Chapter 8 Reading AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf Arewa Novels

AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf

Author :  Ummu Afan Category :  Arewa Hausa Novels

Chapter   8 / 15

21K to 24K   out of 44.6K words


Ameen Ameen gaskiya dai bantabajin mekudi hakaba da Jan talakawa ajikinsa kamar wannan
uban gidan naka

Nan dai suka ta tatattaunawa akan yadda za ayi da kudin

Abba da umma dai suka barmai zabi

Ya shamsu yace shikenan Allah yakaimu gobe aga yadda za ayi

Itakuwa Husnah Allah Allah take safiya tayi taje school taba wa aminiyarta labari

Za a ba copper bash daman turowa gidansu



Washagari Husnah da meenat suna zaune a inda suka saba zama

Husnah tabata labarin za a ba copper bash daman turowa gidansu

aikuwa gaban Meenat yatsinke ras

Wani tashin hankali ya ziyarceta
Tarasa meyake mata dadi

aikuwa har aka tashi daga school meenat batadawo dai dai ba

Tana kallo copper bash ya budewa Husnah gaban motarshi zai kaita gida

Dan tunda aka sanshi yaroki alfarmar zai dinga dawo da Husnah gida idan antashi


Da kyar aka yarda mashi Dan saida yahada da mom dinshi

Husnah tana daga wa meenat hanu Ina AMIN ABDUL HAKEEM kam batasan tanayiba

Ta Lula dunitar tunani

**
MEENAT tana zuwa gida tafada cinyar hajiya rukayya kakanta

Tafashe da kuka maitsanani

Hankalin hajiya rukayya yatashi Dan ta dauki soyayyar duniya ta daura akan 'yar jikan nata
bakaramin so takewa Amina ba

Nan dai dakyar tasamu meenat tayi magana

Tace hajiya nashiga uku nakusan mutuwa

Wallahi idan ban auri copper bash hajiya zaku iya rasani dan mutuwa zanyi

Nan hajiya rukayya tace kwantar da hankalinki kimin bayanin komai

Nan meenat ta kwashe komai tafada mata

Ba abinda yafi burge Hajiya rukayya a labarin sai jin cewan

Bash Dan hamshakin mai kudine a kano


Tace kwantar da hankalinki kaman yazama naki ma anfama

Aure shida Husnah kuma yazama tarihi

Zanje Kaduna aiko
Zan baki mamaki bash da bakinshi zaice yanasonki


Next page

Your comments is needed fans

Kamar yadda nayi typing metsayi haka nakeson

Comments dinki da tsayi

Wallahi comments mai tsayi yana burgeni
Sosai

Ina yinku masoya AKWAI LOKACI踫踫踫踫踫踫

踫踫踫踫踫
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN 潤撕:
潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤

BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM


潤HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN 潤


潤撕潤撕FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION潤撕潤撕

潤撕F.C.T.W.A潤撕



潤撕HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION潤撕



潤DEDICATE THIS PAGE TO adda khadija and shamsu ina yinki over sister
Dik ina ganin comment din ki akan novel di na
Wato AKWAI LOKACI踫踫踫踫

Daya bayan daya zakuji sunanku masoya AKWAI LOKACI FANS GROUP 踫踫 keep
comments kawai 踫




潤AKWAI LOKACI潤




潤PAGE 51 to 60潤

Ya shamsu ya yagyara wa iyayensa gida dai dai gwargwado

Har anyi fenti sabo gida sai kamshin sabon fenti yakeyi da sabon siminti


Ya zuba wa umma sabbin kujeru dai dai karfinshi

Sannan shima ya zuba a dakinsu shida kubra

Yasai TV guda biyu dayasa wa iyayensa daya kuma yasa a sashinsa

Sannan kuma yama umman shi dinkuna kala biyar na fitan biki sai yama abbanshi ma kala
biyar shima masu kyau shadda da kuma yadi

Umma har da hijab uku da ta kallamansu
Uku


Sai Husnah kuma yamata kusan kala bakwai dai dai karfinsa
Ya hada mata da mayafai guda biyar da takalman ta hudu

Sai kayan kwalliya da dai sauransu

Yafi kashe wa Husnah kudi acewanshi ita tafi bukatar hakan


Yama kubra ma kayan fitan biki yace kartayi amfani Dana lefenta

Sannan kuma yasa wa abbanshi kaya a shago Dan dama Abba yana shawa ar sana ar awu na
hatsi



*****

Yauce ranar daurin auren shamsu da amaryarsa khadija
Komai yatafi yadda akeso

ankai amarya dakinta dake cikin gidan su shamsu

****

an daura auren Ahmad da amaryarsa Aisha
Suna shirin zuwa dinner ne Wanda PROFESSOR HAKEEM ya hada wa babban abokinsa


Hakeem da Ahmad sunyi shiga iri daya wani hadadden suit suka saka ango yasaka baki nacikin
ja

Sai Hakeem kuma yasaka brown colour na cikin sa fari

Duk Wanda ya kalli PROF HAKEEM sai yasake kallonshi


'Yam mata sai rawankai suke musam man kawayen amarya


Laila ma taci ado cikin wani tsadadden less Wanda tayi order daga malesia

Tayi kyau kan nan yasha gashin doki
Fuska kuma yaci bleaching kana ganinta dai kasan anci duniya

Ango yashiga mota zuwa gurin dinner

Hakeem yabude mishi bayan mota Laila kuma ta babbar kawar amarya kuma ta bude wa
amarya dayan gefen tashiga


Hakeem ne zaija motar ahmad yace Man please kamin wata alfarma mana
Hakeem yace ina sauraronka malam ango

Ahmad yace kasan idan muisa wajen babbar kawar Aisha ce zata bude mata kofa tunda kai
kadaine a gaban motar ta shiga muje kawai

Hakeem yayi shiru alamun ya amince kenan

Shine rahma kawar amarya tashige gaban mota tana gaida Hakeem ya amsa a dakile kaman
bayaso



Suna isa kuwa bayan Hakeem yayi parking aikuwa har 'yan gulma sunje sun sanar da Laila
cewan ga Mijinta ya dauko budurwa a gaban mota

ai kuwa tafito kaman wata mahaukaciya dai dai lokacin da rahma kawar amarya take fitowa
daga motar Hakeem


aikuwa rahma batayi tsammani ba sai taji mari kau sannan kuma akasa kafa aka kwasheta

aikuwa yazo da tsautsayi rahma tabuga kai sosai take kuwa ta suma

aikuwa cikin tsannanin bacinrai Hakeem yadauki hanu ya zabga wa Laila mari yasake kwasheta
da mari

Nan fa mutane aka taru ganin wannan Abu da Laila ta aikata
Nan da nan 'yan uwan rahma dama suma suna gun sukace basu yarda bayan ansa mata ruwa
ta farka


Hakeem yace kinayin abin kika dama ina kyaleki idan zanyi aure kin isa kiha nanine

To barin fada miki daga yau kikasake min dabban ci irin haka wallahi zanyi maganin ki ban
wawaiya kawai

Wasu da basusan suwayeba

Wata 'yar dattijuwa ta matso tace haba 'yar nan Kinsan fa yaran yanzu ba a hanasu auren
abinda sukeso koda kuwa iyayensu ne
Ballantana keda gani dai baki haifeshi saidai kizama yarshi aisai hakuri

Tajuya kan Hakeem tace haba d'ana da hankalinka zaka mari yayarka a cikin mutane akan
mace

Wasu abin dariya yabasu wasu kunya wasu kuma haushi

Musammam meenat cikin gatsali tafito daga cikin taron

Tacewa matar nan dalla malama kirufemana baki
Wayafada miki kanintane dazakisa mutane agaba da surutu to banana ne itakuma mamana ne
Dan haka kikama gabanki bamason muna furci

Wato cikin tsananin bacin rai Hakeem yadanko Amina yayi mota da ita ya wurga ta ta tashi
motar sai gida

aikuwa Laila tace shikenan zaikashe min 'yartawa Dan zata kwacewa uwarta 'yanci
Tana ihu tana kokarin shiga mota sai saiga motan police nan sunzo tafiya da ita 'yan uwan
rahma kawar amaryace suka dauko 'yansanda aikuwa suka tafi da Laila


Hankalin Ahmad yatashi yace wa Aisha amarya tayi hakuri bari yakira akawo mishi mota subi
bayan Hakeem Dan komai zaiya faruwa



Hakeem na isa gidansu yayi sashen sa Meenat ya dauki belt dukanta yasoma

Kuka sosai meenat take tana bashi hakuri

Wayyo Allah daddy kayi hakuri wallahi bazan sakeba yace Ashe baki da mutunci kikalli kaman
wannan matar kimata rashin kunya ko

Abinda uwarki da kakanki suka koya miki ko
To ba agidana ba Dan ubanki

Mummy hafsat ce yashigo da kyar ta karbi meenat agurin uban

Hakeem ya kalli mummy yace mummy Dan Allah bana son yarinyar nan ta koma gurinsu
Kwatata sunbata wa yarinya tarbiyya

Mummy hafsat tace wai meyafarune nan Hakeem yafada wa mummy hafsat komai harda
dabbancin da uwarta tayi a wajen dinner


Mummy hafsat tayi salati tace yanzu wadan nan mutane bazasu canja haliba gashi harsuna
Neman bata mana jika


Kaman daga sama kuwa suka ance sannu masu tarbiyya
Dana nasan ba Wanda yake haddasa fituna saike hafsat

To wallahi anzo gurin da banzan bariba dan me zaudauki hanu yata dukan matarshi acikin
bainar jama a


Mummyn Hakeem tace aini abinda Hakeem yayi amin dai dai duk abinda Laila takeyi tasamu
daurin gidinkine yaya rukayya

Hajiya rukayya tace wato kekikabashi daman yadauki karuwa a mota ko

Mummyn Hakeem tace ya isa haka yaya rukayya wallahi zanyadda da komai amma banda
mummunan kazafi akan Abdul Hakeem

To wai ma da kuke wannan haukan wayace muku Hakeem bazai kara aure ba

ai Karin aure akan Hakeem wajibine Dan wallahi koshi baiyi niyya ba nizansashi aure dolene


aikuwa hajiya rukayya tafashe da kuka tace yanzu hafsat nizaki cewa mahaukata ina matsayin
yar mijinki kidubi tsaban idona kice muna hauka

Mummy hafsat tace duk abinda yafaru kokuka janyo
Kuma wannan yarinya da kuka sangarta bazata koma wajenkuba

Zanriketa har Allah yasa tagane gaskiya tadawo hanya bakaman Ku da kuka bata ba



Hajiya rukayya tace wannan kuma baki isaba hafsat kinyi kadan kirabani da jikata

Mummy hafsat tace zancen kikeso

Tana amina fuuuuuu suka bar falon



Hakeem kuwa barin falon yayi zuwa dakinsa

Sukabar hajiya rukayya kaman tafashe dan bakin ciki

Wayar hajiya rukayya tayi kara taduba taga Suby ce kanwar Laila tace kekuma ya akayi

Suby cikin tashin hankali tace mama gamunan a police station ankulle anty Laila

Hajiya rukayya tace wani station din kuke

Nan tafada mata tafita zuwa police station din

Hakeem yana shiga bedroom dinshi wanka yashiga

Kafin yafito yadan kwanta yana tunanin bakin hali irin na Laila da 'yan uwanta


**
alhaji abubakar yana office din shi azaune saboda yayi baki daga India

Sai yaji kiran yayarshi hajiya rukayya

Yadauka tare da sallama
Hajiya rukayya tafashe da kuka tace duk inda kake kazo gida ba Lafiya

Matarka da 'danka zasukashemin 'yata da jikata

alhaji abuabakar yace subahanalla ganin zuwa yaya kidaina kukan Dan Allah


Ya kashe wayar yadau hanyar gida

Yana zuwa yasamu yayansa hajiya rukayya a kofar gidanshi
Yafito amota da sauri yace mekefaruwa ne haka

Nan dai ta kwashe karya da gaskiya tafada mashi yace yanzu kishiga mota muji police station
din ayi belinta
Inyaso sai mudawo gida a yi magana


Hajiya rukayya tashiga mota suka nufi can police station din
Suna isa tun kamin ayi parking suka ga Ahmad da Laila

Ahmad yaga motar daddyn Hakeem sai yakaraso gurin motar yagai da daddy

Daddy yace sunbaka belin kenan
Ahmad yace a amma dakyar suka bayar sai da nasa hanun zata je har gida tabawa yarinyar
data sumar hakuri

Daddy yace Allah yarufa asiri kaima kayi kokari Ahmad Allah yabaku masu yimuku

Ahmad yace ameen daddy barin karasa gidan

Daddy yace wa Laila tashiga bayan motar sutafi tabude bayan tashiga

Ta madubi hajiya rukayya tace Dan Allah kalli yadda suka mayar min yarinya saikace wacce
bata da gata

Alhaji abubakar dai baice komai har suka isa gida


Duk yatarasu a falo Hakeem na zaune daddy yace banji daddyn abinda yafaruba naji komai

amma ina insan kai Hakeem wace mata kadauko agaban mota nan Hakeem yawa mahaifinsa
bayanin

Hajiya rukayya tace karya kakeyi kana nufin Laila Karya zata maka

Mummyn Hakeem tace to ita Lailar uwarshice dabazata mishi karya ba

Daddyn Hakeem ya ce ban baki iznin maganaba hafsatu kiyi shiru

Mummy hafsat tayi kwafa

Nan dai daddy yayi musu nasiha meshiga jiki

Hajiya rukayya tace sai maganar yarinya sunce wai bazan koma da Amina ba

Daddy ya kalli Hakeem yace yazakayi haka bayan kuma yarinya dasu tasaba

Hakeem yace daddy idan har yarinyar nan zata koma to ta gaggauta fito da miji tana gama
secondary school kawai aiyi aure

Dan wannan da irin tarbiyyar dasuka bata nan gaba zata iya fin karfin mutane

Mummy hafsat tace wannan shawarar taka tayi dai dai
Dan bazanso jikata ta acikin wannan rayuwar da ba asan nagaba ba

Hajiya rukayya tace kaga abubakar kashiga tskanina da matarka

Daddy Hakeem yace wa mummy hafsat Dan Allah karkisake cewa komai sai na baki dama


Nan alhaji abubakar yace zata koma amma gaskiya nima anan naba da goyan bayan tafitar da
miji kafin nan da tagama secondary school

Hajiya rukayya tace wannan ba abin muwabane
Abamu nan wani lokaci saurayinta zaizo dakanshi yagaisheku aitana dashi

Alhaji abubakar yace to alhamdullila Dan Allah komai ya wuce

Ke Laila ba wa mijinki hakuri
aikuwa hajiya rukayya tace ya za ace tabashi hakuri bayan shiyakamata yabata hakuri daya
dauki hanu ya tsinka mata mari acikin mutane


Ganin abinda hajiya rukayya takeyi yasa Hakeem barin falon yayi sashinsa

Yana fita suka hadu da Ahmad
Hakeem yace ango

Ahmad yace komaidai yakoma dai dai ko Hakeem yace barin shiga nashirya nazo muwuce

Muje musallami friends dinmu na nesa

Ahmad yace karka damu nagama komai

Hakeem yace yanzu har ka rakasu airport Ahmad yace kwarai

Hakeem yace amayar fa Ahmad yayi murmushi yace ai andade da tafiya da amarya

Dan dazu nakirata harsun huta ma

Yan uwanta ma sun kamo hanyar dawowa

Hakeem yace to ai sai musamu mushirya muwuce muma ko karnayi laifi dayawa agurin Madam
Aisha

Ahmad yayi murmushi yace a haba aitasan komai

Idan taga bamuzo ba tasan abinda yatsare mu

Hakeem yace yau zaka shiga dakin amaryar ka

Barima kagani Hakeem yashige sashinsa

Yafada bathroom yayi wanka
Yana gama shiri cikin shadda marun colour ya balain masa kyau kamar danshi akayi shaddar

Yana fesa turare Laila tashigo
Tace daddyn meenat naga kaman tafiya zakayi baka sallamemuba

Hakeem ya watsa mata wani kallo

Yace mekuke bukata tace kayan abinci da na amfanin gida yace kizauna kirubuta duk abinda
bukata zansa driver yakawo muku

Daga yau nabar baki daman da kikesamu harkike ganin kaman kinfi karfina sai yadda kikayi
dani ko

cikin tashin Hankali Laila tace Dan Allah karkamin wannan horon kasan nasaba sayan abinda
nake bukata da kaina


Hakeem yayi murmushi mugunta yace nawa nakebaki dama

Laila tace dubu Dari uku duk wata

Hakeem yace hakane ko ta ce a hakane

Yace kedawa nabari agidan nan tace nikadai

Yace good yanzu duk wata zanturo miki dubu hamsin

Kekadai dai nasan zasu isheki

Yana gama fadan haka yayi waje da brief case dinshi



Haukane Kane kawai Laila batayi ba
Amma hankalinsa yatashi sosai nan tadauki gyalanta tayi gurin mahaifiyarta hajiya rukayya


****
Bayan wata shida professor Hakeem zaune kan kujerar office din shi

Yadauki wayarshi yakira yaya shamsu

Ya shamsu yashigo yace Barka dai yallabai sannu da aiki Hakeem yayi murmushi yace yauwa
malam shamsu

Yace ga wannan ya shamsu yakarba yace ina zankai yallabai

Hakeem yayi murmushi yace nakane malam shamsu zaka kaiya dubawa kagani

Ya shamsu yabude Aikuwa ya shamsu ya dago ido yakalli PROF Hakeem

Yace admission fa nake gani yallabai

Hakeem yace yes nasan kana da burin karatu a rayuwarka

Iyakacin zamana da kai na lura kai mutum ne mai son karatu

So yanzu ga dama nan malam shamsu zaka iya farawa nagama komai har registration da
komai sai dai ka kai credentials dinka asa maka a file

Kuma daga Level two zakafara nariga nayi komai

A department of business administration


Ya shamsu baisan lokacin da tashiba yace yallabai gaskiya ba abinda zance da sai dai Allah
yabaka abinda kake nema duniya da lahira
Allah ya jikan mahaifanka ya ramaka zuria

Hakeem yace ameen malam shamsu na gode kwarai da adduarka a gareni

Sai dai ni har yanzu baka taba tambayata wani Abu da yashafi rayuwata ba malam shamsu
koba bukatar sanin daga ina nafito ne

Ya shamsu yayi murmushi yace zanso sanin tarihinka dakuma tarihin nagartarka a rayuwar
alumma


Nan professor Hakeem yayi murmushi
Yabashi labarin rayuwarshi kaf bai boye mai komai ba


Ya shamsu yaja numfashi yace yanzu tun kana 20years kayi aure kenan

Hakeem yace kwaraikuwa ina da 17 year old girl yanzu haka

8 / 15