa duk wata ji kima da iko da izza da ka nuna sun rushe, saboda a ?arshe mace ce ta raba ranka da gangar jikinka!!

Ya rage naka ka zaSi izza ta halaka ka,ko ka saukar da kai,ka Wauki hakan a matsayin gargaWi na ?arshe"tana kai wa nan ta mi?e a fusace tana take ?afarshi,ta yi waje, suma sauran dakarun suka bi bayan ta

Sai da ta fice daga cikin Wakin Kazuzi ya buWe lumsassun idanunshi yana bin hanyar da ta bi da kallo,bai taSa jin zafin maganar da take gaya masa ba ko ya saka ta a rai ta dame shi,asalima tun daga sanda ya rasa wadda yake jin don ita yake rayuwa gaba Waya duniyar ta fice masa a rai,amma yana ganin zai yi maganin wannan yarinyar da take damunshi da hayaniya

Ita kuwa gimbiya Hayat gargaWi mai ?arfi ta yiwa kuyanginta da dakaru akan su kiyayi sanar da mahaifinta abin da ta yi,don tsanar Kazuzi ce dai babu wanda zai iya hana ta yi,kuma muddin tana numfashi sai ta ga bayanshi, shiyasa bata fatan ya amshi musulunci ma

Da yamma aka gudanar da gagarumar liyafa ta nasarar wannan gagarumin ya?i,da addu'ar Allah ya haska zuciyar sadauki Kazuzi shima ya amshi musulunci Kamar yadda sauran dakarun Baruda da aka kama suka yi

Ita dai gimbiya Hayat bata halarci taron ba,ta aika a gayawa sarki Iyaad cewa bata jin daWi





*DAULAR KAIZUR*

"Barka da wannan lokaci ya shugaba na!"

?aga idanu sarki Mu'iz ya yi yana kallon sarauniya Amna da ta du?ar da kai ?asa tana jiran amsa,a hankali ya furta "Barka da zuwa sarauniyar kaizur"

Sauke numfashi ta yi tana gyara zama a gabanshi,daga yadda ya ga fuskarta ya tabbatar da cewa akwai damuwa, cikin kwantar da murya ya ce"da wani abu ne sarauniya?"

Jan numfashi ta yi, lokaci guda rauninta ya bayyana, cikin rawar murya ta ce"na yi mafarki da Yariman kaizur ne ranka ya daWe!

Ha?i?a yarima yana cikin wani hali mai wuyar fassarawa"

Gaban sarki Mu'iz ya buga,dama ya yi tunanin hakan zata faru,a duk lokacin da wani mummunan abu zai samu yarima Sahal sai sarauniya ta ji a jikinta ko ta gani a mafarkinta,hakan kuma yana tasiri sosai a gare ta

Cikin kwantar da murya ya ce "baya cikin kowanne hali sai alkhairi da izinin Allah

Nima na yi mafarki da shi yana cikin kyakykyawan yanayi,har ma ya sanar da ni a tsammaci dawowarshi nan kusa zuwa sarautar shi in sha Allah "

Murmushi sarauniya Amna ta yi, hawaye suka cika idanunta, cikin sanyin murya ta ce"kwantar min da hankali kake yi ya shugaba na?

Hankalina ba zai iya kwanciya ba har sanda zan ga yarima na ya dawo cikin masarautar nan, ka san yadda nake ji,ina jin zafin cin amanar da aka yi min aka fitar da Yarima daga cikin masarautar nan"zuwa yanzu kuka take yi sosai

Dafa kafaWarta Sarki Mu'iz ya yi, cikin ban baki da lallashi ya fara magana "kowacce rayuwa ta Wan adam akwai jarrabawa,ki ?addara haka tamu jarrabawar take, shekaru ashirin kenan da Satan yarima Sahal,a tsawon waWannan shekarun ban taSa fitar da rai cewa zai dawo gare ni ba,

Na hukunta dukkan masu laifi,na yanke hukuncin kisa ga waWanda na kama dumu dumu da aikata laifin,amma hakan bai bayyana min yarima ba,dole na bar wa Allah komai,damuwa da tashin hankali babu abin da za su ?ara yi sai dagula lissafi

Babu abin da nake tunawa na yi ba?in ciki irin waccan ba?ar azzalumar"sarauniya Amna ta Wago kai a sanyaye ta ce"wacce azzalumar?"

"Wadda take amsar hukunci tsawon shekaru ashirin,amma har yanzu babu abin da ya sauya zani"

Sauke numfashi sarauniya ta yi,a hankali ta ce"Ni kuma sai nake ganin kamar babu laifinta, saboda dole zata yi raunin da ba zata iya hakan ba"

Girgiza kai sarki Mu'iz ya yi, ya ce"ta amsa da bakinta cewa ita ce,amma a yadda na fuskanta akwai waWanda suka saka ta,su nake so na sani kafin na yanke hukuncin "

Gimbiya Amna ta jinjina kai cike da gamsuwa ta ce"fatan nasara ya shugaba na, Allah ya dur?usar da ma?iyanka ya ?as?antar da su a gabanka "

Sarki Mu'iz ya yi murmushin bayar da ?warin gwiwa, sarauniya Amna ta rissina ta ce"na bar ka Lafiya ya shugaba na"daga haka ta mi?e cikin nutsuwarta ta fice daga Wakin,bayan sarki ya sallame ta






*Ga masu sha'awar VIP group an buWe,ku tuntuSe ni a number ta gata nan a ?asa*


#Nusy_bee
08125952284


=?Q?=???? MASARAUTAR KAIZUR =????=?Q?






'?Nusy bee
d'? Young talented writers association YOTA d'?


(Under YOTA'S AMAZING PENS)




Page 6




Tana daf da sauke takobin a tsakiyar kan Kazuzi,wanda yake zaune kawai ba tare ya yi wani yun?uri don kare kanshi ba,kuma har yanzu ko kallon sashen da take bai yi ba,kawai ta ji an ri?e hannunta ?am

A hargitse ta juya don ganin wanene ya yi mata wannan shishshigin,da tsananin mamaki da kaWuwa take kallon mahaifinta sarki Iyaad da fuskarsa take a matu?ar haWe tamkar hadarin da ya gangamo yake daf da fara zubar da ruwa, ba tare da ya yi magana ba ya fincike ta, bai yi wata-wata ba ya Waga hannu da niyyar sauke mata mari,amma ya ji an ri?e masa hannun

Da tsananin mamaki ya Wago yana kallon Kazuzi da ya ri?e masa hannun,ba shi ba ma,duka ilahirin dakarun da kuyangin da ke tsaye kallon Kazuzi suke yi da tsananin mamaki,ya dur?usa a gaban sarki Iyaad yana faWin

"Ka gafarce ni ya shugaba na!mace ce,duk inda mace take ana son a Waga mata ?afa saboda rauninsu"ya faWa kanshi a ?asa

A hankali sarki Iyaad ya sauke hannunshi,a wani irin fusace Hayat ta ce"ina ruwanka da abin da ya shafe ni da abbana?

Me ya kai ka shiga tsakani na da uba na tunda kai ka yi silar barin mahaifiya ta duniya?

Kai musiba ne,kuma ibtila'i ga rayuwa ta! menene dalilin da ya sa za ka rin?a shiga abun da babu ruwan ka?zindi?i kafiri azzalumi?? menene......"

"Hayat!!!"sarki Iyaad ya daka mata tsawa,ta kalle shi da rinannun idanunta,sannan ta sake mayar da hankalinta ga Kazuzi da kanshi yake ?asa har yanzu,babu alamun ya san abin da take cewa a kan fuskarshi,bata damu ba ta cigaba da faWin "karo na farko kenan da mahaifina ya Waga hannu da zummar duka na, karo na farko kenan da mahaifina ya daka min tsawa,kuma duka a gaban hadimai na!!!

Saboda kai,kai dai,na yi maka al?awarin sai na wula?anta rayuwarka,tabbas hakan ba zai tafi a banza ba"tana kai wa nan ta juya ta fice daga Wakin tana hawaye,hadimanta suka rufa mata baya,sarki Iyaad ya bi ta da kallo yana Wan murmushi

Shima bai sake magana ba ya juya ya fice daga Wakin,ragowar dakarun da suke tsaye a Wakin suka bi bayanshi, suka bar Kazuzi a zaune kanshi a ?asa

Kai tsaye Wakinta ta shige bayan ta kori kuyanginta,ta faWa kan gadonta tana kuka sosai,bata taSa jin ta tsani wani mahaluki a rayuwarta ba kwatankwacin yadda take jin tsanar sadauki Kazuzi,kuma al?awari ta Waukarwa kanta tabbas sai ta ga bayanshi

Tana ta kuka bata san da shigowar sarki Iyaad ba ma,sai da ya sanya hannu ya Wago ta,tana kuka sosai,ya zaunar da ita yana magana cikin taushin murya

"Allah ya huci zuciyar gimbiyar Tayaar, albarka kuma alfaharin Tayaar,kuma jinin sarki Iyaad,ki yi ha?uri ki daina kukan nan,za muyi magana"

Ba tare da ta tanka ba ta kama goge hawayenta,sai da ta goge hawayen sannan ta kalli sarki Iyaad cikin raunin murya ta ce"Abby na tsane shi tsana mafi muni

Menene dalilin da ya sa tunda ya shigo cikin Tayaar na daina farin ciki ne?

Abby ka yanke masa hukunci, idan ba za ka yanke masa hukunci ba ka kore shi ya bar garin nan,na tsane shi,na tsani ganinshi,bana ?aunar na tuna cewa akwai wata halitta da ta wanzu a cikin masarautar Tayaar wadda take amsa sunan Kazuzi"

Murmushi sosai sarki Iyaad ya yi yana ri?o hannunta,a ranshi yana sake yarda da maganar Kazuzi da yake cewa mata suna da raunin da ya cancanci a Waga musu ?afa saboda shi,ya ce"tashi mu yi magana ?ata"

Babu musu ta tashi zaune tana goge idanu,sarki Iyaad ya dube ta sosai ya ce"yanzu wacce shawara gare ki da kike ganin za'a yiwa Kazuzi?

Kar ki manta daular Tayaar a duk nahiyar nan babu wani gari wanda yake faWa da zalunci irin namu, alhamdulillahi kuma muna yin nasara

Ba mu kawo Kazuzi cikin daular Tayaar ba sai don mu cusa masa sha'awar musulunci, tunda kamar yadda muka sani musulunci ba'a yin shi da dole,kuma ko da

3 / 11