Author : Suwaiba Muhammad Category : Bookz
kai hannunta jikinshi in da yafi buk’atarta.
“Kullum, sai dai in ke kika ce a’a.” Ya fad’a yana kashe wutan d’akin.
“Make less noise don yanzu yaran biyu muke da su.” Ta furta a hankali cikin kunnenshi.
“An gama Matar Haydar.”
Washe gari da asuba Haydar ya bugawa Abul k’ofa suka tafi masallaci tare, suna dawowa Abul ya sake komawa bacci shine bai tashi ba har k’arfe goma na safe. Wanka yayi sannan ya fito ya samu babu kowa a falon sai mai aiki da take shara ta gaisheshi ya tambayeta ina mamanshi ta fad’a mishi tana d’akinta.
A cikin d’aki ya samu Laila na yiwa Mas’ud junior wanka wanda shima bai jima da tashi daga baccin ba, yana ganin Abul ya fara buga ruwan ciki bahon yana dariya irin ya ganeshi d’in nan.
“Morning to you too young man.” Abul ya fad’a yana isa cikin d’akin ya zauna a bakin gado yana murmushi.
“Ka tashi?” Laila ta tambayeshi tana jin zuciyarta kamar zata fashe tsabar murna da farin ciki.
“Na tashi. Ina kwana Mama?”
“Lafiya kalau. Ya gajiyan hanya.”
“Alhamdulillah.” Ya amsa yana kallon Junior da yake k’ok’arin barin cikin bahon wai zai zo gurinshi.
“Ka tsaya in d’auraye maka jikinka sai ya d’aukeka mana.” Ta fad’a tana rik’eshi yana neman yin kuka.
Cikin sauri ta gama mishi wankan ta mik’ashi ga Abul ko towel babu a jikinshi, sannan daga baya ta bawa Abul towel d’in ya lullu6eshi yana goge mishi kanshi suna yiwa juna dariya babu gaira babu dalili.
“Mama meyasa baku mishi kaciya ba har yanzu?”
“Babanshi yace sai ya cika shekara biyar ko shida.” Ta tashi tana shigar da bahon cikin band’aki sannan ta dawo tana goge gurin da mop.
Bayan ta mayar da mop d’in ta dawo ta samu Abul na shafa mishi man shafawa bayan ya bashi abun wasa yana kad’awa. Tsayawa ta yi a kansu tana jin hawaye na taruwa a idanunta domin har yanzu bata gama yarda wai Abul ne zaune kusa da ita yana ta6a d’anta da Haydar ba. A zatonta zai tsani d’an har yayi k’ok’arin yi mishi mugunta amma sai gashi cikin k’ank’anin lokaci har sun saba da juna, wato jini ba abun wasa bane.
Sai da ta gama shirya Mas’ud J sannan suka dawo falo Abul ya zuba abinci yana ci ita kuma tana bawa Mas’ud J nono. Har Abul ya gama cin abinci ya dawo falo shi bai daina shan nonon ba, zama yayi a kujera ya ce,
“Baya k’oshi ne?”
“Waye? Ohh Mas’ud? Haka yake, amma idan ya k’oshi shi da kanshi zai juyar da kai.” Ta fad’a tana murmusawa.
“Mama are you happy? A hakan?”
Laila ta jiyo tambayar a bazata wanda hakan yasa ta sunkuya ta dubi yaron dake kan cinyarta yana ci daga jikinta yana mata murmushi ta d’ago kai ta kalli Abul ta ce,
“Ina cikin farin ciki Abul saboda a yanzu ina jin kaina complete ba tare da na ji kamar na rasa wani 6angare na jikina ba. I am happy because I found love again bayan na cire rai da samun hakan. I’m happy saboda a yanzu babu mai kirana da sunan karuwa sai dai ace na auri yaro wanda baya damuna saboda nasan hakanne babu k’arya a ciki kuma ba sa6awa Allah nayi ba illa kwaikwayo da nayi da Manzon Allah SAW, amma ka ga kwanaki da ake mini k’azafin zina? Na shiga damuwa sannan na ji bak’in ciki mara misaltuwa. I’m happy Abul, and Ina son in mutu cikin wannan farin cikin.”
“Then nima I’m happy for you Mama. Wannan rayuwarki ce wanda ke kike da ikon tsarashi yanda kike so, I’m sorry I couse you pain da kuma bak’in ciki. Everyday fucking day ina regretting yanda na 6ata tawa rayuwar akan abu da kika tsarawa taki rayuwar, I don’t know what got in to me da har nayi tunanin hakan zai sa ki rabu da mijinki ki yi rayuwa kamar yanda nake so. Kaala Abdi said I’m selfish and I agreed, everything I did is about me not about you or Sabrin, nine ya kamata in kula daku amma sai ya kasance ku kuke kula dani I failed as a man. Babana ba zai ta6a yin farin ciki dani ba idan yau ya samu labarin halin da na jefa kaina a ciki don kin nemi farin ciki a karo na biyu. Kaala Abdi said all that and I believed him, I’m so sorry Mama don Allah ki yafe mini bak’in cikin dana sakaku a ciki. I promise to support you duk da cewa I hate your husband amma I will like to see you happy ko da kuwa dashi ne. I’m sorry Mama.”
Laila kuka ne ya kwace mata wanda hakan yasa Mas’ud J ya sake nonon yana dubanta shima fuskarsa a kwaye alamar zai yi kuka. Ganin haka yasa ta yi saurin share hawayen fuskarta tana juyar da kan yaron ga barin kallonta, sai dai shima Abul d’in hawaye yake yi kanshi a gefe kamar wanda baya son a ga me yake yi.
“After all that happened Abul, na koyi yafiya ga mutane ko da kuwa sun mini cuta mafi muni kuma na koyi zama da su da suka canja halayensu. Kullum idan na zo bacci sai na furta yafiya a gareka saboda bana fatan Allah ya kamaka da alhakina a ranar gobe balle har ace a dalilina ka shiga wuta. Komai ya wuce Abul, ka manta da komai kamar ba’a yi ba. Na yafe maka duniya da lahira, da abun da ka mini a baya da wanda zaka mini a gaba duk na yafe maka, sai ka nemi yafiyar Allah domin shi ka fi sa6awa da ka kauce hanya da hankalinka da kuma iliminka. Allah ya yafemu gaba d’aya.”
“Nagode Mama.” Ya fad’a yana share hawayen fuskarsa.
Itama hawayen nata ta share kana ta mik’e tsaye ta ce,
“Ka je kaci abinci sai ka tafi gidan Sabrin d’in domin tun da safe ta kira na fad’a mata kana bacci.”
“Ki bar abincin kawai domin nasan ta mini a can.” Ya fad’i hakan yana komawa d’akinsa ya d’auko abu ya dawo falon ya mik’a mata.
Laila k’ar6a ta yi tana dubawa cikin farin ciki domin laffaya ce a cikin ledarta mai kyau, ya ce,
“Tsarabarki ce, ga nan ta Sabrin.” Ya nuna mata na hannunshi wanda ke cikin leda.
“Ka kyauta sosai nagode, a ina ka samu kud’i haka?” Ta fad’a cikin d’oki tana warware laffayar ta fara d’aurawa bayan ta mik’a mishi Mas’ud J.
“Sauran kud’in da kike ajiye mini a gurin Kaala Abdi ne.”
“Masha Allah gashi kalar ta mini kyau, shukran habibi.”
Tana gama nad’awa ta shiga d’aki ta d’auko jakarta da kuma baby bag d’in Mas’ud J ta fito tana cewa,
“Mu tafi.”
“Ina zaki je?” Ya tambayeta.
“Shago zan je, ai tun lokacin da Sabrin ta fara zuwa school ni kuma ya zama kullum sai na je.”
“Ohh!”
Da haka suka fita zuwa tsakar gida Laila ta rufe gidan kana ta mik’a mishi key d’in motar tana cewa,
“Mu je ka ajiyemu a shago sai ka tafi gidan Sabrin d’in. Idan na tashi zan kira Haydar ya dawo dani gida.”
Bai yi musu ba ya kar6i key d’in ya shiga itama ta shiga gaba sannan ta kar6i Mas’ud J daga hannunsa ya kunna motar suka fita daga gidan suna hira gwanin ban sha’awa.
A bakin shagon yayi parking ta fita daga motar amma Mas’ud J na ganin shago za’a shigar dashi sannan ga wani a mota zai tafi yawo sai ya fara kuka yana mik’a hannun zai tafi gurin Abul.
“Mas’ud hoo, kai kenan kullum a dinga yawo da kai baka son zama guri d’aya? Ya Salam!” Ta fad’i hakan tana gyara gyalenta da yaron yake k’ok’arin yaye mata shi.
“Kawo shi mu tafi tare, I hope akwai kununshi a cikin jakar nan?” Ya nuna baby bag dake bayan seat.
“Are you sure? Ko da yake sometimes ana kaishi gidan Sabrin yayi awanni ma.”
Da haka Laila ta sakashi cikin car seat d’inshi ta saka mishi belt kana ta rufe marfin motar tana cewa,
“Ku gaisheta.” Murna fal fuskarta. Bata ma shiga cikin shagon ba ta kira Haydar ta sanar dashi abun da ya faru sannan ta kira Mas’ud shima ta sanar dashi wannan abun farin cikin wai Abul d’inta ne ya shiryu yake kuma huld’a da ita kamar da.
Abul yini yayi a gidan Sabrin tare da Mas’ud J wanda da yaji yunwa zasu bashi kunu ya sha ya k’oshi, da ya gaji da kunun ne ya fara neman nono hakan yasa Abul ya yiwa Sabrin sallama suka dawo gida da yamma bayan la’asar. A falo suka tarar da Laila da Haydar suna zaune amma Abul bai kula Haydar ba, yana mik’a mata Mas’ud J kuwa ya shige d’akinsa ya barsu a nan. Da daddare Mas’ud da matarsa Naana da ‘yar su Sultana mai wata d’aya a duniya suka zo yiwa Abul Sannu da dawowa, Abul ya gaishesu cikin mutunci ya k’ar6i snacks d’in da Naana ta mishi ya shige d’akinsa ya barsu a falo suna hira da Mamanshi da Haydar.
Bayan kwana biyu da haka, a weekend da safe Haydar ya tarar da Abul zaune a falo yana danna sabuwar wayar da Laila ta saya mishi. Zama yayi a gefenshi sannan yace,
“Ka fad’a mini cewa baza ka koma school ba, sai daga baya Mamanka ta fad’a mini cewa saboda ka rasa Laptop d’inka ne shiyasa ka ji karatun ya fita a ranka. Idan sacewa aka yi let’s try tracking it ko za’a samu, I know zaka iya hakan. In kuma 6aci yayi let’s get you a new one ko da kuwa sana’ar zaka yi.”
Shiru Abul yayi yana tunani domin shima yana son ya samu laptop d’in amma idan ya tuna cewa a gidan Sadistic Faruk ya bari sai ya ji gwuiwowinsa sun yi sanyi don ya tabbata Faruk zai lalata ko kuma ya k’ona. Amma an ce ‘A man can dream’, deep down yana ji a ransa Faruk bai lalata laptop d’in ba, sai dai ta yaya za’a iya zuwa a ce ya basu? Basu da wannan connection d’in yanzu, sannan ba zai yarda su sake had’uwa ba saboda har yau bai manta irin wasa da rayuwarsa da yayi ba.
“Yana Abuja gidan Senator Gambo Umar.”
Haydar da bai yi tsammanin zai samu amsar Abul ba ya gyara zamanshi ya ce,
“A gurin waye yake? Sannan meya faru har ka bari a can?”
“It’s a long story, but a gurin d’anshi Faruk yake. Sannan mun yi rabuwar babu dad’i saboda shi ya mini wannan lahanin a k’afata wanda har yanzu da d’ingishi kad’an nake tafiya.”
“Banney told me yanda aka kawo musu kai, but he never tell me abun da ya faru a gidan ba. Ya ce labarinka ne idan ka ga dama zaka iya fad’a mini.”
Duk abun da Haydar ya fad’a Abul sunan Banney kad’ai ya rik’e ya juyo cikin sauri ya ce,
“Kana tare da Banney har yanzu? Don Allah ina yake?” Yanda yayi maganar with desperation in his voice yasa Haydar ya ciro wayarsa daga aljihunsa ya bashi numbern Banney wanda a yanzu shima ya shiryu har ya koma makaranta bayan an sha daga, domin da kyar aka d’aukeshi a fannin Medicine bayan sun samu labarin ya ta6a shaye-shaye. Sai dai ilimin da yake da shi yasa suka d’aukeshi a kan duk ranar da aka kamashi da kayan maye ya daina medicine kenan har abada ko da kuwa zai canja k’asa ne.
Abul yana jin Banney ya d’auki wayar ya tashi a gurin ya wuce d’akinsa yana kiran sunan Banney kamar bai gaskata dashi yake waya ba.
“Stepdad d’inka ne ya baka number na ko? Yaushe ka dawo gida ko har yanzu kana Maiduguri ne?”
“Shine ya bani kuma na dawo gida. Meyasa baka nemeni ba all this while Banney? Where are you?”
“Bana son in yi waya da kai in ji kana cikin wannan halin da na bari ne Abul, ina garinmu har na koma school na fara daga farko. Guess duk shekarun da nayi ina karatun sun zube a yanzu. How are you? Don’t tell me you are fine, ka fad’a mini halin da kake ciki nake so.”
“Na dawo gida, na rok’i mamana gafara and my fucking stepdad ya bani adorable stepbrother. I will send you his pictures together with me. What about you.”
“First of all, I’m who I am today saboda wannan fucking stepdad d’in naka, shi ya tsaya mini har na samu makaranta ya kuma d’auki nauyin duk expenses d’ina ba tare da ya gaji ba. After every two months yana zuwa dubani a school in da nake zama saboda ban koma gidan mahaifana ba and he understands why bayan na sanar dashi duk labarina. Abul har yanzu iyayena basu canja ba, they are still dogs.”
Abul runtse idanunsa yayi domin labarin Banney ko shi baya son ji bare wani, sannan shi bai ga bak’in cikin da Banney ya gani ba a rayuwarsa dalilin k’azamar rayuwar da iyayensa suke ciki. Amma a hakan Banney ya gyara rayuwarsa sannan yaci gaba da karatunsa don ceto wanda yake da niyyar cetowa tun farko. Shi kuma me aka masa ma? Don uwarsa ta auri yaro shine har yake da guts d’in lalata rayuwarsa? Ya aka yi ma ya bari maganar mutane ta yi tasiri a zuciyarsa har ya za6i wannan jakar hanyar a matsayin mai 6ullewa.
“I’m sorry dude.”
“Ka tayani yi musu addu’a, ka kuma tayani yiwa Uncle Haydar godiya saboda shi ya taimaki rayuwata ya cironi daga gagari. Na kusa samun hutu na sati biyu, kuma I promised him a gidanku zan yi. Be nice to him or I will kill you with doctor’s scissors.”
Dariya suka yi dukkansu Abul ya ce,
“I missed you man.”
“You sound gay mallam. I mean it, be nice to that man. Yana son mamanka tsakani da Allah kuma yana kareta daga shiga depression ta hanyar halal saboda tsawon shekarun da ta d’auka bata da auren nan zai iya messing da brain d’inta.”
“Fuck off man, this is my mother we are talking about.”
“Call it Doctors intuition but your mother sound happy idan nayi waya da ita, idan zan samu ni tawa mahaifiyar ta zama haka I will literally worship that man. I respect your stepdad, so idan kayi disrespecting d’insa a gabana I swear zan manta duk abotanmu in ci.....”
“Kar ka zagi uwata.” Abul yayi saurin warning d’insa yana murmushi saboda yayi missing d’in Banney ba kad’an ba.
“I will never! Nima uwata ce kuma ta fi daraja akan wacce ta haifeni.”
Sanyi Abul ya ji a zuciyarsa domin zai iya cewa Banney shine abokinsa da yake jin sonshi har cikin zuciyarsa, jin yana cikin farin ciki a dalilin Haydar kuwa yasa yaji sassauci game da tsanar da yake yiwa mijin uwar tashi.
Sun dad’e suna waya wanda Abul har yana mamakin yanda Banney ya san komai na gidansu, domin har fad’a mishi yayi cewa shi zai tura mishi pictures d’in Mas’ud J tun yana jariri har zuwa yanzu. Wannan abu yasa Abul yaji kishi kad’an domin wani bare ya fi shi sanin k’aninshi.
Suna gama waya ya koma falo don yiwa Haydar godiya amma sai ya samu baya nan, komawa d’akinsa yayi ya bari a kan cewa zasu had’u a masallaci sallan magrib.
Haydar kuwa yana ganin Abul ya shiga d’akinsa ya tashi ya fita daga gidan yana danna wayarsa. Ana d’auka yayi sallama yace,
“Brother I need your help.”
Mum Fateey 👌
RUWAN ZUMA 🍯
Suwaiba Muhammad
(Mum Fateey) 09023713064
Wannan page naki ne ke kad’ai K’awata Phaty BB. Allah ya bar zumuncin da ke tsakaninmu. I love you fisabilillah.
(53)
Haydar gidan yayanshi Alhaji Abdul ya isa aka bud’e mishi gate ya shiga wanda zai iya cewa wannan ne zuwan shi na hud’u gidan tun bayan da suka shirya.
A lambun gidan ya samu yayan nashi da wani Ustaz yana koya mishi karatun addini, sai da ya bari suka gama sannan ya iso gurinsu ya gaisa da su kana Ustaz d’in ya tafi.
“Na ga kayi nisa a karatunka.” Fad’in Haydar yana kallon littafin dake hannun Alhaji Abdul yana murmushi.
Alhaji Abdul tattara littafan yayi guri d’aya shima yana murmusawa ya ce,
“Har yanzu kan nawa yana ja, idan na d’auki shafi d’aya kafin gobe zan haddace matuk’ar aiki bai mini yawa ba. Ina d’ana? Na dad’e ban ganshi ba.”
“Yana gida, baka da mata ne da na kawo maka shi ya yini.”
“About that...” Alhaji Abdul ya tafa hannayensa wanda yana yawan yin hakan ya cigaba da magana, “Dama nima ina nemanka zamu yi shawara. Amma kafin nan wani taimako kake nema?”
Ajiyar zuciya Haydar yayi kana ya fad’awa Alhaji Abdul niyyarsa ta d’aukowa Abul laptop d’in sa a gidan Senator Gambo Umar, ya karishe maganan da cewa,
“Allah yasa kana da wani connection da zai iya kaimu gidan har mu kar6o.”
“Ni ban sanshi personally ba amma ina ga kwanaki can da yake rik’e da kujerar Senator sun ta6a wani kasuwanci tare da Baba ya sayar masa da wata kwangila. In ka shirya mu tafi Abuja gobe, idan mun dawo kuma zaka je nema mini aure.”
“A ina ka samu matar?” Haydar ya fad’a cikin farin ciki domin har cikin