Chapter 6 Reading Nafisat Return Book Complete By Ummu Dahirah.txt Arewa Novels

Nafisat Return Book Complete By Ummu Dahirah.txt

Author :  Ummu Dahira Category :  New Hausa Novels 2026

Chapter   6 / 20

15K to 18K   out of 58K words

wani kalma ta soma shiga tsakanin ku? And kuma lokacin ne ka soma sonta?" ta sake tambayan sa cike da zumuɗi da son jin labarin


Murmushi Kaka yayi yana lumshe idanun sa, sai ya buɗe a kanta yace, "kalman da ta soma fitowa a baki na shine haƙuri na bata, sannan ne ta ɗago ta kalle ni, tabbas kallon farko da nayi mata na kamu da matsananciyar ƙaunar ta, kuma sai na nemi alfarman tabi ni inyi mata dressing hannun, da farko bata da ninyan bi na but mutanen da suka taru wajen ne suka saka ta taje, kalman da na soma ji a bakin ta har ta tafi sunan ta kaɗai ta faɗa min".


"Kaka kasan me?"


Girgiza mata kai yayi yana kallon ta


Murmushi tayi da ya bayyana ƙananun haƙoran ta tace, "abinda yake bani mamaki da burgewa yanda ka auri Mata har uku masu suna ɗaya, ko a Film da littafai ban taɓa ganin hakan ba, kuma har kayi rayuwa dasu alokaci ɗaya".


Shima murmushin yayi yace, "Allah kenan shi ya ƙaddara hakan, gashi ke kuma kin zo a ta huɗu".


She laughed and said, "Show me the other pictures, ka ga har yanzu bansan sauran matan naka ba ko a hoto ka ƙi ka nuna mana, wancan ƴar uwan taka da tayi aure a ƙauye kawai nasan zan iya tunawa, tunda nasan ta muna yara kafin ta rasu".


Jakan ya buɗe ya kuma zaro wani hoton ya miƙa mata


Hoton ta'amsa tana kallon matashiyar da aƙalla zata kai shekara 19 zuwa 20, fara ce sol kyakykyawar bafulatana, da sauri Ɗahira ta ɗago kai tana kallon Kaka tace, "Laa Kaka wlh wannan sak Big Dady, ba su da maraba kamar tayi kaki ta ajiye".


Murmushi yayi yace, "Matata ta farko kenan *UMMEE NAFEESA,* Mace ƴar aljanna me tsananin haƙuri, dattako da sanin ya kamata, bazan iya fasalta miki kyawawan halayyan ta ba, wannan hoton anyi sa ne gab da zata rasu, Ni na ɗauke ta a waya shine na ba da aka wanko min, Allah Sarki ta rasu da ƙuruciyarta, ta rasu lokacin da nake matuƙar buƙatar ta, ta rasu sanda ta gama naƙudan Noor (Big Dady) batare da ta ganshi ba ta koma ga Allah. Allah ya jiƙan ki da rahma Ummeeta". Kaka ya ƙarike maganar tasa yana share hawaye


Itama Ɗahira har sai da tayi nata hawayen sabida tausayi sannan tace, "ameen Kaka, may Allah have mercy on them all".


Amsan hoton yayi ya maida a jaka, yana shirin rufewa Ɗahira ta saka hannu ta zaro wasu hotunan biyu tana cewa, "Kaka ka bari mana ka gama min bayani, wannan kuma yaron me tsananin kama da kai wanene?"


Ta nuna masa hoton ɗan ƙaramin yaro dake wasa da kayan wasan da aka zube masa da yawa a gaban sa


"Yarona na farko kenan sunan sa Arif, Sunan Kakana yaci Khabeer, amma tun yana ƙarami ya rasu".


Ɗahira tace, "laa Kaka ashe ban da Big Dady dama kayi wani yaron? Wacece maman shi?"


Hoton hannun ta ya nuna mata


"Ga Maman shi nan cikin hoton nan".


Shafa hoton Ɗahira tayi da hannun ta tana murmushi, hoton KAKA ne da Ƙannin sa biyu Baseera da Ihsan sai kuma Nafeesa mahaifiyar Arif".


"Kaka kuna tsananin kama sosai duk kan ku kowa ya gan ku ya san ƴan uwan juna ne".


Murmushi kaɗai yayi ya miƙa hannu ya'amsa hoton sannan yace, "kawo in mayar zanyi sallah".


"So what about the story Kaka?"


"Ki bari duk sanda na sami lokaci zan tara ku gaba ɗaya in baku cikakken labarin aurena dasu".


"Yauwa Kakus ɗin mu, Allah yakai mu to".


Bayan ya zuba hotunan ya bata jakan ta mayar, ita ta tura sa har Toilet ta zuba masa ruwa yayi alwala sannan ta tafi part ɗin su bayan ta bar sa nan cikin ɗaki yana Sallah.


Tana zuwa Parlour'n su da Fadil taci karo yayi ɗai-ɗai yana kallo


"Yauwa Aunty Ɗahira kin bar wayan ki ana ta kira".


Bata ce komi ba ta wuce cikin ɗakin nasu, ƙarar zuban ruwa tajiyo a Toilet ta san Fadila ce, zama tayi ta ɗau wayan tana duba missed calls ɗin da akayi mata, Baffa ne ya kira ta, itama kiran sa tayi but be ɗauka ba, sai ta'ajiye wayan ta ɗau Novel ɗin da take karantawa *JARUMAI* ta gyara zamanta ta soma karanta wa kafin Fadila ta fito daga Toilet tayi alwala.
[5/23, 4:03 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
             *FAMILY DOCTORS*
                         🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
  *NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
                 _NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻‍


*بسم الله الرحمن الرحيم*


*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞

```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A✍️*


*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈
        

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_



        *EPISODE Ten*



       *WASHE GARI*

       BAFFA ne jingine jikin motar sa yana duba waya, yana sanye cikin ƙananan kaya kamar yanda ya saba waɗanda suka matse sa sosai, kansa da askin zamani da yayi masa kyau sosai, sai faman shaining yake yi alamun ya sha mayuka masu tsada


Shakira CE tafito cikin shirin ta, tana tafiya ɗai-ɗai kamar baza ta taka ƙasa ba, har ta wuce ta hangi Yayan nata tsaye wajen motan sa, sai ta juyo tana kallon sa taɗan ɗaga murya tace, "Yaya inzo mu tafi tare ne?"


Lokacin ne Baffa ya ɗago kansa yana kallon ta, sai da ta samu harara kafin yace, "Where is your car and I will take you?"


"Here's Yaya, wlh I don't feel good about my body that's why I don't like driving".


Gajeren tsaki ya ja yana ɗauke kai a kanta yace, "babu inda zan kai ki ki nemi drever".


Har ta buɗe baki da ninyan yin masa magiya sai taga yana kallon hanyan ƙofar shiga gidan yana sakin murmushi, itama juya kai tayi ta kalli wajen


Ɗahira ce ta fito sanye da Jan abaya me kwalliyan Flower's da stones a jiki, tayi Rolling da ɗankwalin Rigan, face ɗin ta sanye da ɗan siririn farin glasses 👓ɗin ta wanda ya ƙara wa Sky Green ɗin cikin idanuwan ta kyawu, tunda ta fito itama take murmushi tana taho wa cikin tafiyar ta na yanga tamkar zata karye


Tana isowa suka sakarwa juna murmushi me bayyana haƙora, sannan ya buɗe mata motan ta shiga, shima zagaya wa yayi ya shige yaja ya nufi Gate


Shakira dake tsaye kamar an dasa ta ta saki baki tana kallon motar har ta fice


"Cab ɗijam.. Kar dai ace hasashe na ya zama gaske? Uhmm idan ko haka ne tabbas akwai matsala, babu yanda za ayi na bar Yayana yaso wannan me kama da mujiyan.. ina sam".


Ƙwafa tayi tana nufan motan ta ta shige taja ta fice a gidan, ko a cikin motan tunanin yanda ta gansu yau ɗin ya tsaya mata arai, duk da ta san cewa babu wanda ya kai Ɗahira da Baffa shaƙuwa a gidan, amma kuma abinda take gani cikin idanun yayan ta yasa yau ta ɗaura zargi akan su.



             Har tazo ta wuce motan su Baffa a hanya tana kallon motan ta mirror tana jan tsaki, tana kitstsima abubuwa aranta da yawa.



          Su kuwa a cikin motan hira Baffa yake ta mata cike da tsananin ƙaunar ta, ji yake yi ba ya son ko kaɗan tafiyan da suke yi ya ƙare sabida shauƙin da yake ji, shiyasaka yake tafiya a hankali kamar bazai yi ba


Ɗahira kallon sa tayi tana dariyan labarin da yake bata tace, "Yaya don Allah ka bari haka kar cikina ya fashe".


Dariya shima yayi yana kallon ta cike da so yace, "ai Ni nafi son in gan ki kina Farin ciki ne shiyasa nake baki labarin, don haka Ni bazan Dena ba, bari ma in baki wani".


Murmushi tayi me ƙayatarwa cikin ɗauke kai akan sa tace, "to Yaya kabar ni haka dai zuwa anjima sai ka bani".


"Well, my dear Sister, it's over no matter what you want me to do."


Still Murmushi tayi idanun ta akan titi, sau da dama tana mamakin yanda Baffa yake nuna mata kulawa fiye da tunanin ta, kuma yake yin duk abinda take so yake barin duk abinda ba ta so, tasan cewa yayan nata me ƙaunar ta ne tun tana ƙarama don ba ya son ɓacin ranta.



       Yana yin parcking a haraban asibitin ya fito ya zo ya buɗe mata yana nuna mata hanya da hannu, cike da murmushi a face ɗin sa yace, "Yauwa Gimbiya fito an kawo".


Sunan da ya kira ta dashi ya saka tayi dariya tana kallon sa cike da farin ciki, zuro ƙafafun ta waje tayi ta fito, sannan ya rufe suka jera sukayi ciki.







               ⚫⚫⚫


"I told you to come in at 08:00am o'clock. Me ya tsayar da ke?" Doc. Said yayi maganar yana juyawa cikin kujeran sa


Fari tayi da idanun ta sannan tace, "kai ma ban da abun ka ya Docta; kasan ba a raba mu da ɗan shafe-shafe na kwalliya, kuma ka ga 08:00am yayi wuri da yawa".


Murmushi ya saki yana sakar mata wani shu'umin kallo


"Uhmm Sulaima kenan! That's why I love you more sabida wannan kwalliyan naki, ko kaɗan baki wasa da jikin ki wajen kin ga kin fito kin burge kowa, wasu kuwa ko a jikin su be dame su ba". Yaƙarishe maganar da taɓe bakin sa


Dariya tayi tana sake lanƙwashe murya tace, "Ya Dacta kenan! Ni fa nasan da wacce kake yi, kuma kasan zan iya zuwa in faɗa mata".


Waro ido yayi yana dariya yace, "rufa min asiri don Allah karki haɗa ni da ita kin san halin ta, but yaushe Ni zaki bani dama ne wai? Na gaji da wannan kwane-kwanen da kike min".


Sulaima tace, "Ya Dacta Ni fa gaskiya ba na tunanin zan iya harka da kai, ko ka manta kai Mijin Yayata ce? Haba dai ka sauya tunani mana Ni gaskiya bazan iya ba". Taƙarike maganar a shagwaɓe


Lumshe idanu yayi yana sake kallon ta cike da tsananin sha'awar ta, sai da ya ɗago daga jikin kujeran ya ɗaura hannayen sa kan Deks ɗin sa sannan yace, "Sulaima kin san ni; na sanki, why kike son haramta min kan ki? karki manta fa ba wai na ce miki auren ki zan yi ba bare ki kawo wani zancen Ƴar uwan ki, Ni dai don Allah ki bani dama mu more rayuwan mu tare kin san bazan iya haƙura dake ba, kinga matsayin ki daban matsayin ƴar uwanki daban a waje na".


Murmushi tayi tana girgiza kanta cike da yauƙi tace, "ya Dacta let's change our talk, muyi abinda ya kawo ni ka ga ina da inda zan je".


Doc. Said yace, "to shikenan tunda kin fi son haka, amma ki sani ba wai na bar maganar bane kenan, yanzu ya aka yi kika bar ciki ya shiga jikin ki?"


"Hmm tsautsayi mana, wlh nayi mamaki da naje Hospital aka gwada Ni wai ciki ne dani, kuma duk wani matakan tsaron da na saba yi nayi but abun kamar almara".


Ɗage kafaɗa yayi yace, "any way muje ki hau gadon in duba ki mu gani, don Nima Ina da aiki yanzu a gaba na".


Tashi tayi tana cire gyalen jikin ta ta nufi wajen gadon, shima ya tashi ya bi bayan ta.







             ⚫⚫⚫


    Zuwan ta Office ta tarar da patients ɗin ta suna jiran ta, yau bata zo akan lokaci ba hakan yasaka har suka rigata zuwa tunda ƙarfe 10:00am zata soma duba su, yanzu gashi har goma saura


Tana shiga ta saka rigan aikin ta sannan ta zauna taba su umarnin shigowa ɗaya bayan ɗaya tana duba su, tayi wajen awanni biyu tana faman duba su sannan ta gama ta tashi ta shiga Toilet tayi uzurin ta ta fito, wasu files ta ɗauka ta fita ta nufi rooms ɗin patients ɗin ta masu jinya


Tana shiga da gadon farko ta fara, taƙarisa da fara'an ta tana gaishe da matar dake jinyar wata burduwan yarinya, bayan sun gaisa cikin faram-faram sannan Ɗahira tace, "Mama har yanzu bata farka bane?"


Mama tace, "ta farka jiya da daddare, kuma Dacta ɗin da kika ce zata zo ta duba ta ita ta duba ta, ga ma takardan da tace, "in baki". Ta miƙo mata takardan


Ita kuma ta'amsa tana dubawa, sai da ta gama dubawa sannan ta kalli Maman tace, "Mama to ya jikin nata tana samun sauƙi ko?"


"Ai alhmadulillah Dacta ba kamar jiya da safe ba, ta samu sauƙi sosai".


Gyaɗa kai Ɗahira tayi tana rubutu cikin wani file, sai da ta gama ta matso kusa da yarinyan ta soma duba ta sannan ta ɗago tana kallon Maman tace, "Mama insha Allahu komi zai zo da sauƙi, idan ta farka sai ta soma amfani da ruwa me ɗumi ana mata tsarki, daga yau sai a soma mata amfani dashi ko yaushe insha Allahu komi zai zama normal".


"To Dacta mun gode ƙwarai Allah ya saka da alheri".


Murmushi Ɗahira tayi tace, "ameen Mama Babu komi ai, Allah Ubangiji ya bata lafiya".


Mama ta'amsa da "ameen" tana sake mata godiya


Daga nan Ɗahira gadon gaba ta wuce, itama Yarinya ce budurwa, wata shirgegiyar mata take jinyar ta, sai dai yarinyan bata kai wancan shekaru ba don baza ta fi 13yrs ba


Bayan sun gaisa da matar ta tambaye ta jikin yarinyan


Matar cike da sanyin murya kamar za tayi kuka tace, "Doctor babu sauƙi wlh yarinyan nan tana shan wahala sosai, tun jiya farkawar ta biyu, kuma duk idan ta farka a firgice take tashi tai ta ihu tana surutai".


Ɗahira da take bin yarinyan da kallo cike da tsananin tausayin ta ta juyo tana kallon Matar tace, "Mama ki kwantar da hankalin ki insha Allahu zan yi iya bakin ƙoƙari na wajen na ga ta samu lafiya, Allah zai saka mata duk wanda yayi mata wannan abun".


Share hawayen ta matar tayi tace, "ameen Dactor na gode ƙwarai".


Daga nan Ɗahira duba yarinyan ta soma yi, ta jima tana duba ta kafin ta saka mata ruwa tayi mata allura ta cikin ruwan sannan tayi mata sallama ta wuce


Sauran gadon ta nufa ta duba su su ma, sannan taje wasu Rooms ɗin, sai da ta gama ta koma Office ɗin ta.



           Tana shiga taga Baffa zaune yana kallon ta yana sakar mata murmushi


Itama murmushin tayi masa ta shigo ta nufi wajen zaman ta ta zauna, cikin muryan ta na yanga take cewa, "Yaya na yaushe ka shigo?"


"I Come in right now, what's your job?"


"Alhmadulillah. How's yours?"


Murmushi yayi yana shafa suman kansa yace, "uhmm sai godiyar Allah my Sister amma babu daɗi".


Dariya Ɗahira tayi tana kallon sa tace, "kai kenan Yaya, kai da ka jima tsawon shekaru kana aiki kake faɗan haka ina ga Ni da jiya na soma? wlh Yaya da wahala sosai aikin nan duk na gaji". Taƙarike maganar ta tana lanƙwashewa ajikin kujeran


Baffa dariya yayi yace, "oh my dear sister ke dai kawai ki ce ke raguwa ce, amma daga fara aiki kice kin soma gajiya?".


Murmusawa kawai tayi tana ɗan lumshe idanuwan nata don tasan halin yayan nata tsokana yake ji, ita kuma ta gaji ko maganar ma  daƙyar take amsa masa


Baffa da ya tsare ta da idanun sa yana sakin murmushi me ƙara masa kyau yace, "sis Naga da alamun kin gaji tashi muje muci abinci".


Shiru tayi tana ɗan tunani


Hakan ya saka Baffa yace, "Do you have a job?"


Girgiza masa kanta tayi tana miƙewa ta zare rigan aikin tace, "No let's go".


Tashi yayi shima cike da jindaɗi suka fito suka jera har wajen lifter, shiga suka yi yakai su downstairs, mota suka shiga suka bar cikin asibitin, babu nisa da Resturant ɗin da suka je.














_More Comments more post_🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️
[5/23, 9:05 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
             *FAMILY DOCTORS*
                         🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
  *NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
                 _NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻‍


*بسم الله الرحمن الرحيم*


*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞

```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A✍️*


*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈
        

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_



        *EPISODE Eleven*


       Bayan sun shiga sun zauna ne Baffa ya tambaye ta abinda take so?


and she answered, "Everything she wants to eat".


And he ordered Jallof Rice da ferfesun Kayan ciki with some drinks


and they started eating.


Ɗahira ta kalle sa tana murmusawa tace, "How do you get used to coming to your GirlFriend's restaurant like this?"


Sosai Baffa yayi dariya yana kallon ta yace,  "Why did you say that?"


"Uhmm only".


Murmushi yayi a wannan karon yace, "ke dai ki faɗa abinda ke zuciyar ki".


Maƙe kafaɗa tayi cike da yauƙin muryan ta tace, "Yaya Ni dai nasan kana min rowan ta ne shiyasa ma baka taɓa nuna min ita ba ko da a hoto ne, but nasan dai kuna fita irin wajen shaƙatawan nan".


Baffa kallon ta kawai yake yi cike da burgewa, ji yake yi aran sa tamkar yace, "ke ce macen da na taɓa so a *RAYUWATA,* sai kuma ya girgiza kansa still yana murmushi yace, "My sister kenan, idan har zaki yarda wlh ban taɓa yin budurwa ba".


Ƙwalalo idanu tayi tace, "kai Yaya dagaske kake yi ko wasa? How can it be said that Handsome Guy and you have no girlfriend? Ko dai yaya kana ɓoye min ne ba ka son na sani?".


Cikin ido yake kallon ta cike da wani irin salo


Hakan yasaka ta ɗauke kanta tana ci gaba da cin abincin ta cike da yanga da ya zamar mata jiki, komi nata hakan take yin sa


Huro iskan bakin sa yayi be ɗauke ido a kanta ba yace, "Da gaske ƙanwata ban taɓa budurwa ba wlh, akwai wacce nake matuƙar ƙauna sai dai har yanzu na kasa sanar mata".


Ɗago kai tayi tana kallon sa da mamaki kafin tace, "why?"


"Saboda kwarjinin ta.."


Dariyan ta ya saka shi yin shiru yana sake ƙure ta da idanun sa, sosai take dariya shi kuma yana bin ta da kallo cike da tsananin ƙaunar ta da burge shi da take

6 / 20