MAAIKACIYAR GOMNATI COMPLETE HAUSA NOVELS PDF BY ASMA BAFFA.txt

Author :  Asma Baffa Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   20 / 38

57K to 60K   out of 113.6K words

basket,sunzo shiga Palon waishi Omar dole sai ya cusawa Iklas takaici

Wuce mana shi yasa nake missing My Sahar wayayya da ita ba sai nace tayi abuba,Iklas takai bango suna shiga palon ta ajiye basket tace sai ka kira Sahar ta karasa ganin zata kunyatashi a mutane ya kama hannunta kwace hannunta tayi, dungure mata kai yayi masifaffiya jeki , zuciya ta kama Iklas ga mari ga tsinka jaka.

U better watch ur tongue cewar Omar,fushi tayi ta wuce bed room din yana bayanta frnds dinsa cewa suke shegen kaya kana harka,
Kwanciyarta tayi a bed din ta shareshi yana kallonta har ya gama yayi wanka cikin tsadajjiyar shadda ya fito sai da ya duba kalar lace din Iklas sai yasa light blue tunda lace dinta da blue jiki,
Yasha kyau sai kamshi ke tashi cike da kasaita suka fito yan daukan amarya har sunwa Omar nisa,Omar da rigima shi da zai dakko amarya sai ya tafi da mota biyu shi da Iklas a daya motar driver kuma ya dauki wata motar shi zai dauki amarya.
Motoci Jere aka fara iban kawaye da Dangi,wasu yan mata su Uku suka zo wajen motar da Iklas da Omar ke ciki,budewa sukayi dan Allah zamu shiga wannan kafin Omar yayi magana Iklas tace

Wannan motar iyayan amarya zamu dauka Ku fita harda murguda baki,wata a cikin yan matan tace kaji yarinya Da iyayin banxa bakifi sa'ar kanwata ba motar ki ce?
Oho dai ko ma me zaku ce baza a daukeku a motar nan ba,Omar kuwa yaki cewa komai,Raj ne yayiwa Omar horn pls ka kwaso su su kadai suka rage ni zan maidasu gida,Ku shiga badan halinku ba cewar Iklas, shiga sukayi daya daga cikinsu tace karfa ki kaimu bango duka zakici.

Omar ne yaja mota yana jinsu Iklas sai tsige musu takeyi akan sun shiga motar su kar wata tayi mata snatching. Omar zaiyi magana Iklas ta rufe masa baki da tafin hannunta wai kar aji muryarsa,kiss yawa hannun a Jere sun kai 8 ji kake dadas dadadas....yan mata Suma sai kallon kallo sukeyi,duniya tazo karshe yau ga budurwa da saurayi sun daina yin kiss a boyen ma sai a idon mutane,
Iklas sabo da yan matan nan su gane matsayinta ta kama yiwa Omar kiss a saman lips,yan Mata sai gulmarsu sukeyi,daya tace bayin Allah kar kusa Allah ya tarwatsamu sai fada suke kar fa ayi hatsari dasu a banza.
9pm aka raka ango,ko ina Iklas na gaban mota,har Omar ya tattara kayansa suka koma gida,

Ummi da Mama suka samu a Palo,omar part dinsa ya wuce Iklas ta zauna wajen su Ummi kunsha biki cewar Mama sannu,yawwa Mama Iklas ta amsa.
Mama ta kalli Iklas to dama so nake na fada miki daga yau baza ki kwana dakin Omar ba tunda ya warke,an gama komai na schl dinki Baffanku ya gama komai uniform ma duk komai an kawo,ranar Monday zaki koma schl ss3 za a saki dama.
Taji dadin schl sai godiya takewa Mama, amma taji haushin hanata kwana dakin Omar, gaskia da Matsala,jiki a sanyaye ta koma dakin Ummi,tana Shiga ta kama hawaye an rabata da mijinta.

Har Ummi ta shigo ta risketa tana kuka,lfy Iklas me ya sameki,kara volume tayi na kukan har kukan yara ta koma yi ayiye....yiye....me ya sameki ne wai yanzu muka rabu lfy fa,cikin kuka Iklas ta fara
Ni nayi kewarsa...I miss him so much........,dan salon a rabani da mijina za a ce na daina zuwa...shan majina tayi idan an San hakane baza a bawa bawon Allah ni ba dan me zaku daura mana aure,Ummi ce ta bige mata baki,da karfi tana kuka tace shike nan bazan fadi gaskia ba,bawan Allah sai ja masa rai kukeyi baza a fada masa shi mijina bane,yanzu kuma an kuma cewa na daina zuwa wajensa akan wani kudirinku,
Yanci ake nema miki c shashar banza, akan namiji Iklas kike sharban kuka haka Ummi ta fadi,make kafada Iklas tayi ni ba wani yanci,ya Omar fa me hankaline,kuma dan nayi kuka akan namiji haram ne?ai dai naga mijina nane, Ummi cike da takaici tace kije ki fadawa Uwarsa tunda ita tace ki daina zuwa kuma gata tayi miki sokuwa,wannan so ake nuna miki baki gane ba yar bantan Uba kin sani a gaba .

Ciwonsa idan ya dawo ALLAH karma a kirani ai da dare ciwon sa dawowa yakeyi zamuga me kula dashi,kawai kun tsufa sai dai kuce wancen kuce wannan,haka Iklas tai tayiwa Ummi masifa akan Omar, cikin tsakiyar dare ta farka magana ta fara Allah sarki yanzu wani yana can ciwo ya dawo.
Ummi Ce ta farka tana jin Iklas na surutu ta mata banza,kuka iklas ta sa ni wlh a barni naje na kula dashi.
Da kyar da nasiha Ummi ta shawo kan Iklas ta kyalesu sukayi bacci.

Omar kuwa juyi da tsaki kawai yakeyi Iklas taki tazo suyi hirarsu dan tana sashi nishadi,Mama ce ta shigo dakin,Babana tunda Allah yasa ka warke Na hana Iklas zuwa kwana room dinka shike nan sai ka daina jin haushi an hadaka da ba muharammarka ba,to Mama wa zai kula dani banfa warke ba,kaje ka dawo da matarka ta kula da kai,kamar yaron goye ya riko Mama pls ba abinda zan mata Allah zan kiyaye kiyi hakuri Mama, a'a bada ni ba cewar Mama,banfa gama warkewa ba kinga wuyana duk kashi,murmushi Mama tayi Naji in zaka kwanta ka kwanta kaje ka dawo da matarka ko ka auri wata,amma Iklas baza ta dawoba,rokon Mama ya dinga yi amma ta ficewarta ta barshi da kyar ya samu yayi bacci.

Ibzzy Boy ne ya koma wajen wankan tsinke ta rakashi har gidan su Omar sun Dade bakin gate security sun hanasu shiga ba dabarar da Basuyi ba amma security suka hanasu shiga gidan.
Haushi ne ya turnuke Ibzzy boy amma dole ya hakura sai wani time din,ko a hanya yaga Omar sai ya ci uwarsa sannan dole ya auri Iklas,

Sahar ma ta matsu Omar ya aiko da takardar sakinta amma shuru,ta matsu ta tafi Canada ta huta,tana ta jiransa har ta gaji ta yanke hukuncin da kanta zata je ya saketa ta dole,
Washe gari da safe Iklas da wuri ta shirya kwalliyarta cikin wata gaunt iya gwiwa da wando pencil tight legins gashinta ta saki,Ummi na kallonta ta tabe baki,sai shegen chusa kai ba kwarjini.Allah yasa dai mijina na yiwa kwalliyar cewar Iklas tana fesa turare, da Sauri tayi waje so take taga Omar jiya sun kwana basu ga juna ba,palon ta sakko da sauri da Omar taci karo shima ya fesa gayu ya taho ganin Iklas dakin Ummi sukaci karo a hanya,
Murmushi suka saki a tare Iklas kamar an mata bushara da aljanna tace morning Sir,how was ur night Gomnati cewar Omar yana kare mata kallo,Great tace,su Mama sun korar minke ko? Ae wai mu ba miji da mata bane shine sukace tunda ka warke shike nan,
Ke kuma sai kika yarda ai sai kice ban warke ba,kai ka fada musu mana,Mama ce ta fada fa dole ayi mata biyayya,Iklas ta birgeshi a maganganunta,
Ya Omar kalla botin din rigarka ya ciro matsawa tayi jikinsa tayi dage da kafafunta ta shiga gyarawa Omar rigarsa har Colar rigarsa,sai daga gashin kanta yakeyi yana wasa dashi,Mama ce tayi gyaran murya da gudu Iklas ta shige wani lungu tasha conner ta tsere,

Omar kadai Mama ta murdewa kunne sai kara yakeyi yana bata hakuri,na fada ma ka kawo min matar aure Mama ki sakar min kunne muyi magana pls,bazan saki ba, Mama to ki aura min Iklas mana to ni banda wata, dadi Mama taji ta sakar masa kunne,amma kasan Iklas yarinyace bata isa aure ba,Mama ba abinda zan mata sai dai na koya mata karatu duka Mama ta danawa Omar a baya,marasa kunya tashi kaje ga break can,ita ai da tasan bata da gaskia guduwa tayi.

Lekowa Iklas tayi suna hada ido da Omar suka fara magana da ido,Mama juyawa tayi da niyyar kallon me Omar yake wa signa da ido tana juyowa bul iklas ta bace ta kara shan conner kar Mama ta ganta kunya takeji,
Mama na barin palon Iklas ta sakko sai daria sukeyi kasa kasa kunnenka ya Omar yasha murda jifa yayi ja,ke ai wayo kikayi min,wlh ina ganinta na arce.ta window Iklas ta hango sahar taci ado tasha glass baki no respect.
Laaaaa Sir ga matarka nan ka ganta yanzu zata shigo jibarta ko kyau.

Aljana me suffar kunkuru gaskia an cuceka ya Omar an aura maka jagwal. Door bell sukaji,Iklas an tamke fuska ana jiran ko ta kwana karasawa wajen tayi ta bude kofar.






Asmabaffa
[9:10AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ

115-120


By
Asmabaffa




MAMAN SHUREIM jinjina gareki.



Kamshin Sahar ne ya bigi hancinta yayinda ta bude kofar,atishawa Iklas tayi ta karya tana toshe hanci,Omar ne ya matso tare da kamo kafadar Iklas yana mata sannu, Sahar kallonsu tayi ta ja wawan tsaki,ya Omar wari ba dadi naji,sannu to cewar Omar, mari Sahara ta kaiwa Iklas,kaucewa Iklas tayi marin bai sameta ba,dan uwar ubanki wa yake wari?dama Tara ki nakeyi ke har kin isa ni sa'ar ubanki ce,yar matsiyata,
Dagowa Iklas tayi an zaki iyayenta tace ubanki dai na gida me gemun dan akuya ba nawa ba,cakumo Iklas tayi suka fara kokawa Iklas ta dafalfale Sahar ta hanata yin komai,
Omar har wajensu ya tako ya janye Iklas da kyar tana haki tace shegiya me bakin dorunar ruwa, murmushin yake Sahar tayi duk nasan akan wannan kike haukar nan zaki saukene idan akan wannan holokon ne,ubanki ne Holoko ba ya Omar ba,haihuwar kwarin kunya,wacce aka haifeta a titi,
Omar ne ya rufewa Iklas baki ta kwace bakinta tana haki sakar min bakina ni,Sahar ce ta faki idonsu ta zabgawa Iklas mari kafin ta dauke hannunta Omar yayiwa Sahar mari biyu a jere,daria Iklas tayi woolu anji kunya mijinta ya tarewa budurwarsa ya mari matarsa a kan budurwa,kinga ko tanan na gama dake ke ko kula da miji baki iya bafa sai aiki,
Baki omar ya makewa Iklas rufe min baki,Iklas kina sani Surutu fa,Sorry Sir cewar Iklas wai agani ita me ladabi zama sukayi a kujera suka share Sahar tsaye,yau Sahar a ranta ta fasa zuwa Canada ta kudurce sai ta koma gidan Omar so take ya auri Iklas suyi kishi sai ta koyawa Iklas hankali daga ita har Omar,juyawa tayi da wannan kudirin ta bar gidan,

Omar kuwa Iklas ya kama yiwa fada ki daina tsokana Iklas zan daina tare miki,murmushi tayi Allah sai ka taremin yaushe zaka bari a daki Yar marainiyar Allah kana ji kana gani ai shi yasa nake yin tsokanar tunda nasan ina da kai.
To zaki gani ki kara tsokana zaneki zanyi da kaina,baki ta turo a tsokani mutum ace bazan rama ba,shagwaba ta dinga zubawa Omar sai ya Sosa mata kumatunta yana zafi da kaikayi na Marin da Sahar ta mata

Mama ce ta fito Omar meke faruwa ne naji hayaniya?daria Iklas tayi Mama kin zama yan sanda sai an gama fada,ko fashi duk wani tarzoma sai an gama kura ta lafa sai suzo da jiniya,daria sukayi gaba daya Mama tace ja'ira kin mai dani ma kamar kaka Ummi.

Da safe Iklas ta fito tsakar gida tana bawa yan aiki shara tana kara sasu sunata kalkale kalkale suna hira sai son Iklas sukeyi maza da mata bata da girman kai, ya Omar ta hango ya dau wanka sai kyalli yakeyi wani me aiki ta tambaya Inusa wai kuwa dan Allah kuma maza kuna ganin ya Omar me kyaune?mukut Inusa ya sharbe yawun bakinsa yace eh....eh....hajia ai Alhaji Omar yafi kowa kyau ke ni wlh ban taba ganin me Kyansa ba sai da na ganki.
Dadi Iklas taji ai kawana ne frnd dina ka gane ko cewar Iklas,daria Inusa yayi yace ai nan gaba hajia Oga Omar daga ganin Alama sonki zaiyi har aure,murmushin jin dadi Iklas tayi,ta kalli Omar da alama bai hangota ba,sanye da doguwar Riga wata siririya English wear da dan gyale ta fara tafiya tana kwalawa Omar kira ya Omar dan tsaya,har ya bude murfin mota yaji kiran Iklas, tsayawa yayi yana kare mata kallo rigar ta fito da shape dinta,tana karasowa Sir ina kwana,lfy me kikeyi a waje da safen nan?
Wani waje naga yayi dirty fa shine na sasu su gyara, good to kar ki sake na kara ganin ki tare da mazan nan,jibi shigarki fa,so kike su rainaki?girgiza kai tayi alamar a'a.to ki kiyaye mene kike kirana tun daga nesa?
Ya Omar kudi zaka bani nawa sun kare,me zakiyi dasu? Kyauta zanyi murmushi yayi to nawa kike so Hajia Gomnati cewar Omar, cike da shagwaba tace ko nawa ka bani ya isa,
Wajen da yake ajiye kudi a mota ya bude mata ebi yanda zai miki,ni bazan iya iba ba ka bani da hannunka,Iban kudi yayi da yawa ba tare da yasan nawa bane ya bata.
Ya Shiga mota kenan ya fara janta,Iklas ta kara tsaidashi da hannu,birki ya taka tare da sauke glass.

Sir na manta zanje siyo alawar madara makwafta,sai kin dawo kiyi dai shigar kamala saura naji kin fita da Riga iya gwiwa,insha'Allah hijab ma zan sa,Allah dawo da kai lfy,ameen take care.
Iklas harda daga masa hannu ita ga me miji.duk abinda Iklas sukayi a idon Haj Rahina dasu Sadiya,Iklas kuwa komawa tayi wajen aiki kowa sai da ta bashi 3k ta rike ragowar a hannunta ta fara tafiya domin komawa part dinsu taji an jawota baya,tana jiyowa taji Saukar mari tako ina,zafi ya hada ta ko ina,Haj Rahina ta makawa Iklas sanda a kafa, da karfi Iklas ta cakumi Sadiya ta cijeta a wuya saida ta daye mata fatar jiki.

Da gudu Iklas ta bar wajen tana shegu Allah ya isa tsinannu ta shige part dinsu tabar su sadiya na sake saken yanda zasu kamata watarana.Umma tace idan kun kamata Ku sumar da annamimiya babanku yana ghana ba yanzu zai dawo ba sai bikinku gwara aci ubanta da wuri,Aisha tace Umma ya Omar ko kulamu bayayi dan yaga Baffa yafi sonsa,
Kamar ba ubanmu daya ba,zanyi maganinsu gaba daya cewar Umma

Iklas na dingishi ga fuska tayi jajir sawun yatsu rada rada a kumatu Allah yasa su Suhaila ta samu a Palo,su Mama basa nan.
Bata so su ganta haka zasu shiga damuwa lallabawa tayi ta shige dakin Omar
Gyara dakin tayi fes duk ta canja bed sheet,su towel ta kai wa me wanki Wanda sukayi dirty,

Tunda ta fara ba ita ta gama gyaran ba sai 3pm,Sallah da wanka tayi a side din Omar,daga ita sai towel ta lallaba ta zube kayan data cire,ta dauko Wanda zata sa,tana dingishi ta koma dakin Omar ta bar Ummi na baccin rana,

Shiryawa tayi cikin Jan lace Riga da skert tayi kyau komawa tayi ta kai kayan data cire cikin dakinsu Ummi sai bacci takeyi,tashinta Iklas tayi Ummi zanje siyo alawar madara,kedai kawai son yawo irin naki,sai ki fadawa mijinki da babarsa kuma kar ki Dade,to Ummi,me ya sameki a fuska bata boye ba ta fadawa Ummi, Allah saka miki,ki kyalesu Allah na nan,karki fadawa Babar Umaru kinji,to kawai Iklas tace ta sa hajab dinta Iya gwiwa ta je wajen Mama ta mata Sallama,koda mama ta tambayeta gameda fuskarta gaskia ta fada mata bata boye mata komai ba,
Hakuri Mama ta bata sosai,Iklas ta siyo Alawar madara ta dawo sukayi 4eye da Ibzzy ya ciko mota dasu wankan tsinke,da gudu ta fada cikin gida tare da cewa securities kar Ku barsu su shigo,dakin Mama ta shiga Ummi da Mama ta gani ciki suna hira,

Gadon Mama ta hau ta fara shan alawar madararta,ta basu tasu dasu Suhaila,tana sha ta rike wata a hannunta bacci ya kwasheta,to 5 Omar ya dawo dakin Mama ya nufa suka gaisa, sai hira sukeyi da Ummi yana satar kallon Iklas kafarta daya ta kumbura a kwauri wurin yayi ja,

Fuskarta ya kalla nan ma shatin yatsu,gashi tayi ja,a jikin mudubi yake da,amma kamar an mintsineshi ya koma bakin gado ya zauna yana karewa Iklas kallo,Ummi tace kazo yin rashin kunyar taku tashi ka tafi,Mama tace abinci na kitchen jeka dan Allah zaka damemu.Mama kinga taji rauni fa,ga hijab jikinta tana bacci zai takurata,hannu yasa zai cire mata Mama ta bige hannun jeka zamu gyara mata,

Omar shi kam an takura musu Ummi zai samu ya fadawa ta bashi auren Iklas kawai.

20 / 38