Author : Ummu Afan Category : Arewa Hausa Novels
wasa fa watan meenat shadaya amma amma haryanzu
mahaifinta baizoba
Suby tace wai Ku meye kuka damu sai yadawo ne bakusan idan yadawo Baku basamun abinda
kuke samu yanzu ba """""
Laila tace nimadai haka nagani
Nifa wallahi tunda acikamin jaka da abinda nakeso yashekara goma ma baizoba ba abinda
yadameni
Hajiya rukayya tace duk kurinta ne yake damunku inba yarinta ba ai wallahi idan yashigo hanu
zamufi yadda muke yanzu
Dan sai abinda tace zaibata komai ta tambaya zaiyi jiki na bari
amma hakan bazaiyu ba sai
Yaci abinci da maganin har na wajen wata daya inji malam
To ta yaya hakan zaifaru idan bata jawo shi jikinta ba
Laila tace kuma fa hakane mama yanzu manene shawararki mama
Hajiya rukayya tace yauwa anzo gun danakeson azo
Kinga yanzu abinda zakiyi ke Laila kisamu Daddyn Hakeem kice kizakibi mijinki can saudin
Nasan shi da hangen nesa bazaiso shiga hakkin waniba
Idan kikaje can duk wani Abu na biyayyya ki kirkiro kiringa mishi inda zamusamu yasaki jiki
dake sosai inda har zaki bashi abinci kuma yaci
Laila tace to mama yanzu dai zanshirya na tafi gidan mummy hafsat
Zanfada wa daddy komai
Hajiya rukayya tace yauwa yar gari tashi maza kishirya kiyi kama hanya
Suby tace anty Laila zanrakaki
Lailatace shirya muje
Hajiya rukayya tace kuje kawai kubar min yarinyar
Laila tace dama bazamu jeda itaba
****
Laila sukayi sallama a falon mummyn hafsat tana zaune tace a a
Laila kune atafe
Laila tace a mummy Allah yasa daddy na nan
Munzo gurinshi ne
Mummy hafsat idan da sabo tasaba da zuwa Neman daddy agunsu Laila
Mummy tace yanan yanzu zaishigo ya fita sallah ne
Nan su Laila suka zauna zaman jiran daddy
aikuwa daddy shigowa suka gaisa
Yace Lafiya kuwa Laila kokuna bukatar wani abunne
Laila tafada mashi damuwarta nason bin mijinta
Daddy yace wannan ba wani abinda damuwa bane
Kishirya kawai kije kiyi passport agama komai kafin jibi sai kitafi
Laila tace To daddy Allah yakara girma yace Ameen
Ina amaryar tawa
Suby tace tana wajen hajiya
Yace to ace angonta na gaisheta
Nan suka wa mummy sallama suka fita
Daddy ya kalli mummy yace Lafiya kuwa mummyn Hakeem
Mummy tace wallahi alhaji mutanen kotata ban yarda dasuba
Mezaisa tabishi har can yabari mana ai komai daran dadewa zadawo
yanzu haka uwartace ta kitsa mata komai
Daddy yayi murmushi yace insha Allah ba abinda zaisamu Hakeem
Kokin manta Dan naki
Ma abocin riko da addini ne
Dakuma yawaita adduoin tsarin jiki
Mummy tayi murmushi tace hakane daddyn Hakeem
Gaskiya Hakeem kam akwai addua
Sai dai muce Allah yadada tsare mana shi
Daddy yace Ameen
Washagari daddy yagama wa Laila komai nashirin tafiya
Wanda jibi jirginsu zaitashi
Zuwa Saudi
Hajiya rukayya da hajiya suwaiba ne suka sata gaba kan yadda zata yi anfani da magun gunan
dasuka karbo daga gurin malam
Komai Laila ta haddace Dan hartafara hango kanta cikin daula
Washagari jirginsu Laila yadaga zuwa Saudi
Inda tabar meenat 'yarta agurin mahaifiyarta hajiya rukayya
Daddy yadauki waya yakira Abdul Hakeem cikin ladabi Abdul yagaida mahaifin nasa
Daddy yace kashirya kaje airport kadauki matarka
Tana hanya
Cikin mamaki Abdul Hakeem yace Laila kuma daddy
Meyasa zata biyoni har nan
Gaskiya takoma gida kawai Daddy
Daddy yace Haba Dan albarka aure fa ba abin wasa bane
Na kusan shekara bakanan
Ta nemi data zo tagan ka ai baza a hanata bako
Hakeem yace amma daddy
Daddy yace karkace komai ka je airport kadauketa kawai kaji ko
Yace naji daddy Allah yakara Lafiya daddy yace Ameen
Allah yamuku albarka Hakeem yace ameen daddy
Suna gama waya da daddy yace ya Allah
Ahmad yace Lafiya kuwa Man naganka haka
Hakeem yasauke ajiyar zuciya yafada wa Ahmad komai
Ahmad yayi murmushi yace kace nakoma dayan part tunda amarya zata zo
Hakeem dai baice komai ba
Yazauna akan kujera
Karfe hudu dai dai yaje yadauko Laila
Tana ta rawar kai shikuwa Hakeem tunda tagaisheshi ya amsa bakaracewa komai
Wannan shine mafarin zaman Laila a saudiya
Dan bata koma ba
*******
Bayan shekara goma shabiyar
PROFESSOR ABDUL HAKEEM ABUBAKAR
Dan shekara talatindashida aduniya
Cikakken saurayine Wanda ya amsa sunan
THE YOUNG PROFESSOR
ko ina haka akeranshi gida da wajen kasan nan
Yayi suna sosai aduniya saboda kudi da kuma ilimin da Allah yabashi
Har yanzu yanazama a sauddiya ne a inda yake koyarwa a jamiar Saudi Arabian
Dashi da babban abokinshi professor Ahmad
Wanda a yanzu suke shirye shirye komawa kasarsu Nigeria
Laila anzama manyan mata koda wasa bazaka kaga Hakeem kace shine mijinta ba
Ba alamun dacewa a tsakaninsu
HAKEEM bashida rowa koka kadan kudi masu sunan kudi yana cika
Laila dasu
Dan yanzu taza business wuman sosai suke kasuwanci da kanwarta Suby
Idan ta saro kaya a Saudi sai ta tura wa Suby Nigeria
Su duk aganin su Hakeem magani ne yake aiki akansa
Wanda abin bahaka bane dai niyya kawai yayi yake mata abinda yake mata
Amina kuwa agurin hajiya rukayya take sun shaku sosai Dan yarinya dai tayi mugun gado
Shiyasa basa shiri da kakarta mummyn Hakeem Dan tana mata wa azin tabi a hankali kartayi
mugun gado
Yanzu haka ma basa Kaduna suna can kano nan hajiya rukayya takoma Dan mijinta yayi ritaya
sai ya koma garinshi kano
Shiyasa hajiya rukayya tadauki jikarta meenat suka koma can
Yanzu meenat ta Dade a kano
Tana zuwa Hutu Saudi gurin iyayenta
Wannan kenan
KANO
Malam sualaiman yana zaune a wata unguwar talakwa ne dake nan kano
Yana da mata daya da rana biyu
Yaya shamsu shine babba zaikai shekara 36 aduniya
alokacin da umma ta haifi yaya shamsu sai da yashekara ashirin cas
Kafin tasamu cikin asmaullahil husna
Wato asmau kenan
Inda akecemata husnah
Husnah ta taso cikin gata da tattalin uwa Dana uba da kuma Dan uwa rabinjiki wato yaya
shamsu
Tunda aka haifi husnah shamsu ne me dawainiya da ita kasancewar yadade baisamu kani ko
kanwa ba
A yanzu haka husna tasamu scholarship a wani makarantar masu kudi a inda take s s two a
halin yanzu
Husna tana da hankali da nutsuwa ga kuma uwa uba kyau da needed
da Allah ya horemata
Husna yar kimanin shekara shabiyar aduniya
Sun hadu da Amina Abdul Hakeem abubakar
A school lokacin da husna ta samu scholarship tashigo itama Amina alokacin tashigo
makarantar
Amina taso husna Dan Abu guda biyu ne na farko iliminta farinjininta da kuma kyau
Dakyar husnah ta amince wa Amina suka zama kawaye sosai duk inda kaji ance husnah to za
ace amina
Muje zuwa 踫 anfra fa
Fan's kubiyo ummu AFAN
Kawai
Your comments is needed
[30/04, 5:53 PM] UMMU AFAN 潤撕: BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
潤HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
潤GORGEOUS WRITERS FORUM潤
潤G.WF.潤
HOME OF GORGEOUS INTELLIGENT AND EXPERT WRITERS WE ARE THE BEST AMONG
THE REST
潤DEDICATED THIS PAGE TO MY ENTIRE FAMILIES潤
潤AKWAI LOKACI 潤
潤PAGE 36 to 40潤
HUSNA nata saurine saboda tayi latti yau Monday yau ne za a Nada zabin prefect a school
dinsu
Ummu tace husnah naga kina ta sauri yau Lafiya kuwa
Husnah tayi murmushi har dimple dinta suka lotsa tace wallahi ummu yau za a nad'a sabbin
prefect a school ne shiyasa mukeson muje muga wadda za a ba
Yaya shamsu yace kokuma kije a nad'a kuba
Husnah tace aini bandani yaya Dan an min
Interview ma naki bada amsa a hall din
Duk Dan kar abani damuwar nan
Yaya shamsu yace ai duk yadda kikayi sunsani tunda sunsan dalibarsu
Kokinyi shiru sunsan bawai baki sani bane
Tunda dama sunsan bakyaso
Bakince min saki dole akayi kiyi interview din ba
Husnah tace wallahi wani malaminmu ne copper yace lalle sai nayi interview
Kuma duk abinda suka tambayeni Nace I don't no
Komai I don't no kawai
Yaya shamsu yayi dariya yace kedai jekidawo kiban labarin wadda akazaba
Husnah tace to shikenan yaya
Tajuya ta kalli ummanta tace ummu sai na dawo
Ummu tace Allah yadawo dake Lafiya tace ameen umma na
Har takai bakin kofa yaya shamsu yace husnah kiyi hakuri kinji bakudi ajikina yanzu nakeson
zuwa nayi buga buga naga abinda za a samo acigidan
amma namiki alkawari idan nafita nasamu wani abin zana biyo har school dinku
Inbaki Abu mai dadi
Husnah tayi murmushi tace karka damu yaya na wallahi bani da damuwar komai Dan bancika
son cin komai a school ba ma
ai kana kokari yayana Allah yakawo maka aiki maitsoka nasan zamu huta sosai
Yace ameen yar kanwata jeki karkiyi latti
Tafita abinta tana murmushi
Umma ta sauke ajiyar zuciya tace wa yaya shamsu
Kasan wani Abu kuwa shamsu deen yaya shamsu yace a a umma saikin fada
Tace wato akullum na kalleku kaida kanwar ka ina wa Allah godiya daya mallakamin 'ya'ya
nagari
Dan ba abinda zance wa Allah sai godiya kawai
amma duk inda ake neman 'ya'ya nagari nasamu
Abba dayake shirin fitowa daga dakinsa yace munsamu dai zakice zainaba
Tunda Allah yasa shamsu yakawo kwari fa shiyake dawainiyya damu agidan
Shine komai na kanwarsa shine namu aiba abinda zamuce sai muce shima Allah yabashi mai
mishi
Umma tace Ameen malam
Malam sulaima yace babban damuwata shine inga kasamu aiki kayi aure Dan shine cikar
mutuncin mutum
Umma tace hakane ai baki yayi tunda yana da wacce yakeso khadija yarinyar kirki taki kowa
saishi take jira
Ko a yanzu aka tura za ayi komai tunda iyayen ma sun komai
Malam sule yaja numfashi yace hakane kam to Allah yabamu yadda zamuyi
Ya kalli shamsu da tunda suka fara zancen auranshi yashiga duniyar tunani
Dan yana matukar son budurwarshi khadijat wacce akekira da kubra kitama tana son yaya
shamsu sosai Dan
Shekarar ta daya kenan dagama secondary school
Manema sunzo Neman aurenta taki ita sai shamsu
Haka iyayen suka hakura suke zaman jiran shamsu yakawo sadaki a daura aure
Malam sule yakalli shamsu yace karka damu akwai Allah
Shamsu yace barinje Abba sai na dawo ya ma umma ma sallama ya wuce zuwa Neman abinda
zasuci
YAYA SHAMSU daga secondary bai kara gaba ba saboda rashin kudi daya musu katutu shida
mahaifansa
Dan haka kawai ya hakura yake Dan buga bugansa dahaka kuma har Allah yasa aka haifi
kanwarsa husna saiya yaci burin Husna zatayi karatu tunda shi Allah baisa zaiyi mezurfiba
Sai kuma gashi Allah yafara cikawa shamsu burinsa inda husnah taci scholarship
**
Husnah tana isa school tasamu anfara assembly
Ta tsaya daga bayan 'yan mate dinsu suna sauraron jawabi daga bakin principal dinsu
Can sai vice principal yace yace zamufara kiran new prefect dinmu daya bayan daya
Principal tace a fara da head girl ko
Sai copper bash yace am sorry ma
Gwamma afara da sauran kafin head girl
Zaifi Jan ra ayin su
Principal tace OK afara kira kawai
Nan akafara kiransu ana samusu hula da kuma belt
Dansu prefect din hula suke sawa green gabadayansu na head girl ce kawai ya banbanta Dan
nata read cap take sawa
Can taji ance social prefect AMINA HAKEEM ABUBBAKAR
Nan aka dau tafi raf raf raf ana murna
Can sai vice principal yayi gyaran murya yace yanzu zamu Kira me gayya me aiki wato our
head girl
Nan aka kira sunan ASMAU SULAIMAN SHAMSU
cikin gigicewa Husnah tadago kanta aikuwa tana dogowa sukayi ido hudu da Copper bashir
Ya kashe mata ido daya
Cikin tashin hankali Husnah ta daga kafa dakyar tana zuwa ta hau kan stage
Principal ta rungume Husnah tare da
Da samata hulan head girl dinta read cap
Ta daura mata belt dinta read shima
aikuwa daga students har malaman dake wajen aka dautafi Dan sunburge kowa ga read cap
din yawa Husnah kyau sosai kaman Dan ita akayi hulan
Nan dai aka rantsar dasu Husnah a matsayin new prefect
***
Copper Bash ya tsare Husnah alokacin dazata wuce gida itada meenat
Copper bash yace asmau
Ya naga kina ta shan kamshi ne Yau
Meenat tafashe da dariya
Tace uncle ai Husnah fa batasan za abata prefect ba ballantana Head girl
Copper bash yayi murmushi yace ai kuwa ta yaudari kanta
To inba a bata ba waza aba wa
Meenat tace aifa dai kam
Husnah dai tana jin su batace komaiba
Nan driver din meenat yazo daukarta
Husnah kuma dama da kafa take zuwa take komawa
Meenat tace Dan Allah Husnah kizo musaukeki a gidan kinga sai naga gidanku ko
Husnah tayi murmushi dimple dinta suka lotsa
Copper bash ya tsaya kawai yana kallon Husnah komai nata cikin aji takeyinsa da nutsuwa
shiyasa takeda farinjini a school din
Husnah tace wallahi meenat idan ya shamsu ya ganni a mota zai min fada sosai .
Meenat tace kedai kawai bakyason kibimu sai kiyi tayiwa yaya shamsu sharri
Copper bash yace kinga kuyi sauri kutafi gida kar anemeku kuntsaya surutu
Meenat tace to shikenan sai mun hadu goben idan munzo ko
Husnah tace to meenat Allah yakaimu kigaida gidan
Nan sukayi sallama
Copper bash yace wa Husnah muje nakaiki gida da kaina
Tunda kinki kawarki takaiki
Husnah tace Dan Allah uncle kayi hakuri wallahi yayana yaganni da kai zaimin fada
Copper bash yace mezaisa yamiki fada baki kai a rakakin bane ko yaya
Husnah tayi shiru tace kayi hakuri Dan Allah
Yace wato har yanzu Husnah kinkasa yarda da sonda nake miki ko
Kibani dama nasan gidanku da iyayenki wallahi dagaske nake auranki zanyi Asmau
Husnah tace Dan Allah malam kayi hakuri kar yaya yasan da wannan maganar
Dan ya hanani kula koda kawace ballantana
Maganar soyayya tun yanzu
Da kyar yabani dama kawance da mina Hakeem ma
Copper bash yace OK na fahinceki
Ba wai nidinne bakyaso ba umarnin yayanki kikebi ko
Husnah ta rufe ido tana murmushi tayi hanyar fita daga gate din school din
Copper bash yayi murmushi tunda ya gano yafara shiga zuciyar Husnah
Zaisan hanyar da zaibi Dan yasan iyayenta da yayanta shamsu
Bashir Dan wani hamshakin maikudi ne sosai acikin garin kano
Bautar kasa wato NYSC yakaishi school dinsu Husnah
Tunda yadora idonshi kan Husna yaji yakamu da son ta
amma takibashi daman hakan
Next page
[05/05, 11:05 AM] UMMU AFAN 潤撕:
潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
潤HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN 潤
潤撕潤撕FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION潤撕潤撕
潤撕F.C.T.W.A潤撕
潤撕HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION潤撕
潤DEDICATE THIS PAGE TO UMMY 踫 KINA KOKARI WAJEN GANIN NOVELS DINA SUNA
KARBUWA A KOWANI GROUP ALLAH YABAR KAUNA 踫踫踫踫踫
潤AKWAI LOKACI潤
潤PAGE 41 to 45 潤
ABDUL HAKEEM THE YOUNG PROFESSOR
kwannansu biyu da dawowa daga saudiya dashi da madam laila
HAKEEM yana shirin zuwa sashen iyayensa ne don yagaishesu
Yafito daga wanka ne yashirya cikin wani farisol din jallabiya ya faffesa turarruka masu kamshi
Dan akwaishi da son kamshi sosai
Har yagama shiransa zaifita Laila bata tashiba
Ya kalleta kawai ya girgiza kai yayi gaba abinsa zuwa part din su mummynshi