Chapter 11 Reading AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf Arewa Novels

AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf

Author :  Ummu Afan Category :  Arewa Hausa Novels

Chapter   11 / 15

30K to 33K   out of 44.6K words

musu yasha

Aikuwa yaji kunnenshi kaman zai yanke dan dadi
Kodan ya hadu da soyayyane oho


Kafin yayi magana Abba yashigo dattijon arziki

Duk suka mike tsaye sai da Abba yazauna suka zauna suka kwashi gaisuwa

Ya shamsu yagabatar dasu

Abba yace a manya baki ne damu agidan Ashe
Nan shima yashiga musu godiyar hidimansu akansu



Sun dan taba hira kafin Abba yashiga daki yabarsu nan da ya shamsu


Hakeem yace Gaskiya ya shamsu wannan zobon asamin awani Abu natafi dashi zansha zuwa
dare


Ahmad yace narigaka azuci karigani a baki dan kasan duk inda nasha abinda yamin dadi sai
narage wa madam

Hakeem yayi murmushi yace kai man kafadi gaskiya

Ya shamsu dai dariya yakira Husnah yace tasamo jugs guda biyu ta zubo zobo tace to

Hakeem tabita da kallo komai na yarinyar yamishi Dari bisa Dari
Tana da duk wasu qualities din dayake bukata ga mace


Husnah ta zuba takawo ta ajiye
Ta yigaba abinta

Sai da akakira magrib suka yi sallama da su umma da Abba da anty kubra

Husnah tana kan sallaya idan tayi magrib bata ta shi sai tayi isha


Hakeem yaso yasake ganin Husnah

Amma taki fitowa

Ahmad ya ajiye bandir din kudi 'yan dubu dubu yace a ba wa kanwarsu tasai kayan kwalliya

Ya shamsu yace dan Allah karmuyi haka kudauki kudinku

Ahmad yace ai nariga na ajiye kuma ma aibakai muka ba ba kanwarmu muka ma kyauta


Da kyar ya shamsu yabar kudin nan

Suna cikin mota Hakeem ya karya kwana zuwa baibi hanyar gida ba

Ahmad yace man yana zaka kaimu kuma Hakeem yayi murmushi yace sa ido kawai kayi kallo
man

Ahmad yace OK baringa ikon Allah to

Hakeem yayi parking adai dai gurin wani malamin almajirai suka sauka

Malam na ganin HAKEEM yataso yazo sannu da Zuwa professor Hakeem yayi murmushi suka
gaisa da malam Garba

Malam Garba yace mukarasa daga taburma nan suka karasa

Hakeem yace malam bawani Abu yakawoni ba illa Neman wata alfarma

Malam Garba yace alfarma kuma alhaji da kanka
Hakeem yace a malam

Aure nake nema malam

Amma kasan rayuwa ta baci yanzu sai aureka badan anasonkaba sai dai don abinda kakedashi


Malam yace hakane

Hakeem yaja dogon numfashi
Ya kalli Ahmed da ya kagu yaji dalilin abokin nashi nazuwa nan


Hakeem yace malam zanje Neman aure da sunan talaka talakan ma futuk Mara iyaye

Koda anzo Neman tarihina guringa za azo dan
Kai zanfada a matsayin malamin danayi karatu agurin shi

Kai kuma inason kanuna tun ina karami aka kawo maka ni


Wannan kadai nakeson kamin malam

Malam Garba yayi murmushi yace gaskiya alhaji kana da tunani mai kyau Allah ya tabbatar da
alkairi

Hakeem da Ahmad suka ce amin malam


Nan suka wa malam sallama Hakeem yadauko bandir din kudi yaba malam yace gashi a
rabawa yara sadaka

Ya ba malam wani kuma yace Gashi wannan nashine

Malam Garba yayi ta musu addua


Acikin mota Ahmad yace amma meyasa makayi wannan tunanin haka Hakeem

Ahmad yace kana nufin bazasu ganeka ba wai kome

Hakeem yayi murmushi yace duk zan shirya wa hakan

Ahmad yace Allah yasa amma dai yakamata duk wani abinda zakayi wallahi kayi sauri kafin

wani yariga ka


Hakeem yayi murmushi yace inaji ajikina wannan yarinyar rabonace

Ahmad yace to tunda kana da tabbacin haka
Meye na gwada ta kuma

Hakeem yace inason nasan mena aura ne kuma rayuwata zanbata kaga kuwa ina bukatar
bincike sosai


Ahmad yace sai prof komai naka daban ne wallahi gaskiya bazan boye maka ba I like your life
style Bros
Keep it up

Hakeem yayi dariya yace baka jiya abokina

Ahmad yace ai bazangaji

Komai naka is so special


****
Bayan sati uku Hakeem yayi order na fuska daga India

Yau yakesaran za akawo mishi

Hakeem ya zaune wani abokin
Wayar shi tadau kara yana sai yaga number din Wanda yaba sautun siyo mishi fuska

Yadaga wayar yace badai har kun isoba
Doctor isah yace gani ma acikin school dinku

Hakeem yace what's a surprise
Ganin zuwa

Hakeem yafita yaje yashigo da doctor isah

Nan Bayan sungaisa doctor isah

Yafito mishi da sakonsa

Hakeem yakarba yace masha Allah kuma gaskiya kayi yadda nace

Doctor isha yace to ai kasan aikan manya irinku ba kasafai akacika muku shirme ba

Hakeem yace zakafara kaima ko

Doctor isha yayi murmushi yace ansamu ragi sosai yallbai dan Rabin yakai dubu Dari da
hamsin

Hakeem yace OK zaka iya barinshi a wajenka yazama naka doctor

Doctor yace a yi haka yallabai
Hakeem yace karka damu ai kamin komai



***

Da daddare Hakeem ya fesa wanka yadauki jallabiyya yasaka yadauko fuskarsa yasaka kafin
yadauki carbi yarike a hanu

Yadauko wayar Nokia da yasa akasayo mishi second hand wacce duk tasha dauri da roba

Ya kalli kanshi a madubi shida kanshi yaba kanshi dariya

Yadauki kudi yan hamsin da kuma 'yan goma yasaka a aljihunshi


Ya kulle gidanshi yafita zuwa gidan Ahmad yayi sallama
Maigadin yace sannu malam daga ina haka kuma gurin wakazo

Yace inason kamin sallama da maigidan ne

Bayan Ahmad yafito ne yaga mutum ustaz har da gemunshi

Yace assalmu alaikum

Hakeem ya amsa mishi cikin canjawar murya


Hakeem dai yakasa danne dariyar shi yacire fuskan

Ahmad wazaigani Hakeem ne

Cike da mamaki Ahmad yace amma ka shammaceni

A ina kasamu masks nasan dakyar akesamu a Nigeria

Hakeem yace daga India aka kawo min
Kaga kai ma danake tunanin zaka ganeni baka ganeniba

Bana tunanin shamsu da mutan gidansu zasu ganeni

Dan haka ni wuce daga yau zafara basu exam's din su

Hakeem ya mayar da fuskarshi yagyara da kyau yadda baza a ganeba
Yayi bakin titi yatari kekenapep zuwa anguwar su Husnah


Next page

Tofa fans za afara wasa fa

Your comments is needed

Ina alfahari da masoya novel na潤 AKWAI LOKACI潤



踫踫踫踫踫
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN 潤撕: 潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤
潤潤潤潤潤潤
潤潤潤潤潤
潤潤潤潤
潤潤潤
潤潤

BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer


UMMU AFAN

踫踫踫踫踫踫踫



潤撕FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION潤撕


潤撕潤撕 (F.C.T.W.A)潤撕潤撕



潤撕HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION潤撕




潤I DEDICATE THIS PAGE TO YOU sister surayya auwal ina matukar jin dadin comments din
ki amma Dan Allah sister kikara yawan comments din ki ina alfahari da Ku da da comments din
ku潤手手手手





潤AKWAI LOKACI 潤





潤PAGE 86 to 90潤





HUSNAH zaune tana gyaran farcenta Umma tace auta nikam ya kukayi da Alhaji ne naga jiya
yazo


Husnah ta bata fuska tace wallahi Umma guduwa nayi dakin anty kubra na buya Dan wallahi
Umma nibana sonshi

Umma tayi salati tasanar da ubangiji
Tace aidaman zaran hijabin dakikayi kaman kinje
Bazuwa kikayi ba


To ma wai meyasa bakya sonshi meyamiki husnah karki zamo me saka alkairi da sharri mana


Tunda Allah baiyi aurenki da shi abdullahinba sai ki ba
Wannan dama kodan halinsa na kirki badan abin hanun shiba



Anty kubra tace wallahi Umma kullum sai namata wannan nasihar amma kamar anshuka dusa



Husnah tace wallahi ni kwatata bana jin zan iya son wani bayan ustaz ne

Kuma bana son na aureshi nakasa yimashi biyayya Umma na Dan Allah kufahimceni


Umma tace ai shi so ahankali yake shiga
Kyawawan halaiyar wannan yaro kadai zaisa kifara sonshi azuciyarki

Dan yana da duk wani nagarta atare dashi



Kafin Husnah ta yi magana ya shamsu yayi sallama yashigo yazauna

Yana gaida umma kubra ta tashi tace sannu dazuwa tayi hanyar fridge tadauko mishi ruwa
maisanyi

Takawo mishi

Ya dauka yasha kafin yakalli umma yace mekuke ta tattaunawa ne ummana

Umma tayi murmushi tace wallahi wannan shasharce muke taba baki saikace wata uwarmu
Sai waina mu takeyi

Ya shamsu ya kalli Husnah yace wai meyake damun kine husnah

Ustaz yariga yatafi bazai dawoba
Wallahi husnah da ace zaidawo lokacin da akeshirin daurin auranki da Abdul Hakeem za afasa
a daura dashi

Sai dai kash ba a mutuwa adawo

Sai dai ina miki albishir dacewan Allah yamiki sakayya da mafificin alkairi


Mun dade muna Neman hanyar da zamu sakawa wadan nan mutane

Sai gashi Allah yakawo tunda yasawa yallbai kaunar ki aransa

Maizai hana kitayamu maida alkairi da alkairi husnah


Abdul Hakeem yamana komai a rayuwa kuma duk abubawan da yayi mana na tabbatar Dan
Allah yayisu


Kaman yadda kema zamu bashi dan Allah badan abin hanun shiba



Husnah tace shikenan yayana
Namaka alkwarin bazan baka kunya ba
Na amince da shi
Amma wallahi danku Dan wallahi yaya bana sonshi



Ya shamsu yayi murmushi yace Abu mafi mahim manci dai shine ki amince



Husnah ta turo bakin shagwabar tace wato bakadamu dani bako yaya na



Ya shamsu yayi dariya yace caf waya fada miki yar kanwata
Yace ai nafi jidake

Dan idan kikayi aure ma fa tare zamu tafi


Husnah tayi murmushi tace ai wallahi yaya da dagaske kake da naji dadi sosai


Amma nasan kana fada be kawai
Amma nifa kullum sai nazo gidan nan



Umma tace kwarai kuwa daga ke har yayan naki zan ga me hankali acikin Ku


Anty kubra tace gaskiya kam umma
Nima naga alama tana dariya

Ya shamsu yace dawa kikeyi yadauki pillow na gefensa ya wurga mata ta tashi
Tagudu yabita shima


Umma tayi murmushi Dan yadda Dan ta guda yake zaune lafiya da matarshi bata taba ganin
wani abun ki agurin kubra



Husnah tace umma Dan Allah yau kimana danbun tsaki da kanki
Kinga yau nice da girki


Umma tayi murmushi tace naki wayon sai girkin 'yata azo zanyi


aikuwa husnah tayi murmushi duk kugama badaini ba wato sai ran girkin anty kubra zakiyi ko
Shikenan nasan mezanyi muku a gidan kuma dole kuci


Umma tayi dariya tace kinga kuwa kyayi aiki har dare kenan



Husnah tayi murmushi ta tashi tace Abba yakusan da wowa

Barin yi kitchen

Tana shiga kitchen din tafara tunanin abinda zata daura

Taduba store dinsu taga suna da doya

Tadauki guda biyu tafere shi tas ta wanke
Ta rarraba shi kanana
Tazuba tunkuya takawo gishiri tasa dai dai misali



Kafin tadebo albasa attaruhu da tattasai dakuma tomatoes amma kwaya hudu tasa tomatoes
din bata bukatar tumatir dayawa

Nan ta wanke komai tas
Tafara greating dinsu a greater ba a blender ba

Dan bata bukatar suyi laushi

Nan tasoya su da mangyada saidataga tayi soyu sannan tadauko yankakkakun kayan namanta
kanana dake cikin fridge tafashashshe
Tazuba tadauko gyararran kifinta Wanda tariga tacire kayar tas shima tazuba tacigaba da
juyawa

Kafin tadauko maggi tazuba dai su curry da thyme da dai sauransu


Tahada tacigaba da soyawa haba ai nan da nan gida ya hau kamshin girkin husnah

Sai da ta tabbatar ya soyu kafin tarage gas din kadan

Tadebo kwai (eggs) guda biyar
Tafasa su a kwano daban tasaka magi guda daya takada

Kafin tadauko tana zubawa kadan kadan tana gaurawa har tagama tacigaba da juyawa

Gaskiya ko itada datayi miyar yakayatar da ita balantana Wanda saidai yagani kawai saici

Nan ta sauke tasama Abba a kulansa kafin tasa ma umma ma anata kulan

Ta ajiye a gefe

Tadauko nasu ya shamsu da anty kubra tasamusu dama tumsafe tayi kunun ayarta Wanda
yasha madara tasaka a fridge yayi balin sanyi kuwa


Ta dauka nasu yaya shamsu tayi da shi part dinsu
Taje tana ta sallama taji shiru

Can saiga anty kubra tafito da gudu daga bedroom dinsu kanta ba Dan kwali ga gashinta duk
an hargitsa

Ga rigarta zif din agaba yake kana ganin kasan akwai magana Dan anfara Jan zif din amma
baikai kasaba



Kubra bata San ma da mutum a falonba ganin husnah kawai tayi tasake baki tana kallonta


Kubra ganin kallon yayi tace ke malama lafiya kuwa


Husnah tayi murmushi tace a a bakomai gani nayi kinfi to kamar wacce tayi dambe da zaki

Takarasa maganar tana dariya


Kubra tasan metake nufi
Itama tayi murmushi tace kema kwana nawane zakije fada da zakin


aikuwa husnah tabarai ta turo bakin tace zakifara ko anty kubra
Ta ajiye musu abincin tace gashi idan kungama soyayyar kwaci

aikuwa tana fadar haka tagudu


Kubra tayi murmushi kawai kafin ta koma ciki




Husnah wanka tafada tana fitowa tayi sallar La asar dinta kafin taje gaban dressing mirro dinta
tafara shafa mai abinta tanagama shafa maidin tadauko body spray tafesa kafin dauko wani

doguwar rigar English wear tasaka


Ta dauki gashinta daure da ribom baki kasancewar kayanta marun colour ne

Yana da bakin dankwali tadaura tayi daurin tauban
Tasaka jambaki shima marun colour gaskiya ba karya duk Wanda ya kalli husnah sai yaso
yasake kallo


Kayan dama dayane daga cikin kayan da mummy hafsat takawo mata ne

Ta fito tasami Abba da umma sungama cin abincinsu

Abba yayi murmushi yace autar Abba gaskiya abincin yayi dadi wallahi
Waya koya miki ne autar ummanta


Umma tayi murmushi aini wani girkin ma fa kirkiran abinta takeyi kuma saikaga yayi dadi


Husnah tayi murmushi tace aini a school dinmu Abba food &nutrition naza ba akan agriculture

Abba yace kai amma auta ta kinyi dabara

Umma ce takatse musu zancen nasu

Tace anya kuwa kinci abinci Dan nasan halinki sarai idan ba aganki ba saiki kai har goma na
dare bakici komai ba



Abba yace wai har yanzu rashin cin abincinta yanan
Umma tace sai abin da yakaru

Idan tagadama wataran dakanta zata dafa indomie

Ya shamsu ne yashigo falon yagaida iyayen nasa

Ganin fitowar ya shamsu yasa husnah zuwa gurin kubra


Wayar ya Shamsu yayi kara yana yaga yallabai kamar yadda ya saving wayar

Yadauka bayan sungaisa prof yakecewa gani acikin gidanku

Ya shamsu yace haba yallabai kaman wani bako kashigo mana

Hakeem yayi murmushi yace ai gurin matata nazo katurota Dan Allah yakashe wayar yana
dariya

Ya shamsu yafada wasu Abba Hakeem ne yazo

Abba yace ya zai tsaya a waje kuma kaje kashiga da shi falonku tunda yau surkunta yakeji
damu

Umma tayi murmushi tace ina ruwan Abdul Hakeem yaron kirki wallahi


Ya shamsu yaje suka shigo tare da Hakeem harkasa Prof yatsuguna yagaida su umma

Kafin ya shamsu yace mune daga ciki tana can ma


Suna sallama dai dai lokacin husnah take gwadawa kubra rawan ittiki

aikuwa Hakeem idonsa kyam akanta ya shamsu yace to dancer of the year

Anty kubra tayi dariya tace sannu dazuwa tana wa Hakeem cike da kulawa ya amsa tareda
tambayarta gida


Nan ta tashi tayi falon su umma Husnah zata bita ya shamsu ke dawo nan baki iya gaisuwa
bako


Cike da jinkuyar Prof tun ranar daya ganta half nacked bata kaunar su hada ido

Tadawo tazauna gefen ya shamsu kai a kasa


Ya shamsu yace to yallabai saika fito


professor Hakeem yace Weldon ya shamsu

Ya shamsu yayi murmushi yafita


Hakeem yamaida kallonshi kan husnah wacce take ta wasada da yatsunta daya sha Jan lalle


Batayi tsam Mani ba kawai taganshi agabanta

11 / 15