Author : Ummu Dahira Category : New Hausa Novels 2026
Office ɗin Dr. Rahab abokiyar aikin ta tashiga, files ɗin dake hannun ta takai mata ta fito ta nufi hanyan da zai sada ta da Lifter
Usman na ciki yana ƙoƙarin danna numbobi ta'iso wajen, idanun su ne suka sake haɗe wa waje ɗaya, yayinda suka bi junan su da wani irin kallo me cike da tsantsan tsana
Duk da yanayin da yake ji da ganin wannan idanuwan nata masu matuƙar faɗar masa da gaba but yaƙi ya ɗauke nasa idanun a kan ta, illa aika mata da saƙon tsanar da yake yi
Har sai da ƙofan ta kusa rufe wa kafin Ɗahira ta janye idanun ta taci gaba da tafiya ta nufi Steps, ta gummaci ta ɓata time ɗin ta wajen sauka ta bene da ta haɗa hanya da mutumin da zuciyarta tafi tsana a rayuwan ta
Ko kaɗan ba ta ƙaunar haɗuwa dashi a rayuwan ta, musamman yanzu da ta ganshi ya fito a Office ɗin dake kallon nata wanda ta tabbatar da cewa nasa ne, wani irin baƙin cikin hakan taji a ran ta
Tsaki ta dinga jerawa har ta sauka ƙasa ta fita daga cikin Hospital ɗin ta nufi parcking lot, motan ta tashiga taja tabar asibitin gaba ɗaya.
[5/29, 6:40 AM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTORS*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏼
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_
*EPISODE Nineteen*
Horn tayi a bakin tanƙamemen Gate ɗin gidan su
Babu ɓata lokaci me gadi ya buɗe mata
Ta kutsa hancin motan cikin gidan, yayinda ta nufi parcking space Direct ta faka motar, jakar ta; ta ɗauka da wayan ta tafito ta rufe ƙofan motan tare da saka mata keey, mayafin ta tagyara kana ta nufi cikin gidan cikin tafiyan ta na tsantsan yanga wanda ya zame mata jiki
Usman dake cikin motan sa yana amsa Call yabi ta da kallo time ɗin da tazo ta gifta shi, kallon ta kawai yake yi har ta ɓace wa ganin sa kafin ya ɗauke kansa, a ransa kuwa yana jan tsaki cike da jin haushin kallon ta da yayi, shi mamaki ma take bashi ta yanda take irin wannan tafiyan tamkar baza ta taka ƙasa ba, kai da gani kasan tana ji da tashen ƙuruciya da tsantsan yanga, wanda shi a ganin sa iya Shege ne, be san cewa Nature ɗin ta bane hakan, ya riga ya zama jinin jikin ta, har a maganar ta da komi nata cikin yanga take yin sa tare da sanyin jiki sosai, shiyasa komi nata daban ne, she has a very classy class.
Wayan sa ya janye daga kunnen sa ya fito cikin motan ya rufe, jin ana kiran sallah sai ya nufi bakin famfo na can wajen masu gadi yayi alwala ya fice a gidan zuwa masallaci.
⚫⚫⚫
Ɗahira na shiga cikin parlour'n su da sallama a bakin ta, babu kowa cikin parlour'n don haka Direct cikin ɗakin su ta nufa
Tana shiga bata zauna ba ta shige Toilet bayan ta ajiye jakar ta da wayan ta, alwala ta ɗauro ta fito
Time ɗin ne itama Fadila ta shigo cikin ɗakin don itama dawowar ta kenan, itama jakar ta ta'ajiye ta nufi Toilet ta ɗauro alwala, tazo ta shimfiɗa sallaya kusa da na Ɗahira ta tada sallah.
Ɗahira ta soma idar wa, don haka ta miƙe ta fice cikin ɗakin, ɗakin Maman ta tanufa
Tana zaune a kan sallaya tana azkar, sallaman da Ɗahiran tayi ta amsa mata tana bin ta da kallo
A kan sofa ta zauna tana kallon Maman nata har ta ida azkar ɗin
Sannu da gida Ɗahira tayi mata
Ta amsa mata tana tambayan ta "har kun dawo?"
"Eh Mama".
"So Masha Allah, what is your job? Is there no problem?"
She smiled Ɗahira and said, "It's all right, Mama."
Gyaɗa kanta ta ɗan yi kafin tace, "Then go to the kitchen and get some food, and if you leave it later, then."
Gyara kwanciyar ta Ɗahira tayi saman dogon kujeran tana ɗaura hannun ta saman kanta tace, "I'll eat later."
Aunty Amarya bata sake cewa komi ba taci gaba da addu'o'in ta, har sanda ta gama ta tashi ta fice cikin ɗakin.
Ita kuwa Ɗahira tana nan kwance tana tunane-tunane cikin ranta, kuma duk tunanin nata akan Masoyin ta ya ƙare, zuciyar ta na ƙwaɗaita mata son ganin shi matuƙa, tana son sanin ko wane ne but ya ƙi amince wa su haɗu, Allah ya gani tana ƙaunar sa itama, zata so su haɗu ko dan ya nuna mata soyayyar da yake mata a zahiri ba a cikin waya ba, har yanzu ba su taɓa yin waya ba, ko ta kira ba ya shiga, amma kuma idan ta tura text babu daɗe wa yake turo mata reply.
Numfashi taja tana juya kwanciyar nata fuskarta ƙunshe da murmushi.
Aunty Amarya da ta shigo tana kallon ta, kaɗa kai kawai tayi bata ce mata komi ba, sai da ta daidaita kanta a sallaya sannan ta sake duban ta tace, "To idan kin gama murmushin da saƙar zucin; ki tashi ki je kiyi sallah, Abbun ku ya dawo ma yana neman ki".
Murmushi kawai Ɗahira tayi tana kallon Maman nata da har ta soma sallan ta tamkar ba ita ce tayi maganar ba, tashi tayi tana sosa kanta cike da kunya da ya kama ta jin abinda tafaɗa mata, ta fice a ɗakin.
Bayan kowa ya idar da sallan sa fitowa suka yi suka hallara a kan dainning, cike da nishaɗi suke gudanar da dinnern su, kai da gani kasan suna farin ciki, musamman yanda Abbu ke ta jan su da hira yana tsokanar su don shi dama al'adan sa ne tsokanar ƴaƴan sa, yana da son yara kuma ba ya da ɗaurewar fuska ga iyalan sa.
A haka har suka gama cin abincin suka dawo Parlour suka yi zaman hira, in ka ɗauke Fadila da tuni ta shige ɗaki abun ta, don ita bata cika zaman hiran ba ne sai ta ga dama, kuma ko ta zauna baza ta ce uffan ba, wayan ta ko t.v su ne kaɗai abokan hiran ta, wani lokacin kuma idan an sako ta takan saka musu baki ko tayi murmushi, babu me damuwa da halin nata tunda ba baƙon abu bane a gidan nasu, ba ita kaɗai ba gaba ɗayan su hakan a jinin su yake, sai dai nata abun ya girmama ne, to zan iya cewa halin su ɗaya da Usman domin miskilancin ya girmama.
⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫
*Ƙarfe 11:30pm.*
Lokacin ne Hajja Fatu ta tura ƙofan ɗakin mijin ta tashiga da sallama
Be ɗago kai daga aikin da yake yi cikin Laptop ba ya amsa mata
Taho wa tayi ta samu wuri gefen gadon kamar yanda shima yake zaune, ta zauna tana kallon Laptop ɗin, duk da kuwa ba ta ganin abinda yake yi a ciki amma hakan be sa ta ɗauke kanta ba, illa ma ƙoƙarin leƙa wa da take son yi
Shi kuma jin tayi shiru sai ya ɗan ɗago kansa kaɗan ya kalle ta, ganin tana leƙa masa Laptop sai yace, "lafiya dai Hajjaju, what do you want to see?"
Ɗan ja da baya tayi cikin basarwa duk da kuwa taji kunyan kama ta da yayi, sai lanƙwaye murya da tayi tace, "to Abban Baffa laifi ne don na leƙa naga me kake yi? Don't forget that I am also a doctor."
"Eh ke doctor CE sai aka yi ya ya? Ko an ce miki wannan aikin Hospital ne?" Yayi maganar yana yatsina fuska
"Uhmm Abban Baffa why are you like this to me? Mene ne dalilin ka na son ɓoye min sirrin ku? Kar ka manta fa Ni matar ka ce kuma uwar ƴaƴan ka, sannan a duk matan gidan nan Ni kaɗai ce wacce tayi ilmi me zurfi har kuma take ci da gumin ta, idan baku saka Ni a al'amuran ku na taimaka muku ba; to wa zaku saka? Wlh ba na jin daɗin abinda kake min kwata-kwata, na kula ko kaɗan kana ɗauka ta wata aba ce daban saɓanin yanda ni na ɗauke ka". Hajja Fatu taƙarishe maganar nata cikin tsantsan damuwa da ya nuna a muryan ta, tabbatan dai abinda mijin nata yake mata ba ya mata daɗi
Murmushi Abba ya saki cike da mamakin matar tasa, shi be ga abinda yake mata ba da koda yaushe idan taga yana aiki sai tayi ƙorafi, musamman idan ya nuna mata aikin be shafe ta ba duk lokacin da ta buƙaci taya sa, to shi me zai saka ya bata bayan wannan sirrin Business ɗin su ne da ƴan uwan sa, don tana aiki a Hospital ɗin ai ba yana nufin tasan sirrin su bane, da me tafi sauran matan gidan ne?...
"Abban Baffa, I am talking and you are listening because you have made Me nothing." Maganar ta takatse masa tunanin sa
Still murmushin yayi yace, "kin fiye rigima ke kam Hajjaju, kin ga na nemi taimakon ki ne? Meyasaka baza ki ji da naki aikin ba? Ko da ma abinda ya shafi aikin asibiti ne ai ba ɓangaren mu ɗaya ba bare ki taya ni, ki je abun ki na gode".
A fusace Hajja Fatu take kallon sa, cikin takaici da halin mijin nata da har yanzu ya ƙi ya gane tace, "haka kace ko Alhaji? Well shikenan God help".
Da gama maganar; ta miƙe ta nufi ƙofa don ficewa, duk da har aranta ta nuna masa fushin ta ne don ta san halin sa zai iya dawowa da ita, daga nan ma ya faɗa mata abinda yake yi, ita kuma ta samu damar shiga jikin sa har tasan sirrin komi nasu
Amma kuma ga mamakin ta har ta buɗe ƙofan be ce mata komi ba, ɗan juyo wa tayi ta kalle sa sai taga aikin sa ma yaci gaba dayi tamkar ma be san da ita wajen ba, hakan ya ƙara tunzura ta; ta fice tana bugo ƙofan cike da tsantsan takaici
Murmushi Abba yayi yana bin ƙofan da kallo, kana ya girgiza kansa yana maida kansa yaci gaba da abinda ke gaban sa.
Fitowan Hajja Fatu itama Shakira ta fito a ɗakin ta, kallon Mahaifiyar nata tayi cike da nazarin ta kafin kuma tace, "Lafiya Hajja me ya faru ne?"
Huro hanci tayi tana ɗaga idanun ta ta sauke kan Shakiran dake tsaye tana jiran amsar nata tace, "It's me and your father. Let's talk about it tomorrow. I'm not feeling well. What are you doing here?" Ta sauya maganar da tambayan ta
Shakira tace, "I just came out to drink water, har na fara barci ishin ruwa ya tado ni".
Bata ce mata komi ba ta nufi ɗakin ta tabuɗe ta shige
Da kallo Shakira tabi ta dashi, har sai da ta shige kafin ta janye idanun ta tanufi bakin Fridge, buɗe wa tayi ta ciro goran ruwa tasha sosai, sannan ta mayar ta rufe ta koma ɗakin ta.
.
_plz I don't get a lot of comments, if you don't like it please tell me in Dena, don ba nan kaɗai nake yi ba, can da suka fi buƙata sai in riƙa musu su kaɗai, ta comments ɗin ku kawai zan san kuna so aci gaba._
_kar ku manta Vote and share._
[5/29, 8:48 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTOR'S*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL._
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* 🧝🏼
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
𝗝𝗜𝗞𝗔𝗥 𝗟𝗔𝗪𝗔𝗟𝗜 𝗖𝗘✍️
𝗪𝗮𝘁𝘁𝗽𝗮𝗱: 𝗨𝗺𝗺𝘂𝗗𝗮𝗵𝗶𝗿𝗮𝗵👈
𝗦𝗔𝗗𝗔𝗨𝗞𝗔𝗥𝗪𝗔
𝑁𝑎 𝑠𝑎𝑑𝑎𝑢𝑘𝑎𝑟 𝑔𝑎 𝐹𝑎𝑚𝑖𝑙𝑦 𝑛𝑎 𝑔𝑎𝑏𝑎 ɗ𝑎𝑦𝑎. 𝗚𝗢𝗠𝗔'𝗦 𝗙𝗔𝗠𝗜𝗟𝗬.
*EPISODE Twenty*
Da sannu rayuwa taci gaba da gudana, zuwa wannan lokacin Familyn Dr. Al'ameen suna ta shirye-shiryen zuwa Kano ne Bikin Salma (Ƴar Hajiya Laila), yanzu haka saura wata ɗaya
Kaka da kansa ya ba da odan kaya ya raba musu, wai wanda zasu ci biki dashi, matan kaɗai, daga iyaye har ƴan matan, har da su Aunty Zainab da Aunty Zulaiha sai da ya saka aka aika musu dashi, kala bibbiyu ne atamfa da Swiss less, kuɗin su kuwa zai kai dubu ɗari ko wanne, daga gani kasan kayan masu uban tsada ne, sun yi murna matuƙa, nan da nan kowa yakai ɗinki inda zai iya kai wa
Kafin ranan bikin kuwa tuni an amso musu, ranan Alhamis ƴan matan suka shirya tafiya, matan gidan kuma sai gobe juma'a za su taho, su kuma su Big Dady ranan ɗaurin auren asabar za su je, gaba ɗaya har dasu Usman, sannan kuma su dawo a ranan.
Tun 11:00am. Suka gama shirin su, ko wacce da jakan ta a hannu, har haraban gidan iyayen su mata suka rako su
Drever ya amsa jakunan nasu ya saka a bayan mota
Yusra ce ta shiga gaba, su kuma su uku a baya, drever'n yaja motan suka ɗau hanya cike da ɗoki
To dama ba wai sun saba zuwa sosai bane, kasancewar Boarding school suka yi a A.B.U Zaria, shiyasa ba su da lokacin kansu bare su riƙa ziyarce-ziyarcen ƴan uwa, kuma suna gamawa suka soma aiki, wannan dalilin ne yasa sun daɗe rabon da su je Kano, gwara-gwara ma Katsina, hutun ƙarshe da suka samu kafin su gama school a can suka yi, sai kuma suka ƙarisa sauran a Maiduguri, Kano ne dai sun shafe kusan shekaru biyar rabon da su je.
Zuwa ƙarfe 02:00pm. Tayi musu a Kano, Direct family house ɗin *General Isah Basheer Isah (Walid)* suka nufa, wanda a yanzu ake kiran sa da Granny
Gate aka wangale musu drever yaja motan zuwa ciki, be tsaya ba sai a ɓangaren su Salma, kasancewar gidan babba ne me Part-part, da ƴaƴan sa guda hudu maza da jikokin sa waɗanda suka yi aure su wajen uku duk a cikin gidan suke da zama, kuma kowa da na shi Part ɗin, sai na Granny ɗin da matar sa da suke ce mata INNA Haja.
Tun kafin ma su fito daga motan su Salma suka fito tarban su, dayake sun san da zuwan su, ƴan mata ne kusan su goma kuma duk jikokin Granny ne, a ciki har da ƴaƴan yaran sa mata da sukai aure a wani wajen
Sai kuma Shamsiyya da itama tazo tun jiya
Nan da nan suka karaɗe ɓangaren da murna da ihun ganin juna, daga baya kuma suka ɗunguma zuwa ciki
Hajiya Laila na zaune a parlour'n ta tana jiran isowar su, ganin su yasa ta washe bakin ta kafin ta fara musu maraba
Gaba ɗaya wajen ta suka isa suna gaishe ta cike da tsananin farin ciki a fuskokin su
Bayan sun gama gaishe-gaishen ne ta tashi taba su waje, nan kuwa suka ƙara ɓarke wa da Surutu ana hiran yaushe gamo, Sarkin surutu Firdausi tuni ta soma zuba ko haɗiye miyau ba tayi, tana ɗire aya take ɗaukan wani
Yau har da Fadila ba'a bar ta a baya ba, domin tayi zaman ta cikin ƴan uwa ana ta hiran da ita
Sai daga baya ne ma da Hajiya Lailan ta fito, take musu tsiya "ko abinci basu ci ba sun zauna suna ta zuba zance"
Salma ita da su Shamsiyya suka tashi suka haɗo musu abincin, duk sun baje a parlour'n suna ci suna ci gaba da hiran su cike da nishaɗi.
Ƴaƴan Hajiya Lailan ne guda biyu maza, Bashir (Abba) da kuma Yaseer suka shigo cikin parlour'n, yanzu haka ko wannen su da iyalan sa, shi Abban ne babban jikan gidan
Gaishe su suka yi cikin girmamawa, su ma suka amsa cike da fara'a da nuna farin cikin su na ganin su, har da tambayan su Baffa da Usman tare da sauran ƴan gida, duk suka amsa musu da "lafiya lau sun ce a gaishe su," daga nan suka wuce ɗakin Mahaifiyar su suka bar su nan suna ci gaba da hiran su
Ɗahira ce ta kalli Fardausi da ta cika su da Surutu, don ita ce ma ƙarfin hiran, cikin tsokana take ce mata, "Ni wlh da an haɗa ku gaba ɗaya Dady ya aurar daku, ko gidan ma sun huta da surutun ki, yarinya ko haɗiye yawu ba ta yi".
Dariya gaba ɗaya aka kwashe dashi
Ita kuma Firdausin gyara zaman ta tayi har da karkace ɗankwalin kanta tana faɗin, "me kuke ci na baka na zuba? Ai wlh marriage is time and I'm here to do, amma wlh bazan yarda a haɗa Ni da Salma ba, dole sai na zauna nima na taɓa ƴan matanci na Ni kaɗai, haka kawai ai bazai yiwu ba".
Hararan ta Salma tayi tace, "dalla yi mana shiru, Ni wlh ban san ma meyasa Dady ya ƙi tilasta miki fiddo da mijin ba, uwar ma me zaki sauna yi musu bayan ba kya cas ba kya as".
Itama dai Firdausin hararan nata tayi tace, "eh naji dai, baza ai mana auren tare ba ƴar baƙin ciki, wlh nima yanda kika fara aiki kafin kiyi aure, nima bazan yi ba sai na soma aiki na".
Tsaki kawai Salma taja tana sake kwaɗa mata harara
Firdausin ramawa ta kuma yi, har da murguɗa baki
Dama sun saba kasancewar saƙo da saƙo suke, bare kuma dama Salma tana jin haushi an ce ta fito da miji a haɗa da na sauran yayyin su biyu maza da za ayi musu aure, ita kuma Firdausi da sauran ƴan matan ba'a ce musu ba, hakan yasa take jin haushi tunda ba'a haɗa su gaba ɗaya ba
Su dai sauran sai dariya suke musu, basu tashi ba sai da aka kira sallan la'asar, sai ma lokacin