Chapter 13 Reading AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf Arewa Novels

AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf

Author :  Ummu Afan Category :  Arewa Hausa Novels

Chapter   13 / 15

36K to 39K   out of 44.6K words




Hajiya suwaiba ta sauka har kasa tace Dan Allah abubakar kayafe min wallahi duk sharrin
shaidan ne hakan bazai kara faruwaba

Daddyn Hakeem yace haba Hajiya ai duk da abinda kika min bazaisa nadaina ganin ki a
matsayin uwaba
Dan haka kitashi daga tsuguna min


Hajiya suwaiba tace nagode Allah yamaka albarka kaida zuriarka

Hajiya rukayya ma tana kuka taba wa daddyn Hakeem hakuri daddy dayake shiba meruko bane
ya yafemata


Hakeem ya kalli mahaifin nasa yaga daddy na goge kwalla
Bakomai yasa daddy kukaba sai rashin imani irin nasu

Idan ya tuna sune sillar rabashida mahaifiyarshi da ko kamannin ta baisaniba saiyaji wani kunci
Daddy kasa jurewa yayi yatashi yashige bedroom dinsa

Abdul Hakeem yabi bayansa mummy hafsat ma tashi tayi tabisu


Hajiya rukayya tabuga tsaki aikin banza wallahi wannan kukan danayi bazai tagi banzaba

Hajiya suwaiba tace towayafada miki dama tubar gaskiyace

ai kawai ganinayi asirinmu yatonu shiyasa na bullo musu tanan


Laila cikin kuka tace yanzu dai kuna gani Hakeem zaikawo wata dasunan mata

Suby kanwar Laila ta ce ai wallahi duk wacce tayi gigin shigowa gidan ki anty Laila wallahi taja
wakanta balain duniya Dan wallahi sai mun nakasa rayuwarta


Hajiya rukayya tace ai zama bai kamamuba

Ke Hajiya bari musa driver yamaidake gida

Gobe zamuyi nijar saboda ke Laila yau kije kibashi hakuri

Kinuna kinyi ladamar abinda kika aikata har dai yasamu yabarki gobe mutafi


Laila tace shikenan hajiyarmu Allah yabar mana.ke kina kokari ganin farin cikinmu


Nan sukatashi kowa yakama gabansa


Laila ta koma part dinsu tazauna tana tunanin abubuwan da suka faru

Wanda sana diyarshi allura ta tono garma



****

Laila sundawo daga nijar yanzu tana zaune ne zaman jiran amarya Dan tafara aiwatar da
niyarta

Hakeem kuwa sake tsarin gidannasu yabayar akeyi badare ba rana
aiki ake zabgawa


Zama yayi yaga gaskiya a yanzu yakamata dadinsa yadaina fita office
Shiyakamata yayi komai su su huta

Kuma bashida da sha'awar raba gida da mahaifansa

Yayi shawarar dawowa A B U Zaria sunfi kusa da nan

Zaisamu daman da dazaije ya kula da harkokin kasuwancin daddynsa

Ahmad ma yace shima kawai kadunan zaidawo yacigaba da rike company daddynsa
Shiya sama yasa ma aikata gyaran gidanshi na Kaduna

Sunyi parking gabadaya zuwa Kaduna Aisha matar Ahmad ta tare a sabon gidanta dake
Kaduna



Hakeem ankam mala komai ainda aka fitar wa da kowa dinshi

Part din Hakeem yana tsakiyarsu

A babban folon PROF zai iya shiga part din kowacce falon nashi guda biyu akwai a sama
Wanda idan ka haura sama falon PROF shima daga gefe kuma wasu maka makan bedroom
dinshi guda biyune


Kai gaskiya dai naira tayi kuka a gidan Prof

Gabakidayansu yasakewa was furniture's har daiyayensa

Komai yazuba wa Husnah Wanda uba yake wa 'yarsa Prof ya dau nauyin komai

Bakin ciki kamar zai kashe Laila amma ba yadda ta iya dole tanuna bakomai saboda tasamu ta
cimma burin ta akan amaryarsa



Mummy hafsat gobe zasu daga zuwa Dubai itada mummyn Ahmad

Hado kayan lefe


*******

Biki ya rage saura kwana hudu Hakeem ne cikin motarshi yana zaune agefen mai zaman banza

Yayinda Ahmad kuma yake driving zasu kano gidan su husnah


Ahmad yace kai prof gaskiya kacanja wallahi gaskiya Allah yawa husnah albarka data saita
mana kai

Dafa magana wahala yakebaka
amman yanzu sai a zauna dakai asha hira musam man ma na husnah


Hakeem yayi murmushi yace kaikuma dadina dakai sa ido wallahi

Ahmad yace aidole ne asamaka ido yadda yarinya karama tacanja ka


Hakeem dai murmushi yayi yace bazaka kanebane abokina bakasan yadda nakejin babyn a
raina bane ko



Ana kiran la asar suna shiga gidansu husnah ya shamsu yataresuda murna yace kaga
manyan kannena

Ahmad yayi murmushi yace fada dakyau ya shamsu girma fa Allah yabaka


Hakeem yace kana mamakine yaya shamsu

Ya shamsu yayi dariya yace waneni da mamaki Dan na zama yayan manyan maza

Daga shiya shamsun dayayi maganar harsu Ahmad da Hakeem sai da sukadara

Ya shamsu yace bissimilla mushiga daga ciki

Hakeem yace mudai fara gabatar da sallah tukun

Nan suka wuce masallacin unguwar




Husnah zaune itada anty kubra

Anty kubra tace Dan Allah husnah kisanar da kawayenki
Maganar bikinki


Husnah ta yatsina fuska tace nifa bazanyi taroba ma

Nibana mason hayaniya wallahi

Kuma da kika damu bagakiba dake da anty Aisha kusai kuzama kawayena


Kubra tarike baki tace lalle husnah wuyanki ya isa yanka
Nice ma zan zama kawarki ko


Husnah tace to Baku kuka dage saina aureshi ba


Anty kubra tayi murmushi tace aini dadina da gobe saurin zuwa
Kaman yaune zakizo kinacemin anty kubra
Wallahi inason mijina


Husnah tayi murmushi tace humm anty kenan nifa nafada miki auren biyayya kawai zanyi
amma ba wai danso ba

ai nagama soyayya


Anty kubra tace shikenan tunda haka kikace akwai ranar maida martani


Anty jumai wacce aka dauko tunda Sudan saboda gyaran amarya tunda akasa bikin washagari
ummu tayi Sudan dama can ita mutuniyar cance


Anty jumai tadubi husnah tace tashi muje kishiga wankar tunda
Hadin yayi awa biyu da shafawa

Husnah tace anty wai Dan Allah yaushe za adaina min wannan shafe shafen nan da shaye
shayen nan


Anty jumai tayi dariya tace sai randa kikabar gidan

Kuma kuji dakyau dawasu zaki taki tafi

aikuwa Husnah ta turo baki ta tashi taje ta shiga wanka

Tana kansaka kaya taji muryar su yayanta da PROF suna gaisawa da umma a falo


Tayi niyar kwalliya tafasa Dan mutumin nan yabata tsoro ranar


Riga da skirt tasaka nawani tsadaddan net tayi kyau bakadanba

Powda kawai tashafa sai man baki

Tana kan maida kayanta cikin durowa anty kubra tashigo tace amarya ango nakira yana
falonmu husnah ta turo baki tace anty kinfara ko


Zanrama wallahi nasan abinda zanmiki kema

Kubra tace ya hakuri 'yar kanwata nadaina

Dan nasan ki sarai wallahi


Husnah tayi murmushi tace a to dole abani hakuri dai

Tadauki mayafin kayan tayafa

Kubra tace kai husnah kedai komai baki baiwane

Wallahi kinwani canja ne fa gabadaya
Kinciko tako ta ina

Jin abinda anty kubra tace yasa husnah tunani tabbas ko itakanta tasan komai nata yacanja

Kuma acikin sati biyun nan da akafara mata gyaran jiki ne


To gaskiya bazata tasa gyaleba

Ta ajiye gyalen tadauki jibgegen jijabinta

Anty kubra tace haba Dan Allah mijinkine fa yazo zakije masa da wannan katon hijabin

ai gwamma dai kidau ki mayafin dakikayi niyar sawa

Kinga zaisake shiga hanu kafin nan da kwana hudun nan


Husnah tace aikuwa kinja ma wallahi rayuwar hijabin zanyi agidansa


Ta wuce anty kubra tayi falon


Tashiga da sallama ya amsa mata tamkar wani balarabe

Kamshin sa yacika falon

Husnah tanemi kasa tazauna


PROF yakureta da kallo wani kyau yaga tamishi
Kaman yau yafara ganinta


Husnah tagaisheshi bai amsa ba jin bai amsa ba yasa tadago suka hada ido yakafeta da
idonshi

Kasan yasauko yazauna yana fuskantarta yace haka ake tarbar miji baby

Tayi shiru batace komaiba yace babay magana nake fa


Husnah cikin shagwabarta Wanda ita bada niyya tayi shiba tace menama kuma

Yace nafarko nace kidaina samin hijabi idan zakizo gurina bakida mayafaine

Tace tokai meyasa bakason insa hijabin

Hakeem very good question
Nafarko inason hijabi amma a muhallin daya dace asaka kaman kiganni da wani ko abokaina
da kuma sauransu


amma banda dagani saike kisaka
Bakisan nazo naganki Dan nasamu nutsuwabane ?

Husnah tayi shiru tana wasada da zobenta

Murmushi Prof yayi Yakama hanunta tana kokarin janye hanunta prof yacire zoben hanunta
Kafin yasaketa


aikuwa Husnah ta kalleshi a tsorace tace Dan Allah kayi hakuri kabani zobenan

Yace meyasa zan baki tace nima bani akayi

Yace wakenan tayi rau da ido kaman zatayi kuka

Tace masoyina ya muallim


Yace zan baki amman saikinbi maganana kicire wannan jijabin
Dan ba anan yakamata kisaba

Husnah tace Dan Allah yaya kayi hakuri kabarni da hijabina nariga nasaba

Hakeem yace OK yasaka zoben a aljihunsa

Yace nawa kike bukata game da events din ki

Husnah takalleshi tace nima bana bukatar komai

Ya kalleta da mamaki yace saboda me tace bakomai wallahi ni duk wani Abu dayashafi bidia
bana kaunarsa


Dan Allah yaya daman inason na roki alfarmar events din dakukasa akatin nan wallahi banaso
Dan Allah kabarshi kawai



Hakeem yace duk abindakikace haka za ayi amma bashi ne
Duk randa kika haifamin baby zan baki mamaki duk abinda ba ayi a bikin nan ba saina yishi


Husnah tayi shiru can tace tokabani zoben yashare zancen

Yafito da kudi dubu Dari shida ya aje mata yace gasu nasan zaki bukaci kudi banason kitambayi
ya shamsu ko Abba


Duk abinda kike bukata let me know OK

Ya cigaba da kallonta kawai kaman yasami TV

Husnah tace maganar zoben
Yace sakinyi abinda nace miki
Husnah tace nayarda amma saidai nakoma na dauko mayafina

Baice komaiba sai binta dayayi da kallo


Shigowar husnah Hakeem kusan suman zaune yayi Dan baitaba tunanin abinda idonshi
zaiganiba kenan


Da sauri yace baby go and wear your hijab please


Husnah takoma da sauri
Tana shiga dakinta fashe da dariya
Dan bakaramin dariya yabata ba


Hakeem dafe kai yayi take hankalinsa ya tashi

Nan yafara tambayar kansa
Meyasa sai akan yarinyar nan yake jin feelings haka

Maiyasa komai nata is so special to me


Da kyar yaja kafarsa yafita zuwa gurinsu Ahmad da ya shamsu


Ahmad yace muwuce ko PROF yace

Hakeem yace muje muma su umma sallama

*******
Laila takira meenat tafada mata duk abinda kefaruwa


aikuwa meenat kaman tayi tsuntsuwa tazo Nigeria


Tace kiyi abinki mummy babu matar data isa kiyi kishi da ita wallahi

Idan mukazo koni ko 'yar iskar da tayi kasadar auran daddyna


Suna gama waya da Mummynta Laila

Tadubi Bashir tace kaji kuwa mekefaruwa agidanmu

Bash yace saikin fada

Takwashe komai tafada mishi

Tsaki bash yayi yatashi

Yabar gun



Next page

Your comments is needed fan's


Love u all


踫踫踫踫踫踫踫踫踫踫踫踫踫踫
[05/05, 8:53 PM] UMMU AFAN 潤撕: 潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤
潤潤潤潤潤潤
潤潤潤潤潤
潤潤潤潤
潤潤潤
潤潤


BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer


UMMU AFAN

踫踫踫踫踫踫踫



潤撕FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION潤撕


潤撕潤撕 (F.C.T.W.A)潤撕潤撕



潤撕HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION潤撕




潤I DEDICATE THIS PAGE TO YOU Hauwa'u idris ( maman daddy )
Allah yabar zumunci inajin dadin comment din ki Allah yabar kauna keep it up踫踫踫踫踫潤





潤AKWAI lokaci潤




潤PAGE 101to105潤

PROF yashigo direct dakin amaryar ya wuce sai yaji kofa gam

Kuma gashi bashida spire key
Duk guda hudun suna hade da juna


Ya koma dakinsa yayi wanka
Ya koma kan bed dinsa yadauki waya
Yasoma dialing din number husnah yayita ringing

Husnah bata daga wayar ba

Prof yayi mirmushi Wanda shikadai yasan abinda yasashi murmushi

Ya rufe ido Dan bacci amma bacci yace baisan zancenba


Yadauki wayarshi kawai yakira Ahmad

Saida yakira Ahmad sau biyu kafin ya dauka

Ahmad yace kai ango yadai kira da wannan lokacin

Hakeem yace kai dai bari wallahi man
Wallahi yarinyar nan ta kulle min kofa

aikafin yakai karshe Ahmed yafashe da dariya sosai yayi dariyarshi

Kafin yace amma wallahi husnah ta burgeni
Sosai

Hakeem yace Dan iska dariya zaka min ko

Ahmad yace aikaine abokina duk kabi ka tsorata masu yarinya aidole ta kulle kofarta
Dan batasan mezaifaruba idan akabarku Ku biyu

Hakeem yayi murmushi yace duk tagama buyanta badai ta shigo hanu ba

Zanbata mamaki zata shigo hanu ai

Ahmad yace wallahi dai kabi yarinyar mutane a hankali
Bafa babbar mace bace

Dan nasan kasaba da manyan mata

Yayi dariya yakashe wayar shi


Hakeem cikin murmushi yabi wayar da kallo

Yace zanrama ne

Kafin yakoma amma bacci fa yaki Sam
Daya rufe ido zaiga husnah alokacin da yake kissing dinta

Sai yayi murmushi ya rungume pillow kawai bacci yayi awun gaba dashi

Laila duk abinda kefaruwa tana lebe tana gani aikuwa ganin Hakeem ya burda kofa yaji akulle
duk ta gani

Har wayan dasukayi da Ahmad taji aikuwa cikin farinciki ta koma part dinta ta sanar da su
hajiyarta da kanwarta suby

Dan basu komaba ita suby auran nata ya mutu shiyasa zata zauna gurin Laila


aikuwa cikin farinciki hajiya rukayya tace aikin banza Ashe ma duk abinda suke yarinya bata so

Suby tace a a karku manta dama boka yace zai sa gaba a tsakaninsu

Watakila aikin ne boka ne yafara aikitakanta

Inbahakaba wazaiki yaya Hakeem a matsayin miji

Hajiyarsu tace tabbas maganarki hakatake

Kunga ganiba gwamma da muka sake mishi kudi gashi anfara aganin cigaba

Laila dai da farin ciki ta kwanta abinta zuciyarta fati kal



Karfe hudu dai dai na asuba Husnah tafarka cikin nannauyar baccin da ya dauketa

Tashi tayi tashiga bathroom alwala tayi kafin tayi nafilfilunta kamar yarda tasaba ana kiran sallar

asuba tayi sallarta tayi adduointa da karatun alkur'ani

Kafin tacire kayan jikinta Dan jiya bata samu daman cire kayan ba saboda gajiya

Tashiga wanka kafin tafito
Spray kawai da shuwa tashafa sleeping dress tasaka duguwar riga abinta tafada gado abinta

Sosai taji dadin baccinta Hakeem bayan yadawo daga sallar asuba yasake tana dakin husnah
shiru bata budeba

Direct dakinshi ya wuce dakinsa
Shima baccin yakoma


Karfe bakwai da rabi dai dai mai aikin mummy ta buga kofa

Suby kanwar Laila ita tabude kofar

Taga me aikin mummyn Hakeem ce

Tace sannu suby ta yatsina baki yadai ina zaki da basket din abinci haka

Tace hajiya ce ta aikeni nakawo ma amarya abin karyawa

Suby ta kebe baki tace to aikuma basu tashiba amma kawo saina na mika mata

Tabata abincin

Suby ta karba tashige dashi part dinsu gurin su Laila da hajiya rukayya

Laila cikin murna tace yauwa suby dauko maganin a side drawer kikawo

Aikuwa haka suka barbade komai da maganin nan

Farfesuf na kayan ciki sai kunun gyada da kosai

Kai kuma farfesun ganda Wanda yasha kayan hadi sosai

Haka suka bikomai suka badeshi tas

Hajiyq rukayya tace maza ke suby tashi kikaimata

Laila tace abarta ta kai Dan tanason ganin amaryar

Hajiya rukayya tace a a idan kika kai dakanki za azargi wani Abu

Zakiganta ai mudai burinmu kawai tabar gidan

Suby tace wallahi nimafa basanin amaryar nayi bama dan haushi


Husnah cikin bacci taji ana buga mata kofa ta tashi tayi hanyar falonta

Tayi kofa tabude sukayi ido hudu da suby
Suby sai tadauka kaman gezo idonta suke mata wannan irin zukekiyar yarinyar kuma daga ina

Husnah ta ce sannu suby tace ina antyntaki

Husnah ta yatsina fuska tace antyna kuma

Suby tace ina nufin amaya
Husnah tayi murmushi tace OK ai tashiga wanka

Tana ganin suby tasauke ajiyar zuciya

Husnah ta kibata hanya kuma
Suby tace ga shi inji hajiyar yaya Hakeem akawo mata

Husnah tace OK angode barin kaimata
Suby ta mika mata basket din husnah tarufe kofarta

13 / 15