Author : Nana Hafsatu Category : Love Story
°°°°°
Zaune suke baki daya sai ga waya akan kira number Ashfeef ance suje asibitin Naduka na gwamnati bangaren yan accident da quna.
Suna zuwa suka tarar da wata leda an nannade da kyalle. Tamkar an Kona takarda ta yayyanke dinnan tayi baki tayi toka.
"Menene wannan din?" Ashfeef ya tanbayan bakinsa bude ..
Sauran kuwa suka kasa magana.
Daya daga cikin maaikatan wajen yace,
" sunyi hatsari ne da wata tankar mai sun kone baki daya. Su bama a gane komai nasu. Kai ma dakyar aka samu wani dan area ku ya bada number ka .... "
"Bangane ba 'da na. Me yake faruwa? Konuwar me? . Motar mai kuma?" bappah Auwalu ya tambaya baki daya kamar mahaukaci yama rasa mai zai ce.
Gaban Nawraah ya tsananta bugawa tammar zai zullo ya fado,
Maaikacin yace.
"Bayan dogon binciike da mukai.Sunan sa Ashir junaidu. Ko daga Naduka zone.. Allah ya masa rasuwa"
Diiiiim komai ya dauke. Tamkar duniyar ta tsaya chak.baki daya haka suka zama tamkar mutum mutumi dukkanin su aka rasa mai cewa komai.
Idanuwa na zubar da hawaye. Hanci na tsiyayar majina ta tashin hankali. Yayinda fitsari ya cika marar su. Kafafuwa sun gaza daukar nauyin su. Hannuwan su na lankwasar tashin hankali, Ya yinda sassan jikin su baki daya suka yi laushi..
"Allah ya jikan ka da rahama... Hamma Ashir."
Suka jiyo muryar Amnah daga gefe ta kwanta akan ledar da aka sanya shi namansa sun kone kurmus kamar babbakakken kan rago gaba daya shine sanye acikin ledar sai gutsattarin naman jikin sa kamar an soya su sun babbake sun kone. Yayinda sauran rassan jikin nasa kuwa ma babu sun nike a titi sun kone da mai. Wasu kuma bazasu ganu ba. Kasancewar direban motar. Da shi Ashir din da yaran motar tirelan man duk sun mutu...
🥴🤐Acigaba da bin littafin KWANKWASON JIMINA MAI WUYAR SHAFAWA...... A kuma yi hakuri, bana labarin haka yazo 🙏🤭
#RICH VS POOR
#ANEES
#MARWAAN
#NAWRAH.....
#LIFEPARTNERS
#AL HUB HAYAT
_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_
_KU MARMATSO KUSA...🔊_
_ZAFAFA BIYAR 2024_
_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_
_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_
_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_
_________
_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_
_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_
_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_
_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
[3/10, 21:02] Maman: _K'K'J_
_(M/W/S)_
_✍️:MX_
_49_
_Koda kuɗinka sai da rabonka. Ka gani su birgeka, ka saya ka birge mai kallonka. Albishirin ku ƴan kasuwa da masoya. Kuna ina? Ina kuka shiga? Maza ku garzayo kantin sauƙi da rahusar ingantattun kaya na kasarku dama ketarenta. Bari na kaiku, *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING* ke muku sallama irin ta addinin musulunci da babban albishirin shiryawa tsaff domin kawo muku kayayyakin buƙatunku na yau da kullum. Tun daga kan irinsu, atamfa, lasses, shaddoji, materials, abayas, takalma, handbags na zamani, vails ƴan yayi. Hijjabai. Sarkoki da dangoginsu. Kayan shafe-shafen dana kwalliye fuska. Agoguna harma dasu eyeglasses na manyan mata. Kai kai Karfa na cikaku da zance, dan zaku iya ganin komai a *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING* domin farin cikinku. Kayan yara harma dana maza ba mata kawai ba. Ba'a sayen ɗai-ɗai zamu tsaya ba harda sari ga mai buƙata zamu bada in sha ALLAHU kuma akan RAHUSA mai sauƙi da kaima zaka samu naka rabon. Zakuma mukai maka kaya a duk inda kake a *NIGERIA* in sha ALLAHU. Ƴan kasuwa masu sari da masu sayen ɗai-ɗai ku garzayo nan domin gani da ido in sha ALLAHU. Ka gani su birgeka, ka saya ka birge masu kallonka sai a *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING*👇_
https://chat.whatsapp.com/Cce1etNkvVKCBlgSqXa4Ek
:::::::::
Allahu Akbar! Lalle Allah buwayi ne gagara misali, Ya azurta wanda ya so a sanda ya so. Ya talauta wanda yaso a sanda ya so. Ya raya wanda yaso a sanda yayi iko. Haka zalika ya kashe wanda yaso a sanda ya so. Kuma dukkanin abubuwan nan kaunar da Allah ke wa bawan sa yafi karfin alkalami da bakin da zai furta .....
Hakika ahalin Hamidniyya sun shiga dimuwa wadda ta kere duk yadda alkalami zai fasalta. A gub'i a gub'i sun rasa rayuka hudu ... Daga kan kaka, Uwa, Uba zuwa 'Da wato marigayi Ashir ... Marigayiya yafendo, Marigayiya Hindu, Marigayi Junaidu, da kuma marigayi Ashir.
Kuma dukkanin su ba wasu lokaci mai tsawo aka dauka na tazara tsakanin rasuwar ta kowanne ba.... Lalle bawa ya kamata ya koma ya tuba ga ubangijin da ya halicce shi. Domin shi din buwayi ne gagara misali. Mamallakin kowa da komai ...
Dakyar likitoci da maaikatan asibitin bangaren sashen suka tausashe su duka tun daga kan Bappah Auwalu zuwa Amnah .suka saka su a mota suka mayar da su gidah dauke da ledar da ragowar naman gawar marigayi Ashir ke ciki...
Aka wanke shi aka nannade shi a likafani. Haka dan tsakuren sauran naman nasa sai ya zama kamar jariri ne ya rasu aka nade shi...
Akayi masa sallah aka kai shi gidan sa na gaskia wato makabarta gidan kowa... Ba tazarar kaburarruka tsakanin kabarin marigayi Ashir dana iyayen sa marigayi junaidu da marigayiya Hindu...
Ashir ya samu mutane, Mutane sosai da sai ka dauka wani babban maaikacin gwamnati ne ya rasu, ko wani babban dan siyasa ko kuwa mashahurin dan kasuwa ne..
Ba ahalin Hamidniyya Lebanon ko ince ahalin marigayi junaidu su Nawraah ne kadai suke alhini ba. Baki daya mutanen Naduka zone suke alhinin rasuwar Ashir.
Ya samu yabo sosai daga bakunan mazauna yankin Naduka zone, Dana unguwar da sike da ma yan layin su, da wajen aiyukan sa. Bangaren lodin tasha, Da na gangaren wajen wankin mota, Da inda yake leburanci idan ana gini... Magina sun shiga dimuwa wanda suka san shi. Da ma masu fenti Wanda suke harka daya...
Banda tarin mutane da suka zo daga yankin bunza da rasuwar tasa ta riski kunnuwan su. Sun shiga dimuwa sosai.
Haka zalika Ashir ya samu jamaa da suka dinga biyan duk wasu bashikan da ake binsa... Suka koma harhada yan kudade suka ce a bawa yan uwan mai rasuwar Allah ya gafarta masa ya kai masa ladan Amin.
Haka aka dinga zuwa ana taaziyya. Saboda kowa yayiwa marigayi Ashir shaida ta kirki, Babu ruwan sa da shiga harkar da ba tasa ba, Yana mutinta kowa ga ladabi da biyayya, Bai taba fada da kowa, Kuma kowa nasane, komai kankantar aiki inde halal ne zaiyi a biya shi. Don haka kowa yake shedar sa ana masa addu'oin halayen sa nagari su bishi Allah ya haskaka makwancinsa.
Haka aka share makoki... Duk wannan Kwanakin da akai ana makoki. Hankukan kannen marigayin sun tabu sosai tamkar zararru wadanda basa hauka. Don kuwa magana ma sai an tsawatar musu da fada da magig sannan sike yi
Sun koma haka haka gwara Ashfeef da Amnah ma. Amman Nawraah mutuwar ta daketa sosai. Don har karin ruwa ma sai da akayi mata na leda biyar .
Sun Sha zazzabin na rashin lafiya sun kwanta ciwo dukkan su. Abun ya tayarwa da mutane hankali musanman bappah Auwalu da ya Dan sayi alawa ya Kai islamiyar kusa da su yace arabawa Yara akuma yi addua dan Allah Allah ya sanyawa Yan uwan Ashir su Nawraah hakuri da dangana Ameen..
Sannan ya sake sawa aka musu saukar karatu na alqur'ani. Shi ma Kuma ko da yaushe a sallah da bayan yayi karatu, Yana yi musu adduoi Yana gayawa Allah kan ya farfado da zukatan Yan uwan marigayi Ashir
Sai da suka dau dogon zango sosai Kafin su farfado. Amman duk da haka ba wata magana suka cika yi ba daga uhm sai uhm uhm kawai. Kullum cikin Nawraah take. Bappah Auwalu yayi yayi amma Ina ta kasa hakuri kullum sai tayi Kuka sosai idan ta tuno da shi kadai ne dama ya rage musu tamkar shine mahaifi da uwa agare su. To gashi shima an wayi gari Allah daya fi su kaunar sa ya dauke abun sa.
Maganganun Ashir su nata dawo mata Kai. Daman wasiyya yake musu duk maganganun da yake fada a baya.tamkar yasan mutuwa zaiyi kullum cikin yi musu nasihar rayuwa yake Yana kara Dora su akan hanya madaidaiciya.
::
Toh haka rayuwar ta cigaba da tafiya ta kowanne bangare na cikin sashen littafin.
Ko'ina ana samun sauyi na rayuwa wani na dadi wani akasin haka.
A yanzu dai babu wadanda duniya ta sauyawa ta kuma juyawa baya fyace su nawrah da suka sake zama abun tausayi. Sun rame baki daya sun jeme.
Gashi makarantar tamkar da aka basu gurbi gini har an fara karatu basu taba zuwa ba saboda alunin rashin Dan uwan na su. Layla ma taki yadda taje ita kadai sai da Nawraah. Nusaiba ta daketa ta kyareta amma kmadagas layla tace ita gaskia sai da Nawraah zata fara zuwa jami'ar.
Hakan kuwa akayi sai bayan kwanaki hamsin da uku da rasuwar Ashir tukunna sannan Nawraah ta hakura zata fara zuwa jami'ar. Kasancewar bappah Auwalu ya zauna ya sake mata nasiha Mai ratsa jiki da jikinta yayi sanyi ya karkare yace,
"Dukkanin wadandan abubuwan agaba zasu wuce inshaa Allah. Haka rayuwar take wucewa yake kamar baayi ba nawrah. Kuma akace wai mutanen kirki Allah ya ke saukewa. Bayaga haka sanin kanki mahaifan ki da dan uwan ki mutanen kirki ne na kwarai. Duk inda mutanen kirki suke masu Kuma su junaidu sun zarce. Kuma wallahi Allah ba zai barku haka ba. Akwai jin dadi agaba da yardar Allah. Domin Allah shi kadai ya barwa kansa sani Nawraah. Tabbas munyi rashi. Amman Allah dayafi mu son su ya karbe su Nawraah. Sai mu fawwala lamuran mu gareshi. Da yardar Allah Nan gaba sai kinyi dariya . Zakiga komai ya wuce. Addu'ar mu kawai sike bukata musanman taku da kuke Yaya agsre su haka zalika Ashir yake Yaya agare ku..Allah ya gafarta musu kinji? Ki shirya goben Dan Allah kuje kinji? Ki dau hakan a ranki ki saka daga gobe kin shiga wata sabuwar rayuwa wadda acikinta ne komai zai yi sauki na matsatsi kinji? Allah ya muku albarka"
"Allahumma Aameen Bappah. Inshaa Allahu zanje"
"Yauwa haka nake son ji. Mashaa Allah. Bari naje nan layin baya na dawo"
"To bappah sai ka dawo"
Fita yayi daga dakin nasu. Ta juyar da Kai tana duban Amnah dake. Bacci ta sake ramewa itama baiwar Allah duk sai Kashi baki daya sun mokade.
Mikewa tayi ta nufi baya tayi futsari kasancewar akwai rariya da famfo awajen ta dauro alwala ta dakko sallaya ta shimfidah tana sallah. Kan Allah ya shiga lamuran sun ya musu zabi nagari adukkanin abubuwan da suka saka agaba na rayuwar su Allah Kuma ya jikan iyayen su da yayan su. Ya gafarta musu. Jamia Kuma da zasu fara Allah yasa suje a sa'a Amin"
Haka ta daga hannuwa sama bayan ta idar tanata kwarara adduan daga nan juna ta dakko alqur'ani ta zauna tana karantawa. Hawaye ya shiga diga daga idanun ta rayuwar su ta baya kawai take tunowa lokacin da dukkanin su suna raye yadda rayuwar tasu ke tafiya ahankali cike da farin ciki. Amman yanzu duk sun rasu, rayuwar tasu ta jima cikin dinbin bakin ciki da ya mamaye farin cikin su na baya ...
_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_
_KU MARMATSO KUSA...🔊_
_ZAFAFA BIYAR 2024_
_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_
_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_
_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_
_________
_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_
_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_
_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_
_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
[3/10, 21:02] Maman: *_KWANKWASON JIMINA!!_*
_(MAI WUYAR SHAFAWA)_
🦩🦯🦾
_✍️: MX_
*_ZAFAFA BIYAR 2024_*
_vip pages na arewa👇_
*_arewabooks:mssxoxo_*
_*BOOK ONE*_
_paid page :50_
_(FINALE/KARSHE)_
____
*Zafi* ake yi sosai astagfirullah. Gashi babu window a dakin nasu. Dan Amnah ma da wando take kwanciya kawai. Kusan kwana Nawraah take a zaune tana mata fiffita. Gashi ciwon ta kwana biyu ya motsa ya lafa ya dawo yakeyi.
Duk yan kudaden da aka raba musu na ragowar gadon su baki daya har na wajen marigayi Ashir duk akan rashin lafiyar Amnah yake tafiya. Saboda lalurorin ta masu cin kudi ne...
Bappah Auwalu yayi yar buga bugar da zai yi ba wani kudi da yake samu. Wanda ya dan samu din Nusaiba sai ta kwace tace yara ba lafiya su Ahmad zata saya musu magani....
Ko da yake maganar zaa fasa wundo a dakin dasu Nawraah suke. Haka nusaiba a ranar tun safe ta dinga tijara har dare tana dire tsallan albarkar wallahi babu mahalukin da ya Isa ya fasa mata wundo . Ai dakin mallakin ta ne halaliyar ta ne din haka Bata amince ba.
A ranar tsabar bakin ciki sai da Bappah Auwalu ya jera mata marika har biyu a kuncinanta ta dafe kuncinta tana duban sa,
"Ka mareni Auwalu?"
"Na mareki nusaiba. Kiyi abunda Zaki. Haba mace sai kace zazzauciya ? Aradun Allah wani mai tabin kwakwalar ma yafi ki sanin abunda ya Kamata. Ace ke kwata kwata ba digon tausayi a ranki? Ke fa uwa ce. Kin haifa gasunan agaban ki. Baki tsoron ayiwa naki haka?"
"Okay baki zaka mana kenan ni da yaran? To ni na haife su da Kai na kenan? Kai ma ai jinin ka ne. Ko ka ki, ko ka so su, su din da baka son su dai sune 'yayan ka na cikin ka wadancen yayan dan uwan ka ne"
"Duk daya suke awaje na, 'yaya na ne. Wai tsaya na tanbaye ki. Baki tunanin mutuwa ne? Bakya tunanin idan kika mutu kika bar naki yaran wa zai rike mike su? Ko gani kike ba mutuwa Zaki ba jiran duniyar zaa bar Miki eh? Idan baki sani ba duk abunda kayiwa Dan wani ko kaiwa wani na badai dai ba Allah sai anyi akan naka. Musanman maraya wallahi maraya yayi kuka akan zalun tar da kake masa na rantse da Allah Allah dai ba zai barka a haka ba. Na Miki karatun nan nayi nayi amman saboda kwakwalwar kifi ce dake Sam kinki dauka to bari kiji wallahi kin Kai ni karshe. Kinsan Allah sai anyi window a dakin nan sai dai ki hadiye zuciya ki mutum ai dan uwana ne yabaki wajen Kuma mahaifi ne agare su. "
"Sai Kuma kayi. Duk wadannan zubar maganar da kake kamar rubabbiyar bishiyar kanya ba damuna take ba kaji na gaya maka. Abunda na sani wallahi summa tallahi idan akayi window a dakin nan sai kasha mamakin abunda Zan aikata narantse da Allah sai kayi dana sanin sani na"
"Ko? Yo zan nuna Miki ni ne mijin ni ke auren ki ba kece ke aure na ba. A karkashina kike. Kina wani tunkaho kina chatting da matan manya kina hada kanki da su. To bari na tuna Miki Naduka mu zuwa mukai, Baki ne ba anan aka haife mu ba. Kuma mu ba kowan kowa bane bamuda ko sisi. A baya munyi dukiya a bunza a zuriyar mu ta hamidniyya lebanon Wanda ke bakya ciki ma. "
"Yanzu ka fito da abunda yake ranka Auwalu. Gorine Allah na tuba ba yau ka saba ba. Naji bani acikin zuriyar ku ta hamidniyya Lebanon Amman Nima nawa jinin ba matsiyata bane. Allah na tuba kuda kuka Tara dukiyar yanzu Ina fake eh? Mutum ya dinga sanin maganar da zai fada ba'
"Ke dalla can sakarya. Wadda ke bude baki waaaa tana zuba agaban yaran data haifa. Allah ya jikn Hindu a ranar da zata rasu ma sai data Miki nasiha ki kula da yaranta Amma baki daya kinyi fatali da zacen ta"
"Haba nagaji ya ishe ka haka. Hindu Hindu Hindu Hindu kullum dai ba gajiyawa"
"Hmm. Faccalanci dai ba hauka bane. Wannan rashin hankalin naki tun kina amarya na daukar faccala kamar kishiya ba Zaki sauke shi ba. Ace mace ta mutu ma Amman baki dai na kishin faccala da ita ba. Bayan ita bata zauna dake a faccala bama sai yar uwa.. Allah ya wadaran halayar kishin ki ta faccaloli datafi ta kishiya wannan hauka ne. Duk wannan tsanar da kike wa halainta daga nan ta farko. Saboda ta fiki da komai ko. Ta futo a tsatson manya tsatson mu daya sannan anmata kaya na yar manya lokacin bikin su. Sannan tanada kashin samu da yalwar arziki a komai ta kere ki shine dai kike wannan abubuwan to Allah ya kyauta. Ace ta rasu ma Amman kin cigaba da bakin kishin faccalar ki akan yaranta. Suma abin Yana bi su. Allah ya kyauta."
Nawraah da fadan su ya isheta ta jima daki ta dauki hijabi ta zura ta rike hannun Amnah zasu fita nusaiba tace,
"Kagani ko? Yanzu wannan ita zataje haka? Ni fa ban yadda da wannan yawon naki ba kina wani rike hannun Amnah."
Layla ta mike zatabi bayan Nawraah.