Chapter 10 Reading Nafisat Return Book Complete By Ummu Dahirah.txt Arewa Novels

Nafisat Return Book Complete By Ummu Dahirah.txt

Author :  Ummu Dahira Category :  New Hausa Novels 2026

Chapter   10 / 20

27K to 30K   out of 58K words

bayan ya gama ɗakin sa ya koma, kwanciya yayi kan Three sitter ya lumshe idanun sa, shi ba barci yake yi ba kawai kwanciyar yayi, sai da aka kira sallan la'asar kafin ya tashi yayi alwala ya fita


A waje suka haɗu da Baffa suka jera har masallacin dake nesa kaɗan da gidan su


Bayan sun dawo a haraban gidan suka haɗu da Abba da Abbu da dawowar su kenan daga aiki


Gaishe su yayi cikin girmamawa, su kuma sai tambayan shi hanya suke yi cike da fara'a, haka ya'amsa musu sannan ya wuce ya nufi babban Parlour


Fadil na zaune a kan kujera yana kallo shi kaɗai ya shigo


Da sauri Fadil ɗin ya gaishe shi


Da kai ya'amsa masa ya nufi hanyan da zai sada shi da ɗakin Kaka


Da idanu Fadil ya bi shi dashi, sai da ya shige sannan ya taɓe baki a ransa yana mitan "miskilin banza! kai da Fadila wlh ban san wanda yafi mugun hali ba".


Sai kuma ya kwaɓe fuska yaci gaba da kallon sa.






Tura ƙofan yayi ya shiga yana motsa bakin sa


Kaka dake zaune kan Wheel chair ɗin sa kamar ko yaushe yana karatun Jarida ya ɗago yana kallon sa, sai kuma ya yalwata fuskar sa da fara'a yace, "Maraba da Jikalle na".


Takowa yayi ya zauna saman kujeran ɗakin yana kallon Kaka, kaɗan ya saki fuskar sa yace,
"Old man are you still alive?"


Sai Kaka ya saki dariya me sauti yace, "ja'iri ka ƙosa na mutu ko? To ina nan babu inda zan je sai na ga auren ka".


Kyakykyawar murmushin sa yayi yana shafa gashin kansa yace, "uhmm Kaka kace da sauran ka kenan tunda Ni dai ba yanzu ba".


"Koma dai me zaka ce sai naga auren ka tukun zan bar duniyar nan, dama tunda nayi muku maganar kai da takwara babu wanda ya haɓɓa sa, kun fi so dai a haɗa da ƙannin ku ko?".


Usman taɓe baki yayi sai dai be ce komi ba


Kakan changed the conversation and asked, "Ya hanya?" Shi kuma ya'amsa masa a taƙaice


Kaka sai zuba masa hira yake yi, shi kuma daga ya'amsa da Eh sai A'a, daga ƙarshe wayan sa ya ciro yana latsawa yana sauraron Kakan, a haka yaja dogon lokaci a ɗakin kafin ya miƙe yayi masa sallama ya fice.
[5/26, 12:54 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
             *FAMILY DOCTORS*
                         🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
  *NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
                 _NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝🏼‍*


*بسم الله الرحمن الرحيم*


*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞

```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A✍️*


*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

        
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_




        *EPISODE Sixteen*


           Sai ƙarfe 05:45pm. Ɗahira ta koma Office ɗin ta, Jakarta ta ɗauka da abinda zata buƙata ta fito ta rufe Office ɗin ta nufi Lifter


Tana sauka ta fita ta nufi inda motan ta yake ta buɗe ta shiga, rufewa tayi ta'ajiye jakar ta kan Kujeran me zaman banza sannan tayi ma motan keey, sai dai yaƙi tashi, ta daɗe tana gwadawa amma yaƙi ya tashi, guntun tsaki taja tana dafe goshin ta, lumshe idanuwan ta tayi na kusan minti 2 kafin ta buɗe ta sake gwadawa amma ina har yanzu be tashi ba, fitowa tayi tana ɗan waige-waige, sai kuma ta nufi gaban motan ta buɗe Garage ɗin ta soma tattaɓa wa, duk ta duba ko da akwai matsala ne amma ita a fahimtan ta bata ga komi ba


Tana nan tsaye a wajen tana ɗan sake duba wa taji sallama, sai ta ɗago kyawawan idanuwan ta wanda ƙwayan ciki suke ƙyalli sakamakon Hasken fitillun haraban wajen, amsa mishi tayi tana kau da kanta ganin kallon da yake mata tamkar zai haɗiye ta


"Are you all right? I've seen you here before. Are you still gone? What's going on?"


Ɗahira kamar baza tayi magana ba, sai kuma ta ga hakan be dace ba tunda taimakon ta zai yi, bata ɗago ba ta bashi amsa, "Wlh nima ban sani ba, kawai ta ƙi tashi ne".


Dr. Sa'id yace, "ok bari in duba miki mu gani ko?"


Babu musu ta matsa mishi yazo ya soma duba mata, shima ya daɗe yana taɓe-taɓen sa kafin yace mata, "wake up the car".


Shiga tayi tayi ma motar keey amma har yanzu ya ƙi tashi


"Ina ga dai motar ki sai ta ga bakanike coz myb wani matsalan ne babba wanda baza mu iya gane wa ba". Yayi maganar bayan ya rufe mata garejin


"To Nagode". Tace dashi tana ciro jakarta kafin ta rufe motan da keey


"In ba damuwa muje in rage miki hanya mana".


Ta tsinkayi muryan sa da har ta juya baya zata tafi


Jimmm tayi tana tunani domin ita mutumin ko kaɗan be mata ba, coz ta kula kallon tsiya ne dashi tun ganin sa na farko


Murmushi yayi yana takowa wajen ta yace, "don't worry. Ni ba siyar da kanki zanyi ba, ai kin san a nan nake aiki balle kice Ni ɗin baƙo ne, so ni ba baƙo bane babu wanda be San ni ba, My name is Dr. Sa'id Khan".


Kallon sa ta ɗan yi sai kuma tayi guntun murmushi tace, "ba damuwa mu je".


"Yauwa ko ke fa". Yafaɗa yana yin gaba wajen motar sa


Shi ya buɗe mata murfin motan da zumman ta shiga


Sai kawai ta ga abun yayi mata wani iri domin ita idan har ba Baffa ba basu taɓa hakan da wani ba, hakan ko kaɗan be burge ta ba, amma babu yanda zata yi ta shige ta zauna ya rufe mata


Shiga shima yayi yaja motar suka bar asibitin


A cikin motan ma babu wanda yayi magana cikin su, sai da suka ɗan yi tafiya kafin ya soma jan ta da Surutu duk a kan aikin nasu


Ko kaɗan ba ta jindaɗin surutun nasa


Shi kansa ya gane ba ta ƙaunar hiran sa; yanda take amsa masa maganar kamar baza tayi ba, don haka yaja bakin sa yayi shiru yana mamakin yarinyan, shi tunda ya ganta yaji ta burge sa matuƙa kuma yana son ƙulla alaƙa da ita, sai dai ya ga alamun hakan ba me yiwuwa bane duba da yanda take ɗin, da alamun tana da girman kai kuma zata yi wuyan sha'ani, a yanda ya fahimce ta kenan


Har suka kai ƙofar gidan su kafin ya tsai da motan


Kallon sa Ɗahira tayi cikin siririyan muryanta me kamar tana yanga tace,"Thank you, Dr."


He smiled and looked at her and said, "It's all right."


Buɗe motan tayi ta fito


Dai-dai lokacin su Baffa da Usman suka ƙariso wajen sun dawo sallan magriba


Gaba ɗaya kallon ta suke yi, yayinda Usman ya ɗauke kansa time ɗin da ta juyo zata sauke idanun ta a kansu, cikin gidan ya wuce batare da yayi wa Baffa magana ba


Shi kuma Baffan sai ya nufo ta fuskarsa duk babu walwala yana bin motan Dr. Sa'id da kallo da har ya ja ya tafi


Itama ganin ya taho ɗin ne yasa ta tsaya tana masa murmushi


Yana ƙari so wa idanun sa a kanta yace, "wannan kuma wane ne? ina Motar taki?"


Sai da ta kalli hanyar da Dr. Sa'id yabi kafin ta dawo da ganin ta kanshi tace, "Yaya Motata taƙi tashi ne wlh ban san kuma me ya faru ba, shi ne yace in zo ya rage min hanya".


Gaba ɗaya zuciyar Baffa ba ta mishi daɗi, tsananin kishi ne yake nuƙurƙusan sa a ransa, daƙyar ya"iya saisaita kansa ya sake jeho mata tambaya


"Aina Motar taki ta tsaya da har kuka haɗu dashi?".


"A cikin Hospital ɗin ne fa, kuma shima Dr. Ne cikin asibitin shiyasa ma na yarda na hau, but da farko ban yi ninyan hawa ba".


Murmushi Baffa ya kirƙiro yace, "let's go then".


Babu musu tayi gaba yana bin ta a baya duk da ita bata fahimci musabbabin tambayan nasa ba, amma ta san cewa shi ɗin Yayanta ne yana da right ɗin tambayar ta


Sai da suka shiga ciki kafin suka jera cikin gidan, Part ɗin su Ɗahira suka wuce


Suna shiga da sallama, Aunty Amarya dake zaune ita da Fadil suka amsa musu


"Aaah maraba da Mijina". Aunty Amarya tafaɗa tana yalwata fuskarta da fara'a


Baffa na faman shafa kansa yana murmushi ya ƙariso ya zauna a kan kujeran kafin ya gaishe ta


Ta'amsa masa cike da fara'a tana tambayar sa aiki


Itama Ɗahira sannu da gida tayi mata ta wuce ɗakin su ba tare da ta zauna ba


Su kuma suka ci gaba da hira suna kallo


Daga baya itama Umma ta fito aka ci gaba da hiran da ita


Baffa duk ya ƙosa Ɗahira ta fito amma tunda ta shiga bata sake fitowa ba, shi kuma ya zauna ne don ita amma tunda ta fito ta zuba abinci ta sake shige wa ɗaki, aiki take yi a ciki shiyasaka ta zauna nan ɗin tunda ba ta son hayaniya


Sai da aka kira sallan isha'i kafin Baffa ya miƙe tare da Fadil suka fito


Anan suka ci karo da Fadila itama dawowar ta kenan, gaishe da Baffa tayi


Ya'amsa yana faɗin, "Sarkin miskilanci sai yanzu aka dawo?"


Murmushi tayi tace, "Yaya kana son dai tsokana ta ko?"


Murmusawa yayi shima yana cewa, "ai gaskiya ne, kwana biyu ma gaba ɗaya kamar ba kya nan a gidan, rabon da in ganki na jima sai jiya a wajen meeting".


Fadil dake tsaye yana sauraron su yace, "ai Yaya wlh duk wanda ya auri Aunty Fadila ya bani, shiyasa ma zan ba ma Yaya K.B shawara tun wuri ya sauya ta don baza tayi daɗin zama ba idan ya aure ta, yana ji yana gani zata mayar da waya abokin rayuwanta ta ƙyale shi yay ta surutun sa.."


Kawo masa duka tayi dole yayi shiru yana matsawa gefe da sauri


"Wlh zan ɓalla ka a nan wajen; Ni sa'ar wasan ka ne Fadil?" Tafaɗa tana hararan sa cike da haushi


Baffa dariya yayi yace, "mai da wuƙan don Allah wasa yake miki".


Ƙwafa kawai tayi ta juya ta buɗe ƙofan Part ɗin nasu ta shige, tana jin Baffa yana faɗin


"Babu sallama kuma zaki tafi?"


Amma bata jiyo ta kalle sa ba bare ta tanka masa


Su ma wuce wa suka yi suka tafi, Baffa na shan dariyan Fadil da yaci gaba da maganar Fadilan.





             ⚫⚫⚫

             *08:45pm.*


         Suna zaune su huɗu a kan dainning suna cin abinci, babu me magana cikin su sai ƙaran cokula da Plate da ake ji


Kansa na ƙasa yana cakalan abincin kamar bazai ci ba, rabi kuma hankalin sa naga wayan sa yana kallon wani abu da aka tura masa, har kowa ya miƙe suka bar sa nan zaune be ma san sun tashi ɗin ba


Parlour suka koma sukai zaman su, Big Dady da Hajiya suna taɓa hira while Yusra kuma ta mayar da hankalin ta kacokan kan Film ɗin da ake yi a Bollywood, Film ɗin زوجة زوجي searese


A hankali ya miƙe ya taho cikin parlour'n yana shirin wuce wa ɗakin sa


Dady ya tsayar dashi yana faɗin, "Fodio come here we'll talk".


Juyowa yayi ba tare da yace komi ba ya taho ya zauna kan One sitter dake Facing ɗin nasu Dady


Ɗan gyaran murya yayi yana kallon sa kafin yace, "gobe ne zaka soma zuwa Hospital ɗin ko ya?"


Cikin ƙasa da murya kamar wanda yake tsoron yin maganan yace "No .. until Monday".


Jinjina kai Dady yayi kafin yace, "to har yanzu baka shirya aure bane? Tunda ga shi yanzu ka dawo gida Ya kamata ace kun ajiye mata kai da Baffa amma shiru har yanzu baka ce komi ba, kuma idan ban manta ba naji Baba yayi muku magana akan maganar auren ku".


Shiru Usman yayi be ce komi ba, sai ma sad da kansa ƙasa da yayi


Su kuma sun zubo masa ido daga shi har Hajiya suna sauraron abinda zai ce


Yusra dake kallo ma hankalin ta na wajen


Girgiza kansa Dady yayi don yasan halin ɗan nasa, don babu wanda be saba da miskilancin sa ba


"Ya kamata dai kusan kun girma tun kafin mu ce zamu nuna fushin mu a kan ku ku fito da mata, don baza mu zira muku idanu kuyi yanda kuke so ba, ka tashi kaje Allah yayi muku albarka". Dady ya sake faɗan hakan


Miƙewa yayi yana ɗan motsa bakin sa kafin ya nufi hanyan ɗakin sa


Su kuma suka rakasa da kallo har sanda ya gifta ta gaban su ya wuce


Ajiyan zuciya Dady ya saki yana miƙewa ya kalli Hajiya yace, "Let me in. I have a job."


Be jira amsar ta ba ya sake maida kallon sa kan Yusra yana cewa, "Auta ke baza ki je ki kwanta ba sai kin makara ko?"


Kallon sa tayi tana murmushi tace, "Dady zan kwanta yanzu za'a gama wannan sai inje in kwanta".


Gyaɗa kansa yayi kafin yayi gaba yana shigewa ɗaki


Itama Hajiyan bin bayan sa tayi suka bar Yusra ita kaɗai a parlour'n.
[5/27, 6:25 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
             *FAMILY DOCTORS*
                         🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
  *NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
                 _NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏼‍


*بسم الله الرحمن الرحيم*


*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞

```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A✍️*


*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈
        

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_





        *EPISODE Seventeen*


        *MONDAY*

                 *12:30pm.*

                Ya gama shirin sa na zuwa Office, yana sanye cikin wandon jeans blue, sai baƙar riga me gajeren hannu da ya sake fito da hasken skin ɗin sa sosai ya kuma ƙara masa kyau ainun, kwantaccen baƙin gashin sa sai shaining yake yi zuwa siririn sajen sa, babu abinda yake tashi ajikin sa sai sassanyan ƙamshi me tsananin daɗi ga duk wanda ya shiga hancin sa


Wrest watch yake ɗaura wa a tsintsiyan hannun sa me haske sosai da yalwan gashi, fuskarsa babu alamun fara'a ko kaɗan, har ya gama sakawa kafin ya zauna gefen gado ya soma saka Combat ɗin sa da ya kasance Blue Colour da igiyan sa suka kasance baƙi, bayan ya gama saka wa sai ya miƙe ya ɗau briafcase ɗin sa ya fito cikin ɗakin yana rufe wa


Babu kowa cikin parlour'n, sai ya nufi ɗakin Hajiya yayi Nocking yana jiran izni


Hajiya dake zaune kan gado wanda fitowar ta kenan daga Toilet ta ba da iznin shigo wa


Tura ƙofan yayi yana motsa bakin sa idanun sa a kan ta


Kamar yanda itama ta zuba masa idanu tana kallon sa


Takowa yayi a hankali har zuwa gaban ta kafin ya zauna gefen gadon, shiru yayi yana murza hannun jakan dake riƙe cikin fararen tafin hannun sa


Tsawon mintuna biyu Hajiya tana jiran taji yayi magana amma sai taga be da alaman yi, hakan yasa tace, "har ka shirya my son?"


Gyaɗa mata kai yayi yana kallon ta


She smiled and said, "God bless you and good luck."


"Ameen". Yafaɗa a hankali wanda a laɓɓan sa ta fahimci abinda yace


Miƙe wa yayi ya taka ya fice cikin ɗakin yana duba agogon hannun sa.


      Yana fita wajen motan sa ya buɗe ya shiga ya zauna sannan ya rufe, tada motan yayi yaja ya nufi bakin Gate


Tun daga nesa da me gadi ya hango zuwan sa ya miƙe da sauri ya buɗe masa Gate ɗin, yana fita ya ƙara Speed, cikin mintuna ƙalilan ya'isa haraban Hospital ɗin


Ɓude ƙofan yayi ya ziro ƙafafun sa a hankali sannan ya fito ya rufe, ya juya ya soma tafiya cikin taƙama da izza wanda zaka san a jinin sa ne.






               Shakira da Ayush dake tsaye jikin motan Shakiran, Ayush tana faɗa mata yanda suka yi da Baffa sai idanun ta ya faɗa kan Usman dake doso cikin asibitin, baki buɗe take bin shi da kallo


Hakan yasa itama Shakira ta mayar da hankalin ta inda Ayush ɗin take kallo, nan ta hangi Usman har ya shige


Ajiyan zuciyan da Ayush ta saki me ƙarfi ya saka Shakira take kallon ta cike da mamakin ta


"Lafiyan ki kuwa?" Ta tsinkayi muryan Shakiran da ta sake dawo da ita hayyacin ta


"Hmm ba lafiya ba, wane ne wannan Handsome Guy ɗin da naga kamar yana kama da Familyn ku?" Ayush tayi maganar tana tsare Shakira da idanu


Taɓe baki ita kuma tayi tace, "Yaya Usman ne".


"Kaiii amma wlh ya haɗu, Ni zan iya ce miki ban taɓa ganin mutumin da ya tafi da imani na a second ɗaya ba irin wannan, kai wlh ban taɓa ganin wanda komi nashi ya dace dashi ba sai wannan guy ɗin, Kai Amma wlh ban taɓa.."


"Ke dallah ya isa mana, meye haka kike zuba min hauka? ko dai hankalin ki ya gushe ne?" Shakira ta katse ta tana kallon ta cike da takaici


"Wlh baza ki gane bane, amma wlh yayi Ni dai ya gama dani".

Shakira tace, "to shikenan yanzu kenan baki yi da Yaya na sai wannan ko? Ko kin manta alƙawarin da ki kai min?".


Murmushin yaƙe Ayush ta saki tace, "laa I don't mean that. I'm just saying my opinion on this, but I'm not saying I'm better than Baffa, I like Baff.." Sai kuma tayi shiru ganin zata saki layi


Shakira da hankalin ta ma ba ya ga Ayush ɗin, tana kallon Fadila da tazo wuce su tayi saurin kwaɗa mata kira


Fadila dake tafiya waya a kunnen ta tajuya ta kallo su, sai kuma ta soma takowa wajen su har a lokacin tana ci gaba da wayan ta, sai da tazo dai-dai gun su sannan ta kashe wayan tana ɗago kai ta kalle su


Shakira murmushi tayi tace, "manyan gari wai ke idan ba an neme ki bane ba kya neman mu ko?"


Guntun murmushi kawai Fadila ta saki ba tare da tace komi ba illa gyara zaman jakan ta da take yi


"Yanzu muka gama magana da mutumiyar ki a kan ki ma". Shakira ta sake faɗan hakan still tana Murmushi


Kallon ta Fadila tayi da rashin fahimta kafin tace, "who?"


Shakira tace, "Ɗahira, ai ita nake nufi, kullum kuma idan na ganta sai na ce ta gaishe min da ke, Allah yasa tana faɗa

10 / 20