MAAIKACIYAR GOMNATI COMPLETE HAUSA NOVELS PDF BY ASMA BAFFA.txt

Author :  Asma Baffa Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   27 / 38

78K to 81K   out of 113.6K words

ta miki yau zata bar gidan nan, wallahi baza ta tafi a banza ba sai na rama idan Allah yasa na warke,murmushi yayi ya gano me Iklas ke nufi,in dai kana sona kaji dadin zumata Dana baka dazu to ka kyalemin Sahar har na warke idan na rama kuma ka saketa wlh ko na tafiyata wajen Ummi....kuka ta barke dashi irin azabar da takeji,

Omar yace ur wish is my command Gomnatina abinda kika ce shi za ayi, ya sureta sai Toilet.




AsmaBaffa
[9:18AM, 4/21/2018] ‪+234 903 944 2971‬: ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GONNATI
ⓂⓂⓂ

155-160

By
AsmaBaffa




Tana kuka yana mata wanka,Haka ya gasata sosai sai sannu yake mata,fitowa yayi tayi wankan tsarki da kanta da sauransu,bedsheet kuwa blood din Iklas ya gama batashi,cirewa Omar yayi har katifar sai da ya dan shafota,liquid soap ya sawa katifar wurin daya baci yasa dan ruwa kadan da towel karami ya dirje wajen tas,
Hand dried ya dauko ya busar da wajen sannan ya shimfida wani bedsheet din,a washig machine ya wanke bedsheet din ya baza shi,room din ya gyara kamshi ke tashi kawai,Iklas na rike bango ta fito hawaye wani na bin wani,idonta jajir ya kumbura,

Da sauri Omar ya karasa gareta zai riketa tana kuka tace ni....bana sonka...ka daina....ku...lani.ba so...kake... Na mutu...ba...ka...kyaleni....na mutu...ma sai sabon kuka
Omar ya rasa yanda zai lallashi Iklas,kusa da ita ya zauna bakin gadon,zai fara magana tace ni...ka...kyaleni...dama abinda akeyi a auren kenan ni kam Ummi ta cuceni an bawa shugaban mugaye na Nigeria ni.
Daria Omar keyi a ransa,haba Gomnatina dadifa muka je nema,hannunsa daya ya daura a bisa cinyarta, daukewa tayi ta jefar da karfi,
Am so sorry ai kin huta yanzu an bude hanyar next time kece da garabasar,da sauri tace Allah kiyaye,so nake ma ki warke na kunna mana kida ki min rawar nan taki,harara ta balla masa tana ci gaba da kukanta,da kyar ya lallasheta yace, shafa mai mana kimin kwalliya,kuka ne ya taho mata tace ni yanzu ba duniya bace a gabana ba ka daina takura min,kuma ka kiramin Ummita da Suhailata Allah sarki yan uwana

Sultan Omar ya kira a waya, ya na dagawa yace kai munafuki wlh duk sai na muku rashin mutunci yanda ace kun San Iklas matata Ce amma kuka ki fada min,tun da wuri,dariya sultan yakeyi sosai kai kuma sai yanzu kaji haushin?

Malam magani zaka kawo ma Iklas bata jin dadi,nan ya labartawa Sultan yanda Sahar tayiwa Iklas,daga nan yace kuma damafa bata da lfy Sultan sai daria yakeyi

A lallai mutumina Ashe angwancewa kayi dole kaji haushinmu,gaskia Frnd baka da hakuri yarinya ce fa,to malam ina ruwanka in zaka kawo min kazo ko na kira wani,Allah huci zuciyarka gani nan zuwa
Iklas dai kukanta takeyi a hankali tana goge ido,Omar sai aikin lallabata yakeyi yana bata hakuri,
Kukanta ta karawa karfi ga abinda kukayi min kai da matarka yanzu kaje ka kara fadawa Frnd dinka sai sun San me ya faru,sorry baby magani zai kawo kin San kuma dole yasan matsalarki.

Kitchen ya Shiga ya hado mata tea da dambun naman da ta soya jiya,da kyar ta yarda ta ci,tana gamawa Sultan ya kawo magani a compound suka suka hadu ya karbo,wata Riga ya bata tasa marar nauyi,kana ya bata magani ta sha ya shafa mata a shatin bulalar da ta sha wurin Sahar,tare da kwantar da ita,
Kallon Omar tayi tare da turo baki tace kiramin Ummi a waya,to zan kirata amma sai kin daina kuka,hawayenta ta goge na daina to.

Ummi ya kira bugu daya ta dauka a ladafce suka gaisa da Omar,yace Iklas ke son magana dake mika mata wayar yayi,cike da rauni tace Ummi ina kwana gaisawa sukayi,Ummi tace ya najiki haka,lfy kuwa?kukan da ya taho mata ta hadiye tace lfy Ummi kaina ke dan ciwon gobe ko jibi zanzo
Wanne irin zaki zo daga aure wlh kar na soma ganin kafarki gidan mu,duk iskancin da kika dingayi a gidan nan a bar miki mijinki daga kai ki zaki zo yawo,
Kuje kuji dadinku Iklas ke da Omar dinki,a sanyaye tace dan Allah Ummi to ki turo min dasu suhaila kinji,babu daya da zan miki,ki fita idona wlh na fada miki,tunda muka dawo gidan su Omar kina kula su Suhaila ne?ke ga me miji ko?to baza su zo ba,

Um...datse wayar Ummi tayi a ranta tana yar cin uwa taji jiki wa ya fada mata.

Kuka zatayi Omar ya girgiza mata kai amma sai da ta saki kukanta,gajia Omar yayi ya tamke fuska Ko ki min shuru Iklas ko na kara yin second rou...kafin yarufe baki tayi shuru tana zare idanu.
Jinyarta Omar ya dingayi har tayi 3days ta warke sosai har shatin dukan Sahar ya fara bajewa,kula da ita Omar yakeyi kamar kwai babu inda yake fita tunda akayi bikin su sau daya yaje wajen su Mama sai waya.

Iklas kullum sai tayi waya da Ummi tana roko a kawo mata su suleim,amma Ummi taki yarda da kyar Mama tace Abdallah zai kawosu yau suyi mata yini,Tunda Iklas tasha wahala hannun Omar tsoron sa takeyi ko bed din sai yayi mata Jan ido take hawa,yanzu bata shishigin manne masa sai dai shi da ya zame mata manniru
Ko yaushe yana jikinta kitchen bedroom etc sha'awarta ce take damunsa kullum da ita yake kwana yana tashi kamar karota akeyi kullum,gashi ko romancing Iklas bata barinsa,
Da ya kai hannu zata fashe masa da kuka,da kyar ma zata yarda ta kwana dakin,idan kiranta yayi ko wani abun zai karba daga nesa take mika masa ta fece da gudu,ko ta dinga lallabowa kamar barauniya.
Shi yasa gaba daya Omar ya shiga damuwa,baya jin dadi kwata kwata sai dayayi Dana sanin ma bai kusanci Iklas ba,saboda sha'awarsa ta karu,gashi gudunsa takeyi,Sahar kuwa bakin cikinta yake kunsa yanda take bin maza ya ninka na da,so yake ya rabu da ita kar wani laifinta ya shafeshi amma yayiwa Iklas Alkawarin kyale mata ita.

Kafin ya cika mata aiki,yau Iklas murna takeyi su Abdallah zasu zo da sassafe ta tashi Omar na bacci ta zame ta hau gyaran gida,kafin kace me ta gama komai,dakin da Omar ke ciki ne kawai ya rage mata jira takeyi ya tashi,

Tana shiga kuwa taga ya tashi ya shiga toilet,kafin ya fito ta gyara room din sai kamshi,kayan da zai sa ta Ciro masa,yana fitowa yau sabo da murnar su Suhaila zasu zo gashi taga Omar yana fushi da ita yana shareta,shi yasa taje wajensa da niyyar tsane masa jiki,hanata yayi fuskarsa ba walwala,juya mata baya ma yayi, ya gaji da abinda Iklas ke masa da shi yace ta masa guduwa zatayi tana tsoronsa kamar a kanta aka fara,

Abinda yafi bashi haushi gudunsa da takeyi tana nuna tsoronsa take ji kamar wani zaki ko aljani,yanzu dan gulma saboda tasan baki zasu zo tazo wani goge masa jiki,
Hannu ta mika a sanyaye ka kawo nayi ma,cike da masifa Omar ya kalleta bana so da ke kike min? Shuru Iklas tayi tana mamakin Omar dinta fa biye mata yakeyi,sai abinda take so yake mata,yau kuwa harda yi mata tsawa daga kawai tana tsoron kar ya kara mata irin abun nan,

Wata zuciyar tace mata ke Iklas kinfa chanja masa irin tsiyar da kika dingayi kullum,baccin kirki bakya bari yayi saboda masifa,bawan Allah ai yayi hakuri,in wani ne fa ta karfi zai miki,amma ko magana bakyaso ya miki ba irin lallashinki da baiyi ba,idan ma baza ki yarda ki kara bashi kanki ba to ki bari mana ya samu nutsuwa, ki kula da mijinki,Omar bai son hayaniya,dama kuma yaya sarai kin San Omar bai daukan raini,ke kadai yakewa haka,yake miki daria saboda yana sonki,idan kikayi sake wata ta kwaceshi da wuri,kuma kinsan ba ke kadai gareshi ba gobe gobe kwananki zai kare ya koma dakin kishiyarki.

Omar har ya gama shiryawa Iklas na tsaye kamar gunki tana zancen zuci sai ji yayi tace KUTMAR AI WLH BA A ISA BA.shuru ta karayi yana daura agogo yaji da karfi tace KARYANE BAZAN BARI BA,kallonta yayi da sauri yaga dai waje daya take kallon har yanzu,kafin ya ce komai yaji ta kuma cewa MIJINA NA NE NI KADAI harda kwalla zatayi kuka,
Tsawar da Omar yayi mata ita ta dawo da ita daga tunaninta keee lfy kike kuwa?Omar ya tambaya, kyararrabewa tayi zatayi kuka,omar ya wuceta yana aikine bai isheki ba.
Na wuce Office ni idan su Abdallah sunzo su jirani kar su tafi,kallonsa Iklas tayi taga yanda omar ya zuka uban kyau kamar zatayi kuka dan Allah ya Omar ka canja kaya kaji?
Akan me?kallonka fa za a dinga yi..mene damuwarki to?

To baka ci komai bafa? in na dawo zanci,shagwaba zata fara masa yagafa lallai zata jawo masa jangwangwama, bude kofa yayi zai fita da sauri tasha gabansa, to ko kiss baza kayi min ba?cuno masa bakin tayi gaba,taso bashi daria amma ya fuske tare da tureta ya wuce,
Sai daria yake a ransa gwara ya daidaita mata sahu.

Kamar zatayi kuka Haka ta dinga zaga dakin,toilet ta gyara ta karasa komai,duk hankalinta Na kan Omar kar ayi mata snatching, fresh milk kawai tasha da farfesun da tayi,
Wanka tayi ta cakare cikin wata doguwar rigar material,cike da kasaita ta fito main palon gidan,bata ga kowa ba sai yan aikin gidan,tsakar gidan ta fita tana zagawa tare da yaba tsaruwarsa,
Sahar fitowa tayi zata wuce wurin aiki ido hudu sukayi da Iklas kallon kallo akayi ko wacce na Harar yar uwarta, sai da Iklas taje jikin kofa tace sai nayiwa ubanki kaciya da kwalaba,ta gudu cikin palon,sashenta ta koma 10mnt latr sai ga su Suhaila sun fado Palon Iklas da gudu.

Anty Iklas salamualkm munzo, nanfa suka dinga hira Abdallah yace anty nan da 3wks zan tafi Russia karatu,inye cewar Iklas ta shiga yi masa adduar samun nasara.
Suleim tace anty yau da girkinki zamuyi lunch,
Suhaila tace ya Abdallah ance fa mu koma da wuri,harara Iklas ta makawa Suhaila look at u kamar ba wajen antynki kikazo ba,ba inda zaku je sai Honey ya dawo,
Daria suka sheke da ita baran ma Abdallah yace kai anty ko kunya babu.murmushi Iklas tayi tace yara mu yayyen zamani ne.wata Leda suka mika mata gashi inji Mama. Lallai Ummi bata Baku komai Ku kawo min ba?suka ce ae ya Omar kawai tace mu gaisar banda ke,murmushi Iklas tayi Ku kyale tsohuwa zamu hadu ne.

Girki ta shirya lafiyayye kala uku sukaci suka sha,Suna ta hira nan sukayi Sallar azahar da la'asar sukace zasu tafi gida,Iklas ta datse kofar dole sai ya Omar ya dawo Baku isa ba,

Dolensu suka zauna,wanka Iklas ta sakeyi tayi wankan dakakkiyar shadda maroon tasha aiki da farin zare,kafa dauri tayi tayi matukar kyau,sarka da earing duk farare,kamshinta ya cika gidan,
Omar ne ya shigo da sallama da gudu su Suleim suka rungumeshi,sai bin Iklas da kallo yakeyi tayi tayi kyau ga iya kwalliya,Suhaila tace Anty ga Horney din naki fa,daria sukayi Iklas harda sunkuyar da kai wai kunya,

Takaddun dake hannun Omar da ya shigo dasu ta karba hade da magazine, ledar hannunsa ma karba tayi ya mata magana a hankali daya tsarabar su Suhaila ce daya taki ce,ya wuce room,dubawa tayi taga wani tsandareriyar sabuwar laptop ta Apple,dayar ledar kuma kayan zaki ne da gani sune nasu Suhaila.Abdallah ta mikawa gashi tsarabarku su Suleim sai murna sukeyi,daya bedroom din ta shiga ta Adana komai ta bishi daya bedroom din hannunta dauke da takaddunsa,karar ruwa taji alamar yana wanka,a drower ta ajiye takaddun,ta karasa jikin kofar toilet din tare da Dora kanta jikin kofar tace honey na shigo na tayaka,daga ciki yake Allah kiyaye min,pls ya Omar bazan wa abarka daria ba,sai dai in zaki bari muji dadi shuru tayi ta dawo wajen su suleim tayi kus, ba a Dade ba ya fito sanye da jallabiya, mikewa sukayi yaya zamu tafi mu,to Ku Mun gode Ku gaida kowa da kowa,sai munzo har mota suka rakasu,

Kara shirin fita omar yayi Iklas na gefen gado tana kallonsa yafi dazu kyau,wani takaici ne ya tasowa Iklas tasan ma fita zaiyi,maybe zance zaije,kukanta yaji yana tashi kadan kadan,banza yayi da ita yasan me takewa kuka,kofa ya nufa kafin ya karasa ta rigashi ta sa key wlh baza ka fita ba,
Haka kawai me na maka da zaka dinga azabtar dani,ko abinci kinci kakeyi bayan ka bani wahala rannan matarka ta dakeni wanne mataki ka dauka?shine yanzu zaka dinga min haka.

A nutse yace me kike so na miki Iklas,tunda akayi abin nan wanne hakuri ne bana baki,ba lallashin da ban miki ba,koda baki bari na sakeyi ba amma ai bai dace ki dinga guduwa ba kamar wani dodo,dan kinga ina sonki ina damuwa,nasan kinyi min kokari amma ke a tunaninki abinda kikeyi ya dace?girgiza kai tayi tace gaskia nasan dai to banyi dai dai ba, Good amma ai sai ki koma normal ko kamar da,mene baki da labari a harkar nan?to ai ni ban San da zafi ba kuma ai Kaine ka yaudareni kace da dadi,
To ba hakki na bane?nakane mana kuma sai akace kamin mugunta?first ne wajenki dole kiji amma kullum rigimar ki daban a zauna lfy kinki daga kuka sai masifa dare da rana abinda zakice daban.

A hankali tana cuno baki to ba sai kayi hakuri ba kayi min uzuri amma da wuri har ka dau mataki.wanne mataki?gashi zaka fita da dare,dazu da kiga na fita a office aka kirani,yanzu kuma Sultan ke nema na zamuje gaishe da iyayen budurwar Raj.

Da Daren nan shi Raj din bai San kuna da mata ba to baza kaje ba gaskia ya canja time ko suje su kadai,me zaki bani idan na zauna? kajika sai zan baka abu ma zaka zauna kawai nace mijina bazai je ba she, gwara ka kirasu a waya ka sanar musu malam matarka ta hanaka fita,daria Omar yayi lallai sannu Mama, nifa ba wasa nakeyi ba cewar Iklas.

Haka suka dingayi da Iklas ta hana Omar fita,saboda ya Sata farin ciki ya kira Sultan kai nifa wifey ta hana zuwa kuje kawai next time aje dani,Raj ne ya kundumo Ashar dan Kut...uba mayen mace,sumi sumi kamar Salihi yana maganganun banza sai muzuren banza a waje yarinya karama tana zare masa ido,zamu hadu dakai ne,Sultan nayi Raj nayi,gajia Omar yayi ya yanke wayar,Iklas kanta taji ya kara girma,gaskia ta kai mace,ta hana kuma an hanu sai abinda tace da mijinta,bata San wayo Omar ya mata ba,ba wai zata iya hanashi bane kawai dan ra'ayinsa ne.

Abinci ta kawo suka ci suka sha,shirin bacci sukayi ta dauko abinda Mama ta aiko dashi ta sha Omar ya jata jikinsa tayi lamo a kirjinsa, yana shafa bayanta yace babyna kin San me? A'a cewar Iklas wacce ke jinta kamar Sarauniya abinda tace shi mijinta keyi

Ci gaba yayi wifey na Allah ya jarabceni da sonki,har watarana sai inji idan ba Umarni kika bani nabi ba ban jin dadi,ni nafiso a kirani da kan tace in dai a kanki ne,dadi Ya gama kashe Iklas har doro takeyi, ni yanzu a duniya babu abinda zakice nayi banyi ba,
Shidewa ya farayi wai zaiyi kuka, amma ke abin mamaki akan a bu kalilan jinina saida ya hau,bayan kin San ance a iya first night kadai akejin zafi, ba komai bazan bari na halaka ba, yana maganar ya gama cire mata kaya tik,tana so ta hana tana jin nauyin hakan yanda shi ke bin umarninta ace ita ta kasa yi masa biyayya tir da halinta.

Bazan miki dole ba tunda gobe kwananki zai kare Sahar ta sama min Nutsuwa, tunda wacce nakeso ta kasa, da Sauri Iklas ta toshe masa baki ta hanyar zura bakinta cikin nasa, tace haba dan Allah honey nafa warke dama tuni, kawai dama nunawa nakeyi ban warke ba saboda irin zafin Dana ji rannan.

Karki takura kanki baby Sahar na nan gobe, kuka ta fara masa tana ta tirje bedsheet din, ni dai dan Allah ka daina zancen waccen kazo gashi sai yanda kayi dashi,mene bazan ma a duniya ba, kasan kuwa yanda nake ji da kai?




Asmabaffa

Ayi hakuri readers nasan kun jira busy nake yaune that's y na barku da yunwa ba dinner da wuri lol.
[9:18AM, 4/21/2018] ‪+234 903 944 2971‬: ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ

27 / 38