Author : Ummu Afan Category : Arewa Hausa Novels
Yanashiga yasamesu akan dining da mummy da daddy
Daddy yace Dan halal kaki anbato yanzu nace baka shigo break fast ba mummyn ka tace ai
tasan kana hanya
HAKEEM yayi murmushi cike da kaunar iyayensa
Yace ai mummy tafadi gaskiya Dan bazan taba karyawa a wani waje ba matukar muna tare da
mummy
Mummy tace yauwa son fada mishi dai
Nan mummy tayi serving din HAKEEM abinci yafara ci
Bayan sungama break fast ne mummy zata kwashe kwanukan Hakeem yace haba daliba
yazakimin haka kuma
Kezaki kwashe kayan zuwa kitchen nikuma meye anfani na
Mummy hafsat tace nabari tashi ka kawashe
Daddy dai dariya yake musu yakoma kujerar falo yazauna
Hakeem bayan yagama kwashe kwanukan zuwa kitchen saiya dawo falo Dan hira da iyayen
nasa
Daddy yace wai acikin makarantu biyu dasuke bukatarka wanne kazaba kayi lecturing din agun
HAKEEM yayi murmushi yace ai daddy daga ni har Ahmad munzabi muje BUK kano
Daddy yace Allah yasa haka shine alkairi
Mummy hafsat tace amin
Daddy yace kace kuna tare da amaryata kenan
Mummy hafsat tayi murmushi tace MEENAT ko rigima
Yakama ta ma suturota tazo tagaida iyayenta ai
Daddy yace karkice komai tunda basuyi hakan ba shi saiyaje yaganta
Kafin Hakeem yayi magana wayar daddy yadau kara
Daddy yadaga sai sukaga daddy yace subuhanallla a wani asubiti
Mummy da Hakeem suka maida kallonsu kan daddy
Bayan daddy yakashe wayar ne suka tambayeshi abinda kefaruwa
Yace Abba na aka kai hospital
HAkeem yace subuhanalla muje kawai daddy
Mummy hafsat tace nima bazaku barniba muje tare
Suka he asibitin Hakeem ne me driving dinsu
Suna isa suka sami alhaji shuaib bayadda yakara ji
Dan yanajin jiki sosai
Alhaji shuaib yarike hanun Dan nashi wato daddy
Yace Allah yamaka albarka abubakar da kai da zuriarka
Ba abin da zance dakai sai Allah yàmaka sakayya da gidan aljanna duk inda akeneman yaro
nagari ka kai abubakar
Ya kamo hanun Hakeem yace jikallena ga mahaifinka nan nabar maka amanarshi duniya da
lahira
Kabishi kamar yadda yabini
Ya kalli mummy hafsat yace kema Hafsatu Allah shizai biyaki akan yadda kika nuna kaunarki ga
abubakar
Duk yadda aka kai cutar dashi kinki bada damar hakan
Allah yamiki albarka
Tunda alhaji shuaib yafara magana suke kuka musamman daddyn Hakeem
Da mummy
ABDUL HAKEEM ne kawai ya daure amma shima idonshi yayi ja sosai
Can dai likitoci sukace sufita zasu samishi
Oxygen Dan numfashinsa yafara kasa
Alhaji abubakar ne kawai akabari a dakin
Can wajen La asar 'yan kano suka iso asibitin
Kuma harda meenat
Hajiya rukayya itama a rikice tazo jincewa jikin mahaifin nasu ya tashi
amma anhanata shiga taganshi
Hakan kuma ya bata mata rai sosai
Amina kuwa tana ganin daddynta Hakeem tare da mummynshi takarasa wajensu cike da
murnar ganin uban nata
Bayan tagaida Hakeem ne take tambayarsa dad ina mummyna yace tana gida yanzu zata zo
itama
Amina ta kalli mummy hafsat tace wato ma bazaki kimin magana ba ko
Mummy hafsat tace kaga jaira kinga babanki bakima San ina wajenba zaki ce ban miki
maganaba
Sannu uwata mummy hafsat takarasa maganar tana tsokanarta
Amina tace ai wallahi duk abin kidai saina auri mijinki sai naga yadda zakiyi
Mummy hafsat tayi murmushi tace kishigo mana kigani da tabarya zan koraki ai nan mummy
Hafsat tana jikinta ajiki sukata Dan hirarsu amma cikin jimamin rashin lafiyar alhaji shuaib
Ahmad yakaraso hospital din shima cikin jimami
Hakeem na ganin Ahmad yace Man ka karaso kenan
Ahmad yace ai kana kirana nace wa mummy zanzo hospital namata bayani
Itama zasu zo tanason gama abincine sai ta taho dashi
Hakeem yace Allah yakawota Lafiya
Ahmad yace barinje na gaida su mummy suka karasa harwajensu mummy
Yagaishesu yamusu ya maijiki
Amina tace daddy Ahmad ina wuni yace Lafiya qalau daughter ya mummyn ki
Tace banganta ba mu yanzu mukazo daga kano
Kafin Ahmad yayi magana daddyn Hakeem yafito daga dakin yana goge hawaye
Hakeem da Ahmad suka karasa dasauri Hakeem yace daddy yajikin alhajin
Daddy abubakar yace Hakeem Allah ya yi wa mahaifina rusuwa
Alhaji yatafi yabarni Hakeem
Yanzu bani dakowa dama bansan mahaifiyata ba shikadaine min aduniya
Shima yatafi
Duk matan dake gun sukasa kuka
******
Bayan arbain din alhaji shuaib
ABDUL HAKEEM da aminin sa suka fara lecturing B U K
Dan karakaran gidaje makaranta tabasu a matsayinsu na professional akan aikin su
Yanzu Haka suna shirye shiryen auran Ahmad kuma a kano zaitare da matarsa
Itakuma Laila tayi tayi yabarta tadawo kano yaki
Sai dai yazo masu Hutu yakoma
Yanzu haka bikin Ahmad saura sati biyu cas a daura auren Ahmad
*****
Yaya shamsu zaune akan kujera yar tsugune umma kuma na hada zobo Dan duku gidan suna
azumin Monday da alhamis
Itakuma Husnah tana kan hada musu abincin buda baki a kitchen
Kanin kubra budurwar yaya shamsu ne yayi sallma yashigo ya tire
Ya gaisheda umma kafin ya ajiye abincin yace yaya shamsu gashi anty kubra
Kafin shamsu yayi magana umma
Tadauko naira hamsin tace zoka karba ko kace mata angode Allah yasaka da alkairi
Yaron yaki karbar kudin umma yaya shamsu yace haba kanina karba mana ai ba roka kayiba
Yakarba yayi godiya zaifita kenan
Husnah ta tace sani kace wa anty kubra gobe zanzo kitso
Sani kanin kubra yace to zanfada mata
Umma tace kajita kaman wani kitson takeso
Yanzu zatace maka zata kitso taje tadawo da kalba
Husnah tayi murmushi tace umma wallahi banason kitso nafison dai amin kalban kawai
Tagama kwashe komai ta ajiye musu akan taburma
Jelouf din taliya ta musu Wanda ya shamsu yakawo dazu yace a dafa yasan tana son taliya
sosai
Umma tace wallahi yarinyar nan kubra akwai kokari
Bata gajiya da aiko maka da abinci duk Monday da alhamis
Husnah tace gaskiya kam wallahi anty kubra Nada kirki
Yaya shamsu Allah yabaka kudi wannan sallar dai kasamu kamata kayan sallah
Umma tace amin gaskiya kam ta cancan hakan
Shamsu yaja numfashi yace kuma wallahi umma kubra bata jin dadin gidansu
Indai ba abbanta yana gidaba
Kishiyar mamanta tana matsa mata sosai
Yanzu fa wai akwai Wanda yamata magana yanson kubra shine tadage sai kubra ta amince da
auran wani baniba
Dan taki amincewa shine take bata wahala
Kuma abbanta yace bazai mata auren doleba
Sai Wanda takeso zaibata
Shine tayi bakin jini agidan
Umma tace Allah sarki marainiyar Allah
Allah yabaka abinda zaka auro yarinyar nan karabata da gidan nan
Shamsu yace amin umma
Husnah ma tace amin
Yaya shamsu yace barinje sallar magriba indawo muyi buda baki
Shamsu yana fita Husnah tace wallahi ummu yaya shamsu yana bani tausayi
Dan wallahi shima yana son kubra sosai
Umma tace bakomai AKWA LOKACI
watarana sai labari Husnah tace Allah yanuna mana lokacin amin ummu tace
Suma tashi sukayi Dan gabatar da sallah
**
Bayan kwana biyu wani abokin shamsu yabashi
Shawarar mezaihana yakai takardunsa Neman aiki B U K koda masinja aka bashi zai rage zafi
ai
Shamsu yace gaskiya naji dadin shawarar nan daka bani kabiru
Allah yabar zumunci
Kabiru yace bakomai ai zaman taren kenan
Kaga ni a secondary school nake masinja amma alhamdulilla ina samu
Ya shamsu yace hakane yanzu zanyi wanka nakai kuwa
Bayan ya shamsu yashirya zuwa kai application dinsa
Saiya wa umma sallama Yakama hanya
Bayan yakai akace za anemeshi idan yasamu idan kuma baisamuba zaiji shiru
Yabasu number dinsa
Yatafi gida yana ta aduar samun nasara
Idan Allah yasa yasamu aikin nan zaiyi kokarin raba kubra da gidansu tazo suyita maneji
yasan kubra zatayi hakuri da abinda zaibata umma kuma bata da matsala zasu zauna Lafiya
*****
Professor Abdul Hakeem zaune a office dinsa yana duba wasu takardu sai wata mata tashigo
tagisheshi
Tace wai itace sabuwar sakatariyarsa
Abdul Hakeem yace OK zaki iya tafiya sai na nemeki
Tafita
Tana fita Hakeem yakira management din makarantar
Suna ganin wayar office dinsa
Aka je dasauri Dan yanakirane
Manager nashiga yagaishe da professor Hakeem
Hakeem yace ina buka tar a canza min secretary ma ana bayason mace
Namiji yakeso akawo mishi
Manager yace angama sir
Hakeem yabashi izinin tafiya
Sukaje suka zauna meeting
Nan akayi shawarar daukar SHAMSUNDEEN SULAIMAN a matsayin secretary na THE
YOUNG PROFESSOR ABDUL HAKEEM
Yaya shamsu yana kofar gidansu kubra yaje zance
Sai yaga kira da bakuwar number
Yayi picking call din
aikuwa kubra taga yana ta fara a yana godiya
Bayan ya kashe wayar ne
Ya kalli kubra yace kiyimana murna munsami aiki kinga kenan burinmu yakusa cikako
Cikin tsananin farinciki kubra tace alhamdulillahi
Gobe zafara azumina kenan
Da mamaki shamsu ya kalli kubra yace azumin mekuma zakiyi
Kubra tayi murmushi tace aina wa Allah alkawarin cewa duk randa kasamu aiki sainayi azumi
uku cas
Shamsu yace aikuwa bazakiyi kekadaiba tare zamuyi
Nan dai yamata sallama ya wuce gida Dan yasanar wa umma
**
Umma tayi farinciki sosai haka ma mahaifinsa
Husnah kuwa tsalle taringa yi tana murnar ankusa kawo musu anty kubra gidansu
Mahaifinsa yace gobe zaka fara zuwa kenan
Yaya shamsu yace a daga gobe sukace wai karfe takwas zandinga zuwa
Sainaje ma zasubani dokokinsu
Nan iyayen sukayi ta albarka
Washagari yaya shamsu yashirya zuwa wajen aiki
Bayan yayi sallama da su umma
Ya wuce gidansu kubra itama tamishi adawo Lafiya
Yana isa aka gama komai aka turashi office din PROFESSOR HAKEEM
yana zuwa yayi nocking akace yashiga
Professor Hakeem yanakan kujerar shi yana fama da wasu takardu
Shamsu yashiga yagaisheshi professor Hakeem ya amsa batare da kalleshiba
Yace ta akayi malam
Shamsu yace daman nine sabon secretary din da aka turo office dinka
Professor Hakeem yace OK dafatan zamuyi da gaskiya malam
Shamsu insha Allah sir
Sai alokacin professor Hakeem yadago kai ya kalli ya shamsu
Yace ko zan iya sanin sunan malamin
Yaya shamsu yayi murmushi yace Shamsuddeen
Hakeem yace malam shamsu Allah yatayaka riko za iya tafiya
Shamsu yayi godiya yace nagode sir
Ya wuce abinshi professor Hakeem yacigaba da aikinsa
Can wajen shabiyu da rabi professor Ahmad yashigo office din Hakeem yace ya man muje muyi
lunch kasanfa bana jure yunwa
Hakeem yayi murmushi yace wai damma ka kusa shiga daga ciki
Aisha Nada aiki wallahi sai dai ta ringa samaka wani flask
Ahmad yayi dariya yace ai dani dakai duk jirgi daya yakwàso mu
Nan dai Hakeem ya tattara suka fito tare Hakeem yakalli shamsu dake kan kurarshi yace
Abokina zamufita ga key din office din take care
Shamsu OK adawo Lafiya
Suna zaune a gurin cin abinci Ahmad yace waini wannan Dan gayun ne sakatarenka
Hakeem yace kaima kaji mamaki ko
Da naso namishi tambayoyi sai naga rashin dacewar hakan gwamma nagama fahimtarshi kafin
Naji tarihinsa
Ahmad yace hakan ma yayi
amma mutum very responsible person kaman wannan ace yana sakatare
Shamsu yashiga office din maigidan nashi yaga kudi a kasa
Ya dauka ya ajeye mishi a saman tebur
Bayan su Hakeem sundawo yashiga office din sa
Sai ya kalli inda ya zubar da kudi yaga babusu
Dan dama da gangan yayi hakan Dan ya gwada shamsu ne kawai
Yazauna akan kujerarshi aikuwa idonshi yakai kan kudinshi da shamsu ya ajiye mashi su
Professor Hakeem yayi murmushi akaro na farko
Yaya shamsu yashiga ranshi
Karfe hudu dai dai Hakeem yatashi a office dayafito yaga kujerar da shamsu yake yaga yana
waya ne amma yanaganin fitowar Hakeem yawa kubra sallama
Hakeem yayi murmushi yace hala kaida uwargida kuke wayar kuma ka kashe
Yaya shamsu baice komai ba sai murmushi kawai
Hakeem yace natashi kaima zaka iya tafiya
Shamsu yace aisunce wai sai time din tashi yayi zantashi
Hakeem yace no zan musu magana kaje kawai abinka
Hakeem har yayi gaba ya dawo yace sunbaka kudi kuwa
Ya shamsu yace wani kudi kuma nida nafara aiki yau sir yakarasa yana murmushi
Hakeem yayi murmushi yace yakamata subaka kudin daukar aiki
amma zanbaka aro idan anbaka sai ka dawo mundasu ko
Ya shamsu yayi dariya kabarshi kawai sir kar azo basu baniba
Hakeem yayi murmushi yace idan basu baka na barma
Kuma banason musu yashiga tsakaninmu malam shamsu ka karba kawai karmuyi haka dakai
Shamsu yakarba yace nagode yallabai
Yace karka damu
Sai gobe kayi kokari ka koma gida
Shamsu yasake baki kawai yana kallon Hakeem
Yaduba damin kudin da Hakeem yabashi
Nan dai yayi wa Allah godiya cike da farinciki shamsu ya kulle kofar office din su
Yayi gida
Yana zuwa Husnah ta tareshi da murna oyoyo yaya na sannu da dawowa
Shamsu yayi dariya yace yauwa yar kanwata ina umma
Ummu ta fito daga daki tana daura dankwali tace a a dawuri haka
Yaya shamsu yace wallahi Allah ne ya hadani da shugaba nagari yace karfe hudu ma ina iya
tafiya
Umma ta ce alhamdulilla ai haka akeso
Yaya shamsu yace umma ina Abba tace yanzu zaishigo sunje gaisuwar Mara Lafiya shida
malam tanko
Kafin tarufe baki ma sai ga Abba yayi sallama yace a a Dan albarka har andawo
Nan suka zauna kan ta Burma yafito da kudin ya ajiye gaban mahaifinsa
Nan yamusu bayanin komai
Abba yayi gyaran murya yace to yanzu idan akazo ba a baka kudin daukan aikin bafa
Ya shamsu yace nima haka nagani dai
Na nuna yabar kudinsa kawai yace aishi yabani
Umma tace to kaidai duk inda kake ka tabbatar karike gaskiya kazauna da kowa zuciyarka daya
Ya shamsu yace insha Allah
Zankiyaye
Nan dai Abba da umma sukace baza a taba kudinba harsai
anbaka angani koba hakaba yaya shamsu yace hakan ma yayi gaskiya
Husnah tace Abba kawai da yaya shamsu yayi anfani da kudin gurin kai sadakin anty kubra
Koba a bashi tunda yana aiki saiya biyashi a hankali
Abba yayi murmushi yace uwatakenan ke yarinyace har yanzu bakisan duniyaba
Indai aure ne ai zaiyi insha Allah
Suka ce Allah yasa
Bayan kwana biyu ranar alhamis ya shamsu yaje wurin aiki aka kirashi akabashi kudin daukar
aiki naira dubu goma shabiyar
Da yadaqo gida yace wa ma haifinsa ambashi yanuna musu
Abba yace alhamdulilla kaga gobe saika mayar mashi da kudinsa
Allah yayi albarka ya shamsu yace ameen Abba
Abba yace yakabar kudin kuma anan
Ya shamsu yace Abba kayi abinda yadace kawai
Abba yace wa umma tadebi kudin ta ajiye agunta
Washagari ya shamsu yasami professor Hakeem a office yamishi bayani yamayar mashi da
kudinsa
Hakeem shi har ya manta ma yaba wa ya shamsu kudi
Ba karamin burgeshi ya shamsu yayi ba
Yace
Gashi kasiya wa yara sweet
Ya shamsu yayi dariya yace ai banida aure
Hakeem yakalleshi yace
Malam shamsu idan bazaka damu zanso jin labarinka
Next page
Your comments is needed
Fan's
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
F.C.T.W.A
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION
DEDICATE THIS PAGE TO UMMU HANIF