Chapter 7 Reading Nafisat Return Book Complete By Ummu Dahirah.txt Arewa Novels

Nafisat Return Book Complete By Ummu Dahirah.txt

Author :  Ummu Dahira Category :  New Hausa Novels 2026

Chapter   7 / 20

18K to 21K   out of 58K words

yi


Sai da tayi son ranta sannan tace, "Yaya har akwai macen da zaka kasa sanar mata ƙaunar ka gare ta sabida kwarjini? Shin me tafi ka dashi ne? Kyau ko nasaba ko kuwa kuɗi? Ni na tabbata Yayana duk kwarjinin ta baza ta kai ka ba, kai dai kawai kace kana jin tsoron ta; abun kuma da ban san ka dashi ba".


Baffa yace, "baza ki gane bane Sister, duk abinda kika lissafo tana dasu, sai dai kamar yanda nace miki kwarjinin ta da cikan kamalan ta ya zarce duk tunanin namiji ya iya tunkarar ta da soyayya, a kullum idan nayi yunƙurin zuwa gare ta da soyayyata sai inga girman ta da kwarjinin ta bazai bari na sanar mata ba, yanda nake ji a gaban ta da bugawar zuciya da zaran nayi yunƙurin sanar mata sai in kasa, sau ba adadi nayi hakan amma na gaza".


Kallon Yayan nata kawai take yi cike da tausayin sa har yayi shiru, sannan ta ɗaura da cewa, "How can I help you find her love? Why don't you let me know who I am; and I promise to tell her, sannan kuma zan taya ka yaƙi har sai ta amince da kai, Yaya ban ga macen da zata ƙi son ka ba komin kyan ta komi kwarjinin ta kuwa, sai dai idan har baka faɗa mata ba, Yaya ka cire tsoro ko fargaba ka sanar mata don Allah".


Murmushi yayi yace, "na gode ƙanwata, haƙiƙa nasan kina son farin ciki na, sai dai bazan iya faɗa miki ko ita ɗin wace ce ba, but I promise I will try to tell her."


Murmushi tayi kawai ba tare da tayi tunanin matsa masa akan sanin meyasaka be son sanar mata ba? Ita a komi nata tana ma mutum uzuri maybe yana da dalilin hakan ne


"To yaya na gane, but hurry up and tell her because soon Kaka will start talking about your marriage, kuma ka ga idan baka sanar mata ba za'ayi babu kai haka zakai ta zama a Gwauron ka".


Baffa laughed and said, "Well shikenan my sister, but ni nafi son nayi aure lokacin da kema za kiyi".


Zaro idanu tayi tace, "Yaya baka shirya auren ba kenan? Because I don't have a real boyfriend."


"Hmm you're just saying, duk da ban taɓa ganin kin kawo kowa gida ba amma fa ina da tabbacin kina da masoyi don kuwa irin ki ba su rasa masoya".


Shiru kawai tayi a wannan karon tana murmusawa, sai kuma ta duƙar da kanta tana ci gaba da juya spoon ɗin hannun ta cikin abincin


"Talk to us My dear, when will you show me my son-in-law?"


Ɗago kai tayi tana kallon sa tace, "Yaya Ni bani da gwani har yanzu, amma dai ka taya ni da addu'a".


Sanyi yaji cikin ransa, cike da nuna tausayawan sa a fuska yace, "My dear Sister, I promise to help you. I pray to God to bless a good husband who loves you so much, kuma Allah yasa nan kusa za kiyi aure baza kiyi nesa damu ba".


Dariya tayi cike da farin ciki tace, "kamar ka sani Yayana ko kaɗan ba na Son auren nesa sabida ba na Son nayi nesa da ku, sannan ba na son na dena aiki a hospital ɗin mu, Burina yana da nasaba da aiki cikin Hospital ɗin mu, ka ga kuwa ba na so na zama kamar Aunty Zulaiha da tabar aiki lokaci ƙanƙani, tayi nisa babu daman ci gaban ta a nan, nima ina so ayi alfahari dani cikin Family na; ya kasance ina ba da tawa gudunmawa wajen haɓɓaka shi".


Filled with her love Baffa said, "God fulfill your dream My dear sister".


"Ameen my brother, we should hurry back because my waking time is near, and I want to check on my patients."


"To sarkin aiki ba kya gajiya?"


Murmushi tayi kawai tana ɗaukan Holandia tana sha, bayan ta gama ta'ajiye tana kallon sa tace,"Come on, I'm full."


Ɓa ta fuska yayi yana kallon abincin gaban ta yace, "Baki ci da yawa ba ai?"


Marairaice fuskar ta tayi tace, "Yaya na ƙoshi ne".


"Ok to tashi muje nima na ƙoshi tunda kin ƙoshi".



      Sai da ya biya kuɗin sannan suka fito suka shige cikin motan yaja suka nufi Hospital ɗin


Suna shiga haraban Hospital ɗin suka fito ya rufe motan suka jera suka nufin cikin asibitin


A reception Ɗahira ta hango aunty Zainab, tayi saurin zuwa wajen ta tana cewa, "Aunty Zainab".


Juyo wa Aunty Zainab tayi tana kallon ta sai ta faɗaɗa fara'an ta tana faɗin "a'a! my sister. I have been asking Fadila Ni kam ban ganki ba tunda kuka fara aiki".


Dariya Ɗahira tayi tana cewa, "wlh kuwa Aunty nayi ninyan zuwa har Office ɗin ki, to, aiki yayi yawa I don't have time."


Aunty Zainab kallon Baffa da ya ƙariso wajen su ya tsaya yana kallon su tayi tace, "oh ka ga masoya! ina kuma kuka je?"


Ɗahira kallon Baffa tayi suka haɗa idanu, sai ta saki dariya tana mayar da idanun ta kan Aunty Zainab tace, "aunty kenan abinci fa muka je ci da Yaya".


Smiling, Aunty Zainab said, "Hmm Na ga alam ai".


Baffa dake faman shafa kansa yace, "kin ji ABU da wata magana don mun fita da ƙanwata za kiyi mana fassara daban?".


Ɗan waro ido tayi tace, "wai laifi ne don nace masoya kaji min yara?"


Yanda tayi maganar yasa su dariya gaba ɗaya


Still Ɗahira na dariyan tace, "Where's Jinior?"


"Shigo wa ta kenan itama Fadila ta shigo shi ne ta'amshe shi".


Baffa kallon Ɗahira yayi yace, "mu je kin ji My sister Kar mu biye mata".


Hararan sa Aunty Zainab tayi tace, "to babu inda zata je.. kaje kai".


Shima hararan ta yayi yana cewa, "ke fa kina son raina ni fa, wai ba tare kika gan mu ba?"


"Eh tare na gan ku amma aiken ta zanyi".


Kafin yayi magana Ɗahira tayi saurin cewa, "Yaya ka je zan zo har Office ɗin ka".


Gyaɗa mata kai kawai yayi jin wayan sa na ringing, zaro wayan yayi cikin aljihu yana yin gaba abin sa bayan ya ɗaga mata hannu alamun ya tafi


"Hmm Ni dai ina mamakin wannan shaƙuwa na ku, anya.. anya.."?


Ƙwalalo idanun ta Ɗahira tayi tana kallon ta tace, "kai Aunty babu daman Yaya ya nuna wa ƙanwar sa kula wa sai da wani abun? Ni fa na ce miki abinci muka je ci".


"To ai nima ba fitar da kuka yi bane nake magana, mu je kawai". Aunty Zainab ɗin taƙarike maganar ta tana yin gaba


Ɗahira tabi bayan ta suna sauya hiran su


Office ɗin Aunty Zainab ɗin suka shiga, bayan sun zauna ta ɗauko mata wasu files ta miƙa mata


"Ga shi don Allah Ɗahira, ki kai wa Dr. Said don ba na son ya sake damu na".


Amsar files ɗin Ɗahira tayi tana kallon ta tace, "Aunty who is Dr. Said?"


"Aff baki san shi ba ashe, yana nan office ɗin sa na kallon nan wajen ta hannun dama".


"Ok sai na sake zuwa kenan Aunty?" Tafaɗa tana miƙewa tsaye


Murmushi Aunty Zainab tayi tace, "Tom My Sister, ki gaishe dasu Kakus me ran ƙarfe".


Dariya tayi tace, "insha Allah zai ji".


Daga haka ta fice bayan sun sake sallama.



        Tana fita kamar yanda Aunty Zainab tace mata hakan tayi ta nufi hannun daman ta, tana zuwa ta soma dudduba sunayen Offices ɗin, nan kuwa taci karo da sunan sa a saman nashi Office ɗin, Nocking ta soma yi


Dr. Said dake zaune yana ma wata budurwa bayani yayi saurin ɗago kansa cike da fargaba, kallon Budurwan yayi yace, "Yi maza ki kwashe magungunan nan ki saka a jaka".


Babu musu kuwa ta kwashe ta zuba a jakan ta


Shi kuma ya gyara zaman sa yana rufe Files ɗin dake gaban sa tare da kifa wa sannan ya ba da umarnin shigowa


Turo ƙofan Ɗahira tayi da sallama ta shigo


Idanun sa ƙyar a kan ta ya'amsa mata sallaman yana kallon ta, duk da be santa ba amma ya ga tana masa kama da Familyn Dr. Al'ameen


Ita kuwa ƙariso wa wajen Table ɗin sa tayi ta miƙa masa files ɗin tace, "ga shi Aunty Zainab ta ce in kawo maka".


Sai a lokacin ya ɗan saki fuskar sa yana bin ta da wani irin kallo, cike da murmushi a face ɗin sa ya miƙa hannu ya'amsa yace, "Ok thanks".


Juya wa kawai tayi ta fice ba tare da ta kalli ko budurwan dake zaune ba


Har ta fice yana kallon ta cike da tsananin burge sa da tayi, sosai Ɗahira ta ɗauke masa hankali da kyawun ta da cikan halittan ta, musamman ma da take siririyan mace, domin yana ƙaunar irin su. sai faman doka murmushi yake yi ya kasa ɗauke kai daga ƙofan da ta fice


Sai da budurwan nan ta buga table kafin ya dawo hayyacin sa


Ɗan shafa kan sa yayi yana kallon ta kafin yace, "kin tabbatar cikin nan be wuce 5 Months ba?"


Kallon sa tayi a yatsine kafin tace, "Dr. Na rigada na faɗa maka wata 4 ne".


"Ok bari in zo".


Miƙe wa yayi ya nufi wani dogon sip ya buɗe, ya soma bincika kayan aikin da zai yi mata amfani wajen cire mata cikin.


         Wannan shi ne halayyan Dr. Said, yana cire wa ƴan mata ciki ba tare da sanin kowa a cikin a sibitin ba, domin doka ne idan har aka kama ka kana irin wannan cin amanar za'a kore ka, asibitin kwata-kwata basu yarda da aikata wannan zunubin ba.






                 ⚫⚫⚫


     Ɗahira sai da ta koma Office ɗin ta tayi sallah kafin taje ta ƙara duba patients ɗin ta, tana dawowa ta haɗa komi nata da abinda zata buƙata ta fito ta rufe office ɗin


Office ɗin Baffa dake hawa na biyu ta nufa, dai-dai zata shige cikin office ɗin Yusra ta fito nata office ɗin dake kallon na Baffa, kallon juna kawai su kayi suka ɗauke kai, Yusra har da wani sake tamke fuska ta wuce abin ta tana jan tsaki


Ɗahira juya kanta tayi tana kallon ta cike da mamakin ta, har yanzu ta rasa meyasaka Yusra take nuna mata tsana


Bata gama tunanin ta ba Baffa ya buɗe ƙofan yana kallon ta


Murmushi ta ƙirƙiro tana kallon sa tace, "Yayana na gama".


"Ok Muje Nima tafiya zan yi na gama na yau kuma".


Sai da ya rufe ƙofan kafin suka tafi.
[5/23, 11:16 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
             *FAMILY DOCTORS*
                         🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
  *NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
                 _NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻‍


*بسم الله الرحمن الرحيم*


*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞

```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A✍️*


*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈
        

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_


_Ga masu min magana akan littafin JARUMAI kuyi haƙuri don Allah an samu matsala ne shiyasa na dakata amma insha Allahu zan ci gaba very soon._





        *EPISODE Twelve*


      Fitowar ta kenan daga wanka taji wayan ta tayi ƙaran shigowar Text, kallo ɗaya tayi wa wayan ta ɗauke kai ta nufi gaban dressing mirror, zama tayi kan stool tana tsane gashin kanta, bayan ta gama sai ta ɗau handrayer ta soma busar da dogon baƙin gashin nata me tsananin santsi, sabida santsin sa ne ma ba ta yin kitso sai dai ta riƙa gyarawa


Ajiye handrayern tayi bayan ta gama ta soma shafa Lotions ajikin ta, tana gamawa tayi Light makeup a baby face ɗin ta, sai ta miƙe ta ciro kayan ta tasaka


Doguwar riga ce robber kalan ruwan hanta, babu kwalliya a rigan ko ɗaya sai dai wuyan V yake dashi wanda aka saka masa bakin less white colour, haka ma dogon hannun a ƙarshen an saka masa bakin less, Hula ta saka fari wanda ya kasance na rigan ne, tayi kyau sosai kasancewar ta kyakykyawar


Wayan ta kawai ta ɗauka ta fito Parlour.



     Fadila na zaune tana cin abinci at the same time tana latsa wayan ta


She Sit on the One sitter next to Fadila on the Two sitter


Ɗan kallon ta kawai tayi sai ta ɗauke kanta ta mayar kan plasma t.v dake aiki babu me kallo, shiru tayi na ɗan wani lokaci sai kuma ta ɗago wayan ta ta soma latsawa


Da text ɗin da ya shigo wayan ta ɗazu ta fara cin karo, har zata wuce kuma sai ta ga kamar da number akayi mata Text ɗin wanda ada azaton ta MTN ne su kayi mata


Buɗe wa tayi da mamaki take kallon text ɗin, har sake murza idanuwan ta tayi tana sake ƙura manyan idanun nata, jikin ta na rawa ta soma karanta wa:



_"Aslm alaikum ya ke kyakykyawa abar so ga kowa, za kiyi mamakin ganin wannan text ɗin nawa aduk lokacin da ya riske ki, amma ba abun mamaki bane domin an ce me son ɗan tsuntsu shi ke bin sa da ji fa, Ɗahira na daɗe da ƙaunar ki cikin zuciya ta, sai dai har yanzu na kasa fitowa fili na sanar miki, ba don komai ba sai don ban san ya zaki amshe Ni a matsayin Masoyi ba, but know that I love you and I will continue to love you until my breath goes out, I Love You .. I love You with all my heart."_

        _MASOYIN KI✍️_



Ta maimaita text ɗin ya fi sau biyar, gaba ɗaya ta ruɗe domin abin da bata taɓa gani bane a gare ta, tunda take babu wanda ya taɓa nuna yana son ta kuma babu wanda ya taɓa tura mata text da sunan masoyin ta, hakan ne ya saka ta shiga wannan ruɗun tare da bugawar zuciya me tsanani


Zumbur ta miƙe ta nufi ɗakin su


Fadila tabi bayan ta da kallo cike da mamakin sauyawan ta lokaci ɗaya, amma sai dai bata ce komi ba ta maida hankalin ta kan wayan ta.




    Tana shiga ta nufi kan gadon ta ta zauna, sake ɗago wayan nata tayi ta sake karan ta text ɗin


"Anya wanda ya turo text ɗin nan ba mistake yayi ba?" Tafaɗa cikin sanyin murya tana bin wayan nata da kallo


Ƙure Numban tayi da idanu ko za ta san me irin shi but ko kaɗan bata taɓa ganin ma irin Numban ba, domin kuwa sabon Numban da MTN suka fito dashi ne me 091


Har ta latsa da ninyan kira taji ko wane ne sai kuma ta yanke da sauri don bata san me zata ce ɗin ba ko da an ɗauka, zuciyarta ta bata shawaran kar ta sake ta kira wataƙil mistake ne aka yi, kuma be kamata ta kira ɗin ba, da haka ta'ajiye wayan ta kwanta tana tsira wa waje ɗaya idanu cike da tunani


Da sauri kuma ta tashi zaune tana faɗin, "amma kuma ya kira suna na ai, Of course I am. This text is for me, but who is it?"


Duk yanda taso yin tunanin gano wanda zai iya mata amma ta kasa, koma wa tayi ta kwanta tana ajiyan zuciya.






           ⚫⚫⚫


  Yana kwance saman kujeran sa yana faman latsa wayan sa yana murmushi


Wayan ce ta soma ringing hakan ya saka ya dakata da abinda yake yi yana kallon baƙuwar Numban da aka kira sa, shiru yayi na ɗan wani lokaci kafin yayi peacking call ɗin ya saka a kunne


Daga can ɓangaren muryan mace ce ta doki dodon kunnen sa


"Aslm alaikum".


"Wa'alaikis salam". Slowly he gets up and sits up


She smiled and said, "Do you know who Dr. Al'ameen Abubakar Al'ameen is?"


Baffa da yayi tsimi yana sauraron muryan ta sai be ce komi ba


Hakan ya bata damar ci gaba da faɗin, "My name is Dr. Ayush Abdulkarim and I work at your Family Hospital." Sai kuma tayi shiru tana tunanin abinda zata ce


Baffa yace, "to Allah yasa dai lafiya? But I don't know you."


She smiled and said, "Yes, you will never know me because I have just started working at the hospital, but idan har ka bani dama zan iya bayyana maka kai na domin mu san juna, tunda ina son alaƙar mu tayi nisa ne, that's why." so I asked for your number and I called you ".


Shiru yayi cike da mamakin ta


"To me zai sa ta so ƙulla alaƙa dashi?.."


Be gama guntun tunanin sa ba ta katse sa da faɗin, "I'll meet you tomorrow insha Allah, I'll come to your office. Byee Take care." Bata jira me zai ce ba ta kashe wayan


Shi kuma ya ciro wayan yana kallo, ya jima a haka yana tunani kafin ya'ajiye wayan ya miƙe ya shige toilet don ɗauro alwala.






⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫


Dariya suka kwashe dashi har da tafa wa


"Wow gaskiya kin yi ƙoƙari Ayush, amma kina ganin zaki iya jawo hankalin shi gare ki har ya manta da wancan shashashan?"


Murmushi me ma'anoni da dama Ayush ta saki tana kallon Shakira tace, "ke dai ki zuba idanu ki gani, da zaran mun haɗu ma zan sanar masa ina ƙaunar sa don ma ya sani tun yanzu".


Dariya Shakira tayi tace, "Thanks.. sai kuma mu jira muga shirin namu zai yi aiki ko kuwa.."


"Idan ma bazai yi ba sai mu sauya salo". Ayush tafaɗa itama tana dariyan


Jinjina kanta Shakira tayi cike da jindaɗi sannan tace, "Is it tomorrow when we meet?"


"Yeah insha Allah". Cewar Ayush tana ɗaukan jakan ta sannan ta buɗe murfin motan


Daga nan sallama su kayi ta fito cikin motan, ita kuma Shakira taja tabar ƙofar gidan su Ayush ɗin


Tana nan tsaye tana ɗaga mata hannu har ta ɓace ma ganin ta, murmushi ta saki tana faɗin, "Uhmm Dama ta biyu kenan, yanzu komi zai soma min daɗi, tabbas Buri na zai yi saurin cika, da wannan shirin naki Ni kuma zan cika tawa Burin".


Dariya tayi ta shige gidan su


Babban gida ne me sasa biyu, na farkon shi ne na mahaifin ta, inda akwai ɗakuna Huɗu da kichen a bakin ƙofan gidan; sai kuma bayi dake can ƙuryan sasan wanda aka rufe sa da fale-fale


Ƴaƴan Baban su su goma ne maza da mata kuma itace ta Biyar, sannan duk mahaifiyar su ɗaya.



7 / 20