Chapter 10 Reading AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf Arewa Novels

AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf

Author :  Ummu Afan Category :  Arewa Hausa Novels

Chapter   10 / 15

27K to 30K   out of 44.6K words

kubra umma kuma tanacan bangaren dattijai mata

Ahmad yace kaga ikon Allah malam shamsu kai ne anan kokuma wa

Ya shamsu yajuyo jin ankira sunanshi
aikuwa yaga su Ahmad da Hakeem
Hakeem ma jin an ambaci sunan malam shamsu

Yasa yadago mai suka yi murmushi gadayansu

Nan ya shamsu yabasu hanu suka gaisa

Yace wasuka zowa Ahmad yace daughter dinmu ai nan take karatu

Kaifa yace nikuma kanwata ce anan

Kubra tace ina wuninku Hakeem da Ahmad suka amsa

Ahmad yakalli inda madam dinshi Aisha take yatashi yaje yarada mata magana akunne aikuwa
Aisha ta task da sauri

Tana zuwa ta kama hanun kubra tace alhamdullilahi yau dai nima na hadu da kawata

Kubra ma dayame wayayyiyace tace nima naji dadin haduwata dake

Nan Aisha taja hanun kubra suka koma gurin su daban


Nan kuma ya shamsu da Hakeem da Ahmad suka can gaba wajen special guest

Nan akafara taron da addua

Can principal tafara jawabinta kamaryadda aka saba

Daga can kuma ta ce itada kanta zatakira best student of the year

Wanda duk shekara akeba principal dama tazaba da kanta ta kuma bata kyauta duk karshen
shekara haka akeyi


Wani daga cikin teachers dinsu ya tashi yakarbi Mike din hanun principal da list din hanunta


Yafara kiran suna kaman haka

Best student of the year
Kowa ya kasa kunne

ASMAU SULEIMAN SHAMSU

aikuwa duk student aka dauki tafi raf raf raf

Dan daga malamai har student sunsan Husnah ta cancanta sosai

Cikin nutsuwa Husnah ta tashi ta isa gurin principal
Nan principal tace wazata kira ya tayata karba
Husnah tace wa principal ya shamsu za akiramin

ya shamsu suna zaune duk hankalinsu yakoma kan head girl
Shi ya shamsu baifada musu wacece kanwar tashiba

Sai jisukayi ankira ya shamsu yatashi cike da alfahari da 'yar kanwarshi bata bashi kunya
kokadan


Ahmad da Hakeem suka hada ido
Ahmad kaddai itace kanwar tashi

Hakeem yayi murmushi yace ga zahiri amma fa yarinyar taburgeni matuka
Yayi maganar yana kallonsu Husnah

Cike da mamaki Ahmad yakalli abokin nashi

am I dreaming ?
Man what are you saying

Hakeem bai kalleshiba murmushi kawai yayi ya dauke idonshi daga gurin su Husnah ya mayar
da kanshi kan wayarshi


Murmushi Ahmad yayi dai dai lokacin ya shamsu yadawo yazauna

Ahmad yace kanwarkace ya shamsu yayi murmushi yace yar karamar kanwata kenan

Yace masha Allah
Allah ya albarkaci rayuwarta

Ya shamsu da Hakeem suka ce ameen

Daga nan kuma sai akafara ba wa prefect satificate dinsu ya rage sauran na social prefect da
Head girl

Aka kira social prefect AMINA HAKEEM ABUBAKAR

Nan akabata sertificate dinta da kuma gift dinta maman Laila ita tayata karba

Hakeem kallo daya yamusu yacigaba da abinda yakeyi

Can akakira me gayya mai aiki wato head girl

Husnah taje ta karba itada yaya shamsu principal Tamika kyautar aka musu hoto

Duk wani kyauta da akerabawa Husnah ita takarbi na farko abin yaburge kowa ana karshen

Husna ta tashi zata karba sai kawai tafashe da kuka Dan tasan koba komai yayanta zaiyi
alfahari da ita

Principal ta rungumeta tana share mata hawayen

Tace asmau Allah ya albarkaci rayuwarki

Ya shamsu yaji dadin adduar principal

Yace Ameen hajiya mungode Allah yabar zumunci

Nan fa students sukayi tazuwa suna daukar hoto da Husnah suna mata fatan alkairi

Masu bata gift nabata kai gaskiya Husnah tayi farin jini sosai har malamai suna tururruwar hoto
da ita


Meenat zaune abin duniya yadameta tana matukar jin bakin ciki abin da kefaruwa da Husnah

Laila tace wai ita wannan yarinyar fa saikace aljana komai ta handame ita kadai

Meenat tace kyaleta dama yunwa ne yakawota school din Dan dama 'yar matsiyata ce

Scholarship taci tashigo

Hajiya rukayya dole ai yanzu naji batu


Motar school ce ta kaiwa Husnah gift dinta har gidan




****

PROFESSOR HAKEEM yana zaune cikin falonshi kusan sati kenan da graduation dinsu
Husnah amma kullum da ita yake kwana da itayake tashi aranshi

Kuma tunda yake a rayuwarshi bai taba saka 'ya mace a rayuwarahi ba

Kuma a yadda ya fuskanci zuciyarshi takamau son 'yar baby nan

Shida kanshi yake wa kanshi dariya

Ya duba agogo yaga sai yanzu 8:30 nadare tayi
Yaje ya hada Kofi

Yanasha kadan yana tunanin Husnah

Abinda baisaniba shine Ahmad yadade a bakin kofa yana kallon abokin nashi daya fada shauki


Ahmad yayi gyaran murya hade da sallama

Hakeem yajiyo suka hada ido da Ahmad

Ahmad yace abokina wai meyake faruwa ne
Kwana biyu naganka kaman akwai wani Abu

Hakeem yayi murmushi tareda kurbar copee yace shine kabar matarka kazo gulma ko



Ahmad shima dariyar tare da dauko lemu maisanyi a fridge

Yadawo yazauna

Ahmad yace inkarashida gulma kaikaso

amma dai ni bazan bar nan ba sai kafada min


Hakeem yatashi yakoma bayan kujera yace
Ahmad am in love


Ahmad yayi dariya yace daman nasani


Duk wannan boye boyen naka duk kallonka nakeyi

amma gaskiya idan har kasamu yarinyar nan kayi sa a wallahi

Hakeem yace wace yarinya kenan tunda nidai ban fada wacce nakeso da bakinaba

Ahmad yayi dariya yace karka rainawa wa kanka hankali mana

Kawanwar shamsu koba hakabane

Hakeem yayi murmushi yace amma ya akayi kagane hakan dawuri

Ahmad yace shekaru talatin muna tare fa dan uwa taya za ayi barangane matsalarka ba


Hakeem yayi murmushi yace hakane amma bazan fada ba sai na musu

Jarabawa daya kaga daga tabbatar gidan danaje Neman iri

Next page
Your comments is needed fans❤❤❤❤❤


Anfara wasa fa fans❤❤❤❤

Sainaji ku
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN :


BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM


HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN


FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION

F.C.T.W.A



HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION



DEDICATE THIS PAGE TO sis JIDDER (BAEWAR ALLAH)
WANNAN PAGE IN NAKI
SABODA KAUNA DA KIKE NUNA WA WANNAN
NOVEL NAWA NA
AKWAI LOKACI
Allah yabar zumunci keep it up ❤❤



Masu comment ina sane da Ku kafin na kamla littafin nan duk sai kunji sunanku daya bayan
daya so kucigaba da bin ummu afan takuce ❤

AKWAI LOKACI





PAGE 66 to 70





PROF HAKEEM zaune kan resting chair dinsa a bakin sweeming fool yana shan iska dan
yanzu yafito daga cikin ruwan

Wayarshi ta daukara yana dubawa yaga dalibata wato mummynshi kenan dan sunan dayasa
mata kenan

Bayan sungaisa Hakeem yace mummyna albishirinki mummy hafsat tace goro

Yace naga matar aure a kano fa

Cikin tsananin farin ciki mummy hafsat tace alhamdulilla naji dadin wannan albishir

Yaushe zakazo katura mahaifinka gidansu yarinyar


Hakeem yayi murmushi yace daliba kenan ai ban ma taba fada wa yarinyar ba nikadai nake
kida kuma nake rawa na

Mummy tace shirme ni harkasani ina murna to idan bazaka iya fada mata nika nuna min
gidansu yarin sai naje

Ayau saina zo kano wallahi akanka my son

Hakeem yayi murmushi yace nasani mummy na

Nasan zakifi kowa farinciki shiyasa nafada miki tunkafin na fada wa yarinyar

Sai mummy Kinsan masu soyayyar Allah kadan suke aduniyar nan

Kuma dadin da dawa ma yarinyar danagani din ba masu karfi bane

Kinga idan naje kaitsaye Kuma akayi rashin sa a saikiga sun soni don kudina badan Allah


Mummy taja numfashi tace hakane son sai dai zuciyata tana bani bazataba son abinda baidace
dakaiba


Hakeem yayi murmushi yace Kinsan menakesonyi mummy tace a a son sai kafada

Yace zan jarabasu nagani zanje amatsayin talaka banida komai

Ingani zasu karbeni kokuwa


Mummy tace hakan ma tayi son dina
Kuma ina maka fatan alkairi

Insha Allah zasuci duk wani jarabawar da zakayi musu

Wasunan surukartawa Hakeem yayi murmushi mummy ta sosa mishi inda yake mai kaikayi

Yace ai harma tazama surukarki
Mummy tace aiba surukaba ma 'yata zama son

Hakeem yayi murmushi yace asmau amma anakiranta da HUSNA


kai masha Allah ashema babban suna ne da ita

Insha Allah asmau zata Mata agareka tun kafin naganta naji inasonta


Hakeem yace shiyasa nakeson Ku iyayena kuna matukar daraja abinda nakeso

Allah yabani matar da zata bauta muku da zuciya daya badan kudinku ba ko kudin danku


Mummy hafsat tace aikasamu son zantayaka da addua

****

Washagari Hakeem Bayan sungama komai ya shamsu yazo musu sallama zai wuce gida dan
karfe hudu yake tashi a lectures


Ahmad yace wa ya shamsu yaufa kafanmu kafarka zamuje mugaida Abba da umma

Dan idan muka biye maka bazaka gayyace zuwa samun ladan nan ba


Ya shamsu yayi dariya yace shikenan idan kun shirya muna iya tafiya

Hakeem yace na dauka zaka kawo wani excuse ne ince ai ba umma kai kadaibane muma
namune


Ahmad da ya shamsu sukayi dariya

a motar Hakeem akatafi ya shamsu agaba Ahmad yabaya

Ya shamsu yana nuna wa PROF HAKEEM hanya




******

HUSNAH ce zaune tsakar gida tagama aikin gidan kenan tas ko ina yadau kamshi

Ita kuma anty kubra tana kitchen tana hada abincin dare Wanda sudama kafin biyar sungama
komai sun zuba a kula

Kuma aikin sukayi Husnah da kubra yau idan kece da aikin gida to dayar kuma saitayi abinci

Yau Husnah ce da aikin gida

Tagama komai da wuri tana wa anty kubra dariya tana kitchen dan yau ya shamsu yace ayi
tuwon semovita miyar kubewa danya
Har kudin danyar kifi yabayar

Anty kubra tace zanrama ai Allah yasa ran girkinki Abba yace sakwara yakeso

Husnah tayi murmushi tace kai ai danagane kuskurena kuwa


Umma datake jinsu tace tun tuni kinjuye ruwa Yakama kishiga kiyi kisamu kifito kije min aika ko


Husnah tace to umma
Umma ta kalli kubra tace sannu kinji kubra Allah dai yamaku albarka yabaku masu yimuku
kuma

Kubra acikin zuciyarta ta amsa da amin dan tana jin kunyar umma idan tace Allah yabasu
masuyi musu



Husnah tafito daga wanka tayi dakinsu tashafa mai tadauko powder tashafa sai kwalli sai tasa
lips glow alebenta


Tabude akwatin kayan ta tafara zaban wadda zata saka

aikuwa idon ta yakai kan wani material pink da kuma ratsin baki ajiki Wanda ya shamsu yamata
a bikin shi

Tunda tasa a biki batasake sawaba

Sai tadauko shi tasaka dinki duguwa Riga ce
Daga sama ya dameta sosai dan Husnah fa akwai kayan aiki

Shiyasa umma bata cika barinta fita da gyaleba saidai hijabi dan Allah yamata kira

Husnah takalli kanta a madubi itakanta tasan tayi kyau sosai

Sai kuma tasan dakyar umma zata bari tasaka gyalen material din

Itakuma yau mayafi takeson yafawa

tace barin gwada dai tagyara gashinta tadaure da ribbon fari
Kafin tayafa gyalenta dan bata saka dankwaliba
Kota saka dankwalima abanza

Dan bayazama akanta sabonda tsantsin gashinta


Tadauko turarenta tafesa kafin tadauki Jakarta na suwaga pink da takalminshi duk pink tasaka
Kai masha Allah da wannan kyakkyawar hallita


Tafito tace umma nafito
Umma ta kalli 'yartata tace au da wannan gyalen zakifita

Husnah tace Allah sarki umma na gyalen kayan nefa

Kuma kinga kayan ai yana da fadi sosai
Kafin umma tayi magana anty kubra taleko tace umma dan Allah kibarta wallahi tayi kyau kuma
kinga ai kayan yana da fadi

Umma ta ce wato bakinku daya ko to shikenan kije Allah yakiyaye hanya

Husnah tace to umma baki min bayaninba umma tace kinci gidanku yau kika saba karbomin
zuman ne

Husnah tayi murmushi dimple dinta tsuka lotsa sosai
Tace to ummana afuwan nadauka bakaman na kullum bane


Tayi waje sukace mata adawo Lafiya




adai dai kofar gidansu ya shamsu yanuna wa Hakeem yayi parking

Suka fito atare Ahmad yace kashiga saikamana iso

Ya shamsu yace to shikenan yaya cikin gidan alokacin umma ce kadai a tsakar gida kubra ta
fito mata da taburma
Dan anna suke hirar Daren su gadaya

Ya shamsu yayi sallama umma tace a a ubana har andawo yace a umma yagidan nan dai
yagaida umma kafin yace umma daman su ogana na office ne sukazo gaisheku

Umma ta ce shine kabarsu a waje kuma sushigo ciki dan Allah haba waje

Ya shamsu yaje ya musu iso zuwa cikin gidan

Umma ta ce kashiga dasu daki Ahmad yace a umma mu kusa da ummanmu zamu zauna basai
munshiga dakiba

Umma taji dadin har ranta tace to shikenan 'ya'yan ummu kuzauna nan suka kwashi gaisuwa
agurin umma ta amsa cike da farin ciki
Nan kuma ta musu godiyar hidimar dasukeyi da su

Hakeem yace haba umma ai mu da shamsu Yanzu munzama 'yankuma bagodiya tsakaninmu
ai yiwa Kaine

Umma ta ce hakane kam Allah yake mutum da mutum
Kodai Allah yasaka muku da aljanna

Umma ta ce wa shamsu ubana aisai kayi maza kaje nan shagon mati ka karbo musu lemu mai
sanyi da ruwa

Hakeem yace haba dai umma mufa ba bakibane

Komai ummanmu tabamu cizamuyi
Ba umma ba harta ya shamsu yaji dadin wannan kara da Hakeem da Ahmed suke musu

Sallmar HUSNAH ce yasa Hakeem daga ido yakalli hanyar waje aikuwa suka hada ido cikin ido
Husnah tayi saurin dauke idonta dan dama akasi aka samu ta kalleshi

HAKEEM yasamu Kansa cikin wani yanayi Wanda yakasa fassarashi ba Ashe ganin da yayi
mata a school ma tafi haka


Husnah ta durkusa har kasa tagaishe da su Hakeem Ahmad ne karfin amsawa shikam ogan ba
baki
Yakasa komai ne

Ba Wanda ya kula da canzawarshi sai Ahmad

Ahmad murmushi yayi shikadai

Kubra tafito tagaishesu

Ahmad yace ai kawarki basan zamuzo ba dakinganta

Kubra tace dan allah yakawo mata Aisha Dan zaman da sukayi a gurin graduate dinsu Husnah

sun saba sosai


Ahmad yace ya mata alkawari ran sabar zai kawo Aisha tamata wuni daga nan tagaida umma

Umma ta ce Allah yakawo ta Lafiya umma na maraba da ita

Husnah da kubra suka kawo musu abinci a kula da biyu suka ajiye
Husnah tadauko plate guda biyu da serving spoon duk ta ajiye musu

Sai ta dauki jug ta kawo musu ruwa maisanyi na randar umma ta kawo musu da cups biyu


Umma ta ce maza hada musu zobo Husnah
Husnah tace to umma ai na dafa tunda dazu hadawa kawai zanyi saidai ba kankara


Ya shamsu yace hada barin karbo kankara

Ya shamsu yafita jimawa kadan sai ga shida kankara yakawo yaba wa husnah

Hadaddan zobo ta hada Wanda yasha kayam kamshi da cocumba

Tasa musu a jug shima takai musu kafin ta wuce dakin anty kubra umma tace bara nashiga kuci
abincin Ku

Ya shamsu yace bissimillarku kuci abinci

Hakeem yayi murmushi yace aiko baka fada ba

Ahmad yayi murmushi dan yasan dalilinsa na fadar hakan

Hakeem yayi serving kanshi

Tuwo daya yasaka sai sai yasa miyar baiga ruwan wanke hanuba sai

Yace yaya shamsu ruwan wanke hanu dan bana cin tuwo da cokali

Ya shamsu yayi dariya yace amma yallabai kaso barkwanci ninekuma yayan
Hakeem yayi murmushi baice komai ba

Ya shamsu yakira Husnah takawo ruwan wanke hanun

Takawo ta ajiye gaban ya shamsu shikuma ya mikawa Hakeem gabansa


Hakeem sosai yaci tuwon dai Bayan ya cinye Leda daya sai ya kara Ahmad nema yarage
kadan

Ya shamsu yace haba yallabai dan Allah kacinye wallahi umma zataji dadi

Hakeem yace rabudashi ya shamsu tsoron madam Aisha yakeyi kartatsareshi sai ya cinye
abinta yakasa Bayan yacinye na gidan umma

Duk suka kwashe da dariya
Hakeem yatsiyayi zobon da Husnah ta hada

10 / 15