Author : Billy Pinky Category : Arewa Pen
shi kayiba ba zaka ce yayi magana ba.
Gaba ki dayan su nutsuwa suyi,
Barka da dare yah Aj su hada baki gurin fada.
Da kallo ya bisu daya bayan daya,
"Ke"
Ya furta tamkar mai ciwon hakori,
Zaituna da tasan da ita yake tace Na'am yah Aj tana nufo inda yake tana wani rangwa d'a.
Tom bema san metake ba dan hankalin shi bashi gareta,
"Karna dawo na ganki a haka.
Yafada yana haurawa upstairs,
Me feenah zatai itada aynah inba dariya ba har da shewa.
Zaituna da ranta yayi ko loluwar baci itama b'angaren granny ta nufa dan ta gane nufin shi ta cire kayan jikinta kenan.
"Shiko kaitsaye dakin Ammii ya nufa.
Haka yayi ta zuba mata shagobba san ransa saiki rantse shine auta kamar ba Wanda gaba daya yaran gidan ke tsoro har ma manyan shakkar sa suke.
"Zakai dinner ne yau ko aa?
Tafada tana kallon shi.
"A'ah auta ta amso min Madara a gurin granny ita zansha"
Tom dayake itama tasan halin nashi baya son cin abinci bare kuma na dare ya gwamace yasha Madara ko coffee.
"Saida safe yayi mata yabi ta wata kofa da Kai tsaye part din shi zata kai shi............✍️
🌹 RAYUWATA 🌹*
*Story and written✍️*
*Bilkeesu .S. Aliyu*
_💞(Billy pinky)💞_
*🤝 Amanar nazari writer's association📚🖊️*
*[07070260240]*
_WhatsApp number or call_
_📚N.W.🖊️_
*Book 1 📖*
*Page 20&21*
"Yanzu zakaje ka gaishesu ne koh sai ka dawo?
"Saina dawo yanzu time ya kure"
"Allah yah tsaremin Kai ya dawo da kai lafiya Allah yabada sa'a"
"Ameen yah Allah cewar Addah, shima Ameen yace yana sunbatar goshin ta kana ya fice cikin nutsuwa, dolene inka kaleshi ka 'kara kallo .
Tunda ya fito compound din gidan tight security d'in dake zagaye da harabar wurin suka wani irin kamewa tare da sara mishi,
Had'i da gaishe shi"
"Hannu kawai yadaga musu tare dace wa kun tashi lpy?
Cikin harshen turanci.
Bai jira amasa warsu ba ya nufi"
"Gurin shegun manyan car's d'in dake jibge wuri guda su nufa shida security d'insa.
Zu'ke'kiyar ba'kar motar da juseph ya fiddo,
Wanda ko makaho ya shafa yasan eh lallai kudi yayi aiki wurin siyenta. Dan sai wani irin kyalli da sheke take mai daukar ido.
Gatan dai bata cika hayaniya ba kuma Bata mamaye waje ba. Tsaf take kala da yanayin matasan zamani irinsa dake gara kan nera bisa ga damar da ubangiji ya basu."
"juseph ne ya bude masa motar ya shiga sanan Yuoseef ya shiga suma sauran security d'in shiga nasu suyi su fita a jere susa motar da Aj yake a tsakiya juseph ke driving"
"Kai tsaye company su nufa"
"Ganin katon company dasu zo yasani furta masha Allah gaskiya company ya hadu ga girma, a saman company dauke yake da wani tambari Mai kamar tauraro irin tambarin dake jikin motocin shi"
"Har ciki su shiga guys d'insa su bude Mai motar,
Saida yadau tsawon lokaci kafin ya fito gaba daya ma aikantan sai girma mashi suke."
"office din danake kyautata zaton nashine, dan yafi ko ina tsaruwa, kuma security's ne aciki da wajen shi. ya shiga youseef beye dashi"
✨🤍✨
Uhm dan Allah meye ai bin wanan shigar granny? bama wannan ba ace yah majeed ya dawo amah baki gayama mummy ba?
"To ban fada ba kinga daga ke har uwar taki inbaku rabu dani da zancen Abdulmajeedu ba wallahi zan saba muku.
Kedashi kwata-kwata baku dace da juna"
"Kamar zaituna zatai kuka tace granny kina nufin nida yah Aj bamu daceba?"
"To banda abinki inake ina Abdulmajeedu?
jikifa yara ba tarbiyya, jifa shigar dake jikin ki da sunan wayewa, shiyasa yaran 'kauye sufiku hankali wallahi.
Takare maganar tana cigaba da damun furar ta,"
"Zaituna nashirin sake magana, granny ta zuba mata wani kallo, wuce ki bani guri kin wani tsayamin aka"
"Harara itama tazuba ma granny tana wuce bedroom din ta,"
"Kwafa granny tayi tacigaba da abin da take tana mita"
"Tana shiga ta danna ma mummy kira wayar na fara ringing ta fashe da kuka.
Aikuwa mummy na dauka taci karo da kukan zaituna, nanfa hankalin ta ya tashi an ta'bamata shalele.
Kinga ya isa haka fadamin meya faru?
Nanfa ta shirya karya da gaskiya tafada mata, kuma granny ma wai nida yah Aj bamu daceba takai karshen maganar tana sake fashewa da kuka"
"Kinga ki kwantar da hankalin ki, wallahi indai ina numfashi a doron kasar nan bamai auren majeed sai ke,
Inko kiga baki aure Shiba to saidai bana numfashi wallahi.
Bari Yaya ya dawo"
"Yauwa mummy na shiyasa nake kara sonki wallahi sosai Allah ya barmin ke"
____🤍💗
"B'angaren Ammii kuwa bayan Aj ya fita ne take karaba addah hakuri.
A'ah aminiya bakomai Nima jiya basma take sanar min ya dawo, kuma yau ina Shirin zuwa saiga fennah tashigo raibace, nake tambayar basma wai fada suke da zaituna.
Yaushe zaituna nan tazo gidan nema?
"Saida Ammii taja numfashi kana ta bude baki tamkar Bata son maganar tace.
Okay nima fitowa ta kenan natar suna yi maybe yau tazo,
Fitowar majeed nema sudena.
Takai karshen maganar kamar bata so"
"Ai kinsan yaranan sai addu'a wallahi Allah dai yashirya Mana"
"Ameen yah Allah"
"Daganan su cigaba da firar su irin ta aminai"
_____________
*Kaduna✨*
Tsaf su shirya cikin bakar abaya wacce ama kolliya da farin duwatsu sai takalmi Mai dan tudu. Safiyyah datai rolling din gale saita fito kamar balarabiya"
"Sallama suyima ummi anty hajara na musu tsiya aikuma yawo salamu alaikum jiya an fita yauma haka. Dariya suyi su fice suna mata gwalo.
Eyye zaku dawo kusa menine har ke ishan. tafada tana daga murya dan su jiyo ta da kyau"
"A motar Isha mutafi. Kai tsaye gidan anty zainab muje antyn Isha. aikuwa taji dadi sosai anan muka dade dan sai gabda magrib mukoma gida. Isha tayi-tayi Dani naje na gaida momy nace mata insha Allah gobe kan natafi zan zo. Badin taso ba ta ajemu bakin get ita kuma ta karasa gida kasancewar anguwar su daya"
"Koda mushiga ba kowa a parlour cikin sanda mu wuce sama Dan kar ummi taji mu tace yanzu mu dawo. Gab da zamu shiga daki saiga anty hajara nan. murmushi tayi tana fadin ummi!
aida gudu mushige muna dariya.
Itama murmushi tayi ta koma daki"
"Saida muyi sallar isha'i sanan mu fito parlour lokacin ma dady ya dawo amah Banda yah saif. Muna cikin dinner ya dawo, shima nandin ya nufo. nice farkon tashi aikuwa ina zama yah Ansar ya kirani, munsha waya har nake sanar mai gobe zan koma gida, da kuma sa ranar anty hajara. yace ai ummi ta fada mishi,
Har su gaisa da buhaisa da ganan muyi sallama.
Yau bamu wani dade muna fira ba kowa ya tafi daki, koda mu shiga ma bamiyi wata fira ba nida buhaisa kasancewar mungaji ko bacci yake ji,
*Washegari....*
A hankali take bude idanun ta tasauke shi akan agogon dake ma'kale a bangon dakin bakin ta dauke da addu'a tashi daga bacci
A round 8:30 ai da sauri ta duro a gadon Kai tsaye bathroom ta shiga bata wani dade ba ta fito da alamun wanka tayi duban ta takai kan bed din amah ba buhaisa alamun ya riga ta tashi.
Wanka tayi lotion kawai ta shafa ta saka doguwar riga mai dan santsi da hula kana ta fito parlour.
"Bayan sun gama breakfast, su tafi gidan su Isha, ai kuwa taji dadi sosai taja su suje su gaida momyn ta daganan su shige ciki fira su sha kamar baza su hadu gobe ba.
Buhaisa ce dai yau haushi takeji safiyyah. zata tafi gida, saida suyi sallar ashar sanan su koma gida.
"Kasancewar yah saif ne zaikaita"
Tsaf tashirya cikin atamfa riga da siket Wanda d'inkin ya zauna daram ajikin ta kamar dan ita ayi, kasancewar tafi buhaisa kiba, shiyasa kayan su kamata sosai, gogaggen Hijabin ta tasaka hadi eyeglasses, facemask dinta kuma ta mayar jaka ta fito.
Aikuwa buhaisa ta cika tai fam kamar zata fashe da kuka anty hajara ta tasata a gaba tana tono ta.
Saidai da tasata kuka, daga baya su koma lallashin yar auta.
Koda safiyyah ta fito itama lalashin tayi, ki kwantar da hankalin ki, bikin anty hajara fa yazo Kinga tun ana saura sati biyu zanzo to kinga ai na kusa dawowa.
Badi taso ba yah saif yace kinga tashi mu tafi kar yamma ta cikayi.
Sallama suyi da ummi da anty hajara kana su tafi.
Har kofar gida ya kaita shirin fitowa take taji ya rikemata hannun ta waigowa tayi tana Mai zuba mai hararar da ita kanta bata san ta Mai ba,
"Hannun ya saki yana dan wayan cewa, tafiya zaki ba sallama?
Ko kinyi kewarsu ne?
Ya jera mata tambayar ajere.
"Kai kawai ta daga mishi tare da cewa kadan.
"Kiyi kewar tasu?
"Uhm
"Tom shikenan sai yaushe kuma?
"Yatsun hannun ta tadaga mai guda biyu tare da cewa week.
"Two weeks?
ya fada yana kallon safiyyah.
"Uhm
"Yar kurma kenan wato na isheki koh Tom shikenan sai munyi waya.
"Baki tadan turo jin ya kirata da yar kurma,
Amah batace komai ba saida ta fita hannun ta rike da murfin motar kana tace.
"Thank you yah saif Saida safe, ka gaidamin da sisy nah please.
Ta hada hannu wan ta alamun roko.
"Baki ya saki yana kallon ta, saida ta rufe murfin motar, kana ya dago da sauri har takai bakin get.
Saida yaga shigarta ya sauke ajiyar zuciya kana ya tada motar ya tafi.
"Saida motar shi ta tafi ta dago daga leken da take tana sauke ajiyar zuciya, ga baki daya tsoran shiga take amah haka ta dake tai sallama a kofar parlour.
"Gabaki dayan su suna zaune a parlour daga mom har anty Waleeda da yah safwan dashi ba zaman gidan yake ba sai baby.
"Aikuwa da gudu baby tazo ta rungume ni nima rungume ta nayi muna kara sawa cikin parlour.
Tunda nayi sallama su zuboma kofar ido harna karasa ina gaida mom,
"Abin mamaki saida na ta'bata ta d'ago firgigit.
Kuma ta amsamin harda tambaya ta yasu ummi,
Amsa wa nayi ina gaida yah safwan shima dai amasa wa yayi tare da cewa ina kishiga ne safiyyah?
"Naje gidan ummi ne .
"Oooh shiyasa abincin ma sai anga dama akeyi a gidan kenan?
Bance komai ba na tashi na nufi anty Waleeda na rungume ta, duk da tana tureni amah ban damu ba dan ba karya nayi kewar su.
Yadda nai tsam mani hakan ce ta kasance Dan parlour dai sai addu'a wallahi.
Ina mamakin san jiki irin na mom da anty Waleeda.
"Bedroom nashiga na barsu da mamakin dawo wata, dan itafa mom batai tsammani zan dawo ba.
To shima dai bedroom din sai addu'a dan yama fi parlour datti,
Jaka tana ajiye ina Mai leka bathroom wayo Allah, na furta ina mai fitowa da sauri.
Parlour na fito na wuce kitchen na dauko kayan shara, bedroom din na share tare da yin mopping.
Na koma bathroom shima share shi nayi abin takaici ga pad nan haka duk na hada na share kana na wanke bathroom din.
"Saida akira magrib na gama aikin, yah safwan nata min sannu da yake shi ba halin mom ya biyo ba.
"Around 4:00
Natashi, raka'a atul fijir nayi kana nai sallah asuba tare da azkhar, nafara karatun alQur'ani ban wani dau lokaci ina yiba natashi nafara gyaran gidan kafin karfe 7:00am nagama komai har girki,
Wanka nayi har na fito anty Waleedah bata tashiba bare tayi sallah tashinta na kumayi, me hali baya fasa halinsa dan yauma masifa ta hauni da ita kyaleta nayi na cigaba da kintsawa.
"Tsaf na shirya cikin less pink wanda amai ado da fararen duwatsu, dinkin riga da siket,
simple makeup nayi dan kuwa daga fouda, sai kwalli, da lips gloos, and maskara, da na taje eyelashes dina dashi aifa ya fito gadar-gadar Masha Allah, kalba na hade na daure da ribom,
Parlour na fita dan na karya bakowa a parlour sai yah safwan, gaisawa muyi tare mu karya dan shima zai fita gurin aiki,
Jeki dako mayafi na ajeki,
Tom yah safwan.
Gogagen milk hijjab nasaka da face mask da eyeglasses sai plate shoe shima pink waya ta