Chapter 14 Reading Nafisat Return Book Complete By Ummu Dahirah.txt Arewa Novels

Nafisat Return Book Complete By Ummu Dahirah.txt

Author :  Ummu Dahira Category :  New Hausa Novels 2026

Chapter   14 / 20

39K to 42K   out of 58K words

ba shiyasa hankalin su ya tashi da ganin yanda jikin sa yayi mugun zafi.


    Gaba ɗaya iyalan gidan sun hallara a bakin ƙofar ɗakin da aka shiga da Kaka, kowa hankalin sa a matuƙar tashe, da yawan su sun kasa zama sai zagaye suke yi, irin su Ɗahira kuwa sun kasa jure wa sai sharan hawaye suke yi.



    Su Abbu na ciki su ne masu duba shi, su kansu hankalin su ya gaza kwanciya, sabida halin da suka ga Kaka ya shiga, sun kasa shawo matsalar sai faman zufa suke yi.
[5/31, 6:58 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
              *FAMILY DOCTOR'S*
                         🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
   *NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
                 _NAFISAT ISMA'IL LAWAL._

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* 🧝🏼‍


*بسم الله الرحمن الرحيم*


*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞

```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A✍️*


𝗝𝗜𝗞𝗔𝗥 𝗟𝗔𝗪𝗔𝗟𝗜 𝗖𝗘✍️

𝗪𝗮𝘁𝘁𝗽𝗮𝗱: 𝗨𝗺𝗺𝘂𝗗𝗮𝗵𝗶𝗿𝗮𝗵👈

        
𝗦𝗔𝗗𝗔𝗨𝗞𝗔𝗥𝗪𝗔
𝑁𝑎 𝑠𝑎𝑑𝑎𝑢𝑘𝑎𝑟 𝑔𝑎 𝐹𝑎𝑚𝑖𝑙𝑦 𝑛𝑎 𝑔𝑎𝑏𝑎 ɗ𝑎𝑦𝑎. 𝗚𝗢𝗠𝗔'𝗦 𝗙𝗔𝗠𝗜𝗟𝗬.


          *NASIHA*
   _Sallah tana maganin duk cututtukan da suke samun zuciya. Ita ce haske mai kawar da duhu da zunubai. Abu Huraira ya ce, "Na ji Manzon Allah yana cewa:_
      _"Ku duba nan; idan ɗaya daga cikin ku yana da rafi a bakin ƙofar sa kuma yana wanka cikin sa sau biyar kullum, shin wata ƙazanta tasa za ta yi saura?" Sai suka ce, "Ba wata ƙazantar sa da za tayi saura". Sai ya ce, "Wannan kamar salloli biyar ɗin nan ne waɗanda da su ne Allah yake wanke zunuban mu"._
       _A sallah ne ake ganin tahƙiƙanin daidaituwa da adalci. Lokacin da Ladan ya yi kira da cewa: "ku yi gaggawa zuwa Sallah, ku yi gaggawa zuwa ga falala. Duk waɗanda sallar ta rataya a kansu, masu arziƙi da faƙirai, manya da yara, sarakuna da talakawa - dukan su za su taru a sahu guda ba wani bambanci tsakanin su, dukan su bayin Allah ne. Za su taru a bisa aƙida guda a ɗakin Allah, suna tuna Allah kaɗai, suna tawali'u gare shi._




        *EPISODE Twenty Two*


      Wajen awanni biyu da shigar da Kaka, kafin su Abbu su fito, sai dai basu ba ma kowa damar ganin sa ba, sabida a time ɗin sun yi masa alluran barci; yana cikin barci, domin ba sa son ayi hayaniya da zai ja har ya farka daga wannan barcin.



     Gaba ɗaya iyalan gidan sun kasa kataɓus a ranan, ko jirgawa sun kasa yi a baƙin ƙofar, sai da su Big Dady suka yi musu magana ne, akan "su tafi gida," sannan ne su Hajiya suka koma gida, yayinda su Ɗahira kuma suka koma bakin aikin su, but jefi-jefi suna kewayo wa ko Kaka ya farka.



     Har dare be farka ba, haka ilayan Doctor Al'ameen suka kwana a cikin wani hali a wannan ranan, sai washe gari aka samu ya farka, sai dai sosai suka shiga farin ciki a ranan, sabida Kaka ya samu sauƙi tamkar ba shi ba, babu wanda yayi tunanin zai tashi da lafiya haka, sai ga shi har magana yana iya yi, kuma yana iya yin sallan sa, domin tunda ya tashi ya buƙaci a kai sa yayi alwala, sai da ya gabatar da sallolin da ake bin sa, sannan ya samu yaci abinci daƙyar, aka ba shi magani ya sake komawa barci, sakamakon alluran da aka sake mishi, sabida ana son ya sake samun hutu sosai.



   A ranan haka mutane sukai ta zuwa duba sa, gaskiya Kaka na mutane ne, ba ga talakawan ba; ba ga attajiran ba, manyan mutane kama daga ko wani gari duk ana ta zuwa gaishe shi, har mutanen Maiduguri dangin su duk sun zo wasu daga ciki duba sa, su Hajiya Ikram, Hajiya Laila tun a ranan suka shigo Kaduna.


     Kwanan sa biyar a asibitin yana samun kulawa daga ƴaƴan sa da jikokin sa, ya samu sauƙi sosai, sai dai sun hana a mayar dashi gida dole sai ya ƙara samun sauƙi


Shi da kansa ya matsa musu dole suka sallame sa ya koma gida, a ranan sun ga mutanen anguwa, suna ta ɓulɓulowa gaishe da Kaka, da waɗanda suka je asibiti, da waɗanda ma basu je ba duk sun biyo sa gida.


    Bayan kwana uku da sallamo sa ne, wanda ta kama ranan Lahadi, ya saka aka tattaro masa iyalan gidan


Bayan kowa ya hallara ya soma musu jawabi akan abinda ya sa ya tara su, ba komi bane illa maganar aure


"Fodio da takwara na da ku zan so ma, har yanzu shiru ban ji kun kawo min maganar wacce kuke so ba?" Yayi maganar idanun sa a kan su


Shiru suka yi ko wannen su, don basu yi zaton akan hakan ya tara su ba. Sai da Abba yayi musu magana kafin Baffa ya buɗi baki yace, "Kaka Ni dai har yanzu bamu gama daidaitawa da wacce nake so ba, but I will bring it to you in a short time,  Calm down baza ka mutu ba insha Allahu sai ka ga auren mu".


Sosai maganar Baffa ya ba wa waɗansu dariya, sabida yanda yayi maganar cikin barkwanci


Abba kuma daƙuwa yayi masa yace, "ka ga naka Baba na, ba maganar wasa ne ya tara mu anan ba kaji ko?"


Duƙar da kai Baffa yayi yana sosa ƙeya yana murmushi


Haka zalika ma Kaka murmushin yayi yace, "to takwara na Allah ya kawo ta lafiya, sai dai a wannan gaɓar lokaci zan ba ku, sabida ina so nan da wata ɗaya kacal ayi auren ku mu huta, ba wai ku kaɗai ba, ina nufin har ƴan matan, gaba ɗayan ku zaku fid do da miji ayi muku aure".


Sosai maganar Kaka ya razana Ɗahira dake kusa dashi, dasauri ta ɗago kai ta zuba masa manyan idanuwan ta, kamar an tsikare ta kuma tace, "Kaka, do you mean us?"



Kallon ta yayi yana murmushi yace, "Yes, my wife, I hope all of you will be married in just one month, domin tabbas na san ba zan jima ba a duniyar nan, wannan ciwon ya ɗaga min hankali, shiyasa na yanke shawaran gaba ɗayan ku; ku fitar da mazajen aure sai a haɗa dana yayyin ku, zuwa nan da sati ɗaya na ba ku ko wacce sai ta turo wanda zata aura, kun ji ko?"


Gaba ɗaya amsa mishi suka yi, ban da Ɗahira da tunanin ta ma ya bar duniyar


Sai kuma Usman da tun sanda Kaka ya soma zancen, ya ɗaure fuskar sa tamau, ko ɗago kai ya ƙi yayi, bare kuma yasa baki.


    Daga haka Kaka ya sallami kowa taron ya tashi


Ai kamar jira Ɗahira take yi tuni ta bar parlour'n, sabida ruɗewa har so tayi ta bangaji Usman da yazo ficewa shima, Allah ya tsare hakan be faru ba ta dawo hayyacin ta


Wani banzan kallo ya watsa mata yayi hanyar Part ɗin su hannayen sa biyu cikin aljihu.


Ɗahira bata bi ta kansa ba, tunda ba ta shi take yi ba, yanzu hankalin ta duk a tashe yake, burin ta kawai ta ƙebe tayi tunani, "shin ita wa take dashi ne da zata kawo a matsayin miji? Wannan tunanin shi ne yayi matuƙar wargaza mata duk wani walwalan ta da nutsuwar ta.


     Tana shiga Part ɗin su, ta shige ɗakin su ta yaɗa zango a kan gadon ta, buga tagumi kawai tayi ta hau tunanin mafita, bata ankara ba sai ga hawaye


"Innallillahi wa'inna ilaihi raji'un! What is going to happen to me? By the time I get married no one has ever said he loves me, so who will I choose as my husband?" Tayi maganar a cikin zuciya tana me share hawayen da bayan hannun ta


Sai kuma ta saka hannu ta ɗauki wayan ta ta hau lalubo Numban Masoyin ta na ɓoye, wanda tayi serving Numban sa da My LOVE. Shiru tayi tana tunanin me zata yi, sai kuma ta soma kiran Numban, sai dai a kashe yake, wani yawu me ɗaci ta haɗiye cike da baƙin cikin da taji ya tokare mata maƙoshi, bata taɓa jin haushi irin na yau ba a duk sanda tayi yunƙurin kiran sa, amma wayan a kashe. wannan maganar me muhimmanci ne shiyasa ba ta so suyi sa a text message, tafi son ta Kira sa suna jin muryan juna, sannan ta faɗa masa abinda take so ta sanar masa.


    Sai dai babu yanda ta iya haka ta tura masa text message kamar haka:



_"Now everything is over between us. If you really want me, then I need you to explain yourself to me at this time. I don't want you to talk to me again unless you do what I need you to do."_
      


Abinda ta rubuta kenan ta tura masa, sai ta kwanta tana lumshe idanun ta, tare da zaman jiran reply ɗin sa.


       Bata fi mintuna goma da tura saƙon ba, sai ga reply ɗin sa ya shigo


Da sauri ta tashi zaune ta janyo wayan tana duba wa, sosai tayi farin ciki da amsar da ya bata, murmushi kawai take saki tana karanta wa


_"I am also waiting for this day to be beautiful, insha Allahu zuwa gobe zan bayyana miki kaina, just choose me when I come to you."_



Take tayi mishi sending ɗin time ɗin da zai zo, ƙarfe 03:00pm. Tana tura masa ta kwanta tana zuba murmushi, tunanin kawai yanda haɗuwar na su zai kaya take yi, take ta lumshe idanuwan ta tana sake dulmiya a kogin tunanin masoyin nata.






         ⚫⚫⚫⚫⚫


       Baffa dake tsaye kan benen Part ɗin su, yana tura mata text ɗin ya saki murmushi me fid da haƙora, ya sani dole ne wannan ranan zata zo, amma yanzu ya rigada ya gama shirya mata, ya shirya yanda zai fito fili ya bayyana ƙaunar sa ga masoyiyar sa, domin samun mallakan ta a matsayin matar sa, wanda ya daɗe yana tsimayen zuwan ranan


Wani kyakykyawar murmushi ya sake saki cike da farin ciki a ransa, shafa suman kansa yayi kafin ya soma taka wa ya wuce Part ɗin su, shiga yayi da sallama a bakin sa


Hajja Fatu dake zaune tana jiran dama shigowar sa ne, shiyasa ta zauna a parlour'n zaman jiran sa. Amsa mishi sallaman tayi tana murmusawa tace, "yauwa Baffa na, taho ka bani labarin surukar ta wa".


Dariya ya saki yana isowa wajen ya zauna tare da faɗin, "kai Hajja wai dama jira na kike yi?"


"Iyi wlh, ai tunda kafaɗa na kasa zaune na kasa tsaye ina so inji wacce me sa'ar ce ta same ka?"


"Uhmmm Hajja kenan! Ko dai Ni ne me Sa'ar dana same ta, ke kanki Hajja sai kin yaba da zaɓi na, because you will never have a Daughter-in-law like her, I know you will be very happy if you know who she is".



Cike da farin ciki Hajja tace, "yauwa ɗan albarka, wlh idan ka samo wacce tayi dai-dai da ra'ayina, you must finish everything for me, domin da ita ne zan riƙa ɗagawa a gidan nan, sannan zan fi kowa fariya".


Baffa dai murmushi kaɗai yake zuba wa, yana kallon Mahaifiyar ta shi


"Ina jin ka yarinyan ƴar gidan wane ne?"


"Hajja ba wata bace sai Ɗahira wacce kika sani na gidan nan".











_To fa nan ake yin ta. Ya kuke ganin za'a kaya?_


_Hajja zata amince da zaɓin Baffa?_


_ko kuwa Ɗahira zata amince da Baffa a matsayin Mijin ta?_


_me zai faru?_


_ta Comments ɗin ku kaɗai zan tabbatar da cewa kuna so in ci gaba, idan kuma ba kwa so falillahil hamdu, dama hutu nake son tafiya, sai mun haɗu a next week._
[6/2, 3:32 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
              *FAMILY DOCTOR'S*
                         🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
   *NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
                 _NAFISAT ISMA'IL LAWAL._

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* 🧝🏼‍


*بسم الله الرحمن الرحيم*


*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞

```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A✍️*


𝗝𝗜𝗞𝗔𝗥 𝗟𝗔𝗪𝗔𝗟𝗜 𝗖𝗘✍️

𝗪𝗮𝘁𝘁𝗽𝗮𝗱: 𝗨𝗺𝗺𝘂𝗗𝗮𝗵𝗶𝗿𝗮𝗵👈
        

𝗦𝗔𝗗𝗔𝗨𝗞𝗔𝗥𝗪𝗔
𝑁𝑎 𝑠𝑎𝑑𝑎𝑢𝑘𝑎𝑟 𝑔𝑎 𝐹𝑎𝑚𝑖𝑙𝑦 𝑛𝑎 𝑔𝑎𝑏𝑎 ɗ𝑎𝑦𝑎. 𝗚𝗢𝗠𝗔'𝗦 𝗙𝗔𝗠𝗜𝗟𝗬.





        *EPISODE Twenty Three*


       Zumbur Hajja ta miƙe sabida jin bazatan maganar ɗan nata, cikin tsantsan takaici tace, "kana kuwa cikin hayyacin ka Al'ameen? Ɗahira?.. Ɗahiran ce kake nufin zata zamo suruka ta?"


Shima Baffa miƙe wa yayi a wani irin yanayi, domin dai tabbas ya san akwai matsala tunda yaji Mahaifiyar sa ta kira sa da sunan sa na ainihi, cike da alhini yace, "Hajja to mene ne laifi idan na so Ɗahira? Na ga ai ita ƙanwa ta ce ko?.."


Be rufe baki ba Hajja tace, "kai da Allah ja can mara hankali mara tunani, wanda be san inda yake masa ciwo ba, ka rasa wacce zaka so sai Ɗahira? To ban amince ba, idan har Ni na haife ka, to, babu ta yanda za'a yi ka auri wannan yarinyan".


Sosai hankalin Baffa ya tashi da jin zantukan mahaifiyar na sa, cikin matuƙar damuwa yace da ita, "Hajja wai me Ɗahiran tayi miki ne da kike son jifan ta da baƙin fenti? Mene ne aibun ta shi nake son sani?"


A fusace take kallon sa tace, "aibun ta kake son sani ko? To na tsane ta ne ba na ƙaunar ta, ba na son ta zamo suruka ta, idan ko ka bari hakan ta faru, na rantse da Allah sai na tsine maka albarka".


"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!!". Abinda kawai Baffa yake faɗa kenan yana bin ta da kallo


Ita kuwa zama tayi tana huci kamar zakanya, sai kuma ta sake kallon sa tace, "umarni nake ba ka, idan har ka bari wani ma yasan da zancen kana son ta a gidan nan, to har abada bani ba kai, tun wuri kaje ka nemo wata ka aura, ko kuma Ni in zaɓa maka zaɓi na".


Baffa shiru yayi har yanzu idanun sa a kanta, sai dai a wannan lokacin komi ya tsaya masa cak daga duniyar tasa, be san sanda hawaye suka soma sintiri a fuskar sa ba, sai jin ɗumin su yayi saman kuncin sa.




      A dai-dai lokacin ne Shakira ta shigo part ɗin, kallon Yayan nata tayi dake hawaye, kafin ta mayar da idanun ta kan Hajja dake faman karkaɗa ƙafafu fuskarta a matuƙar ɗaure, nan da nan hankalin ta ya tashi ta ƙariso da sauri tana tambayan "me ke faruwa?"


Lumshe ido kawai Baffa yayi, sai ya buɗe ya ja ƙafafuwan sa ya nufi hanyar ɗakin sa, yana shiga ya faɗa kan gadon sa ya soma tsiyayar da hawaye, sosai yake kukan zuci, zuciyar sa na tafarfasa, babu abinda ke dawo masa a kwanya sai maganganun Hajja, "shin taya ma hakan zai faru? Taya zai iya cire ƙaunar Ɗahira da ya jima yana dakon sa? Ina sam bazai yiwu ba, idan kuwa hakan ta faru, ya tabbata mutuwa zai yi".





         **** **** *****


       Hajja duk abinda ke faruwa ta sanar wa Shakira


"Ai dama na sani, ba tun yau ba dole ne akwai soyayya a tsakanin su, I already understand Hajja."


Hajja said, "Then why didn't you tell me in the first place, sai da abu yayi nisa? Yanzu da ace ban tambaye sa ba haka zai je ya faɗa ma mutanen gida ga wacce yake so, kinga kuwa babu ta yanda za'a yi in hana faruwan hakan, na tabbata wlh sai anyi auren nan, tunda dama iyayen ku babu abinda suke ƙauna sama da su ga anyi haɗin zumunci a gidan nan, ina sam wlh ba dai da ɗana ba, dama Yusra ko Fadila yace yana so sai in bar sa, amma ya rasa wacce zai jajibo min sai ƴar A'ishah, maƙiyiya ta" .


Shakira tace, "Nima kai na Hajja na so raba su tun farko, ina wannan ƙawar tawa da muka taɓa zuwa da ita gidan nan Ayush?"


Hajja gyaɗa kanta tayi tace,"yes I understand her, wacce kuke sintiri a asibiti tare lokacin ciwon Kaka".


"Eh ita, wlh she really loves Baffa Hajja, kawai ki haɗa sa da ita tunda shima Yayan ya saba da ita".


Ɓata fuska Hajja tayi tace, "sam ɗana bazai auri ƴar talakawa ba, da ace dai suna da hali ne, amma tunda basu dashi ban amince da ita ba, Ni yanzu na tsara wacce zai aura, idan be samo wata ba, zan haɗa sa da Sa'adatu ne, yanzu ma ɗauko min wayata in Kira Mahaifiyar ta muyi magana, gwara ta dawo nan ko ya ganta ya so ta".


Tashi Shakira tayi don ɗauko mata wayan, duk da a ranta bata ji daɗin haɗin ba, amma ko ba komi Yayan ta bazai auri Ɗahira ba.




    Sa'adatu yarinya ce wajen ƙanwar Hajja Fatu, Hajiya Amina wacce tayi aure a Legos. Dama tun farko Sa'adatu ta jima tana ƙaunar Baffa, sai dai shi ya ƙi amince wa da ita sabida bata yi masa ba, wayewar ta yayi yawa, akwai ta da rawan kai.








⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫



       *WASHE GARI*

     A ranan Ɗahira ta tashi ne cikin walwala da farin ciki, burin ta kawai anjima yayi ta sanya masoyin nata a idanu, koda ta gama shiryawa cikin Abaya baƙa me kwalliyan stones, sai ta yafa gyalen shi ta saka flet shoes, sallama tayi wa Aunty Amarya ta fito ta shiga cikin motan ta


Koda ta isa asibiti Direct office ɗin Baffa ta wuce, sai dai babu shi, domin Office ɗin ma a rufe yake, tayi mamaki sosai amma bata tsawwala ba, sai ta wuce Office ɗin ta.






       ⚫⚫⚫


    Ɗan adai-daita sahu ne ya sauke Ayush a bakin Hospital ɗin, kuɗin sa ta biya sa sannan ta shigo cikin asibitin


A dai-dai lokacin ne Shakira ta shigo itama da motan ta, parking tayi ta fito tana gyara zaman mayafin ta


Hango ta da Ayush tayi ne yasa ta nufo ta tana washe baki, tana ƙarisowa suka soma gaisawa kafin suka jero suka nufi cikin asibitin,

14 / 20