Author : Ummu Afan Category : Arewa Hausa Novels
Zama yayi kasan shima yana fuskantarta
kasa dagowa tayi saboda kunyarshi gashi itadai bawani sonshi take ba
Yace tunda nibaza a gaisheniba nibarin gaisheda my wife
Dafatan kin wuni lafiya kasa amsawa tayi
Yace koki amsa gaisuwata konasa hanu na dago da fuskarki
aikuwa bashiri tadago tace cikin shagwabbiyar murya tace kayi hakuri karka tabani ina wuni
Professor Hakeem yayi matukar kaduwa jin wanann murya na husnah
Gawani masifaffan kyau tamishi
Kayan data sa ajikinta kaman Dan ita akayisu
Prof jiyayi kaman ya rungumeta a kirjinsa kozai zamu saukin sha'awar data taso mishi lokaci
daya
Husnah ganin hanun Prof kawai tayi yadanki hanunta
Cikin tashin hankali husnah tabi hanunshi da kallo
Yace baby kinsan damuwata wallahi kece ina matukar son kasacewa dake amatsayin mata
amma haryanzu bansan matsayina ba agurinki
Husnah tace zanfada maka amman saika sake min hanu
Hakeem yayi murmushi yace shike nan inajinki
Husnah tafara magana tace na'amince zan aurekà amma bana jin zaka sàmi soyayyata Dan
nariga nagama soyayya a rayuwatà Dan ni kwata kwatà soyayya bai karbeniba
Kar sàinafara sonka kaima narasàka
Takarasa maganar da kuka mecin rai
Hakeem jiyayi kukan har cikin ranshi yadauko hand kacif a aljihunsa fari Sol yasha kamshi
yamika mata
aikuwa ganin hankacif din nan saiyada ta girgiza
Ta karba dasauri tace Dan Allah yaya a ina kasamu wannan hand kacif din
Hakeem yace nawane kokina sone cikin sauri tadaga kai tace Dan Allah kabarmin wallahi irin
Wanda ya muallim yake amfani dashine
Koranar da zamu rabuma shine a hanunshi
Takarasa maganar hawaye mai tsanani Hakeem yace banason kukan nan kigoge fuska kimin
magana Wanda yamutu ai yamutu
Husnah tayi murmushin data kumatunta lotsawa sosai
Tace aikuwa sai dai kayi hakuri Dan har abada bazan daina tunaninshi ba saboda yatafi da
zuciyata gabadaya
Hakeem yaji matukar jintausayinta kaman yarungumeta ya rarrasheta
Husnah tacigaba da bashi labarin soyayyarta
Akan bashir da abinda yayi mata bayan tadauki zuciyarta tabashi lokaci kawai akejira ayi biki
amma yafasa
Kuma yakoma suna soyayya da babbar kawarta
Sannan takarabashi labarin masoyin asali ya muallim
Hakeem yace nikuma na godewa Allah nakuma godewa saurayinki dayace yafasa
Dan da befasaba danayi asarar zukekiyar yarinya kamarki
Kinga kuwa nidan gatan Allah
Akaro nabiyu yasake kama hanun Husnah yace please baby kiyarda dani
Yakura mata ido tace naji amince amma kasake min hanu Dan Allah bakyau fa
Hakeem yace nasani baby shiyasa nakeson abanike a matsayin mata saboda banason
nacigaba da sabawa Allah taba jikinki batareda aure ba
Because I can't control my self in front of baby
Husnah ta tabbatar dagaske yakeyi
Tayi murmushi bara maka ruwa da lemu
Yaji dadi har ranshi data nuna kulawar ta agareshi
Murmushi kawai yayi tare da 'daga mata gira ta tashi zata je sai kuma taga idonshi akanta
Ta juyo a shagwabe please yaya kajuya kadaina kallona inbasokake nafadiba
Maganar yaba Hakeem dariya yace jeki na rufe idon
Da gudu kuwa tafita yabi bayanta da kallo
Sai yatuna da ranar dayazo amatsayin ustaz
Zataje dauko masa kudi wai sai yarufe idonsa
Murmushi kawai yayi shikadai
Tare da zaro wayarsa daga aljihunsa
Sallama tayi da tire a hanunta dauke da abinci ta ajiye gabansa
Hakeem yaganta cikin wata jibgegen hijabi abin yaso bashi dariya ma
Kar dai ace tagane abinda yake kallo
Sai yayi murmushi kawai
Husnah tace ga abinci yaya
Hakeem yace nakoshi
Husnah takalleshi tace saboda me
Hakeem yace saikin fada dalilin ki nasaka min hijabi daga shiganki dauko min ruwa
Husnah tayi murmushi kawai
Tace sanyi nakeji tafada tareda boye kanta cikin hibinta
Hakeem yace baby
husnah tadago batareda ta amsa ba
Yace cire hijabin nan kizo ki serving dina
Husnah ta marairai ce kaman zatayi kuka tace Dan Allah kayi hakuri yaya wallahi kunyarka
nakeji
Prof ya tsareta da maya tattun idonshi masu kwarjini
Yace OK kinfison acire miki da kauna ko
Husnah tayi saurin girgiza kai
Yace OK do as I said cikin sanyin jiki husnah tacire hijabin ta ajiye kan kujera tasauko kasa ta
Samishi abinci
Prof ya gyara zama yafara cin abincin tareda tsareta da ido
Duk kallonshi yasa ta takura
Yace batayi tsanmani ba taka spoon din a hanyar bakinta
Tadago ido takalleshi ya daga mata gira
Tace azumi nake yi
Yau Wednesday dama ana azumin nafila
Husnah tace wallahi Nina koshi cikina ma kaman zafashe
Yace tunda yayi niyar bata tabude baki kawai yasamata
Bata da zabi haka tabude Dan karamin bakinta yasaka mata
Yanayin yadda take cin abincin nata ma kawai abin kallone
Yatsaya kawai yana kallon ikon Allah
Yace bude bakin nagani
Tayi saurin cewa na am da karfi
Tace inazuwa umma nakirana ta tashi tagudu abinta
Hakeem murmushi yayi kawai yagama cin abincinsa yafita yashamsu yace har zaka gudu
Hakeem yace a nayi bakine
Shine zanje nagansu
Ya shamsu yarakashi har gurin mota
Prof yakira megadi yabashi manyan lodoji yashiga dasu gida
Ya shamsu yace yallabai Dan Allah karage kashe mata kudi haka sunyi yawa karka manta fa
yarinyace Husnah har yanzu bata gama sanin kantaba
Prof yayi murmushi yace karkadamu itama ai hakkinace so konawa zankashe mata basuyi
yawaba
Karka damu ya shamsu
Nagode da kulawarka
Yashige mota yayi gaba
Yabar ya shamsu da tunanin irin karamcin na PROFESSOR HAKEEM
****
Meenat sun wuce honey moon itada agonta bashir a inda zasu zaga kasashe sama da biyar
Shiyasa ma suke saran sai nan da 5 months zasu dawo Nigeria
Dadddyn Hakeem da shi dawasu amin tattun abokansa sukaje nemawa ABDUL HAKEEM
ABUBAKAR SHUAIB
Auran ASMAU SULAIMAN SHAMSU
Sun bada sadakin husnah da zinare Wanda akalla zai kai million daya da rabi
Abba da ya shamsu suka suka kikarba
Daddyn Hakeem yanuna rashin jindadin shi
Sai su Abba suka karba tare da wa abin albarka
Nan daddyn Hakeem yace yana Neman alfarmar asaka auran nan da two Weeks
Next page
Your comments is needed Fan's
Ina alfahari daku masoyana ❤❤❤❤❤❤
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Story & written
By
The special writer
UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
(F.C.T.W.A)
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION
I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SIS NERFEESERT A MUSA
INA MATUKAR JIN DADIN YADDA KIKE COMMENTS DINKI DAFATAN ZAKI CI GABA DA
SUBURBUDO COMMENTS
KEEP IT UP
AKWAI LOKACI
PAGE 91 to 95
PROF zaune cikin falonshi na gidansu yanawa da Ahmad madam Laila tazo tazauna kusa da
shi fuska a kode
Tace ina da magana fa baban meenat
Hakeem yakalleta da nutsuwa yace ina sauraronki maman meenat
Laila tadago kanta ta kalleshi Dan taga kaman yau akwai abin arziki
Sai tadauko ko kwalliyar da tayi ne ta burgeshi
aikuwa sai tasake wani shagwabe fuska wai ita zatayi shagwaba
Abin yaso ba Prof dariya amma sai ya make
Tace daman inason wasu kudine Dan Allah
Hakeem yayi murmushi tare da kurban copee dinshi
Yace kaman nawa kike bukata uwargida rangida idan bake bagida
aikuwa kanta yasake fashewa
Tayi dariya tace kuma daga ni bawata nice amarya nice uwargida
Saboda dariya Hakeem har kwarewa yayi
Ya ajiye coffee din yana murmushi Wanda yake karawa kyakkyawar fuskarshi kyau
Yace Allah ko tace sosai
Yace nawa kike bukata kenan
Tace million biyu Hakeem ya kalleta yace sun isheki
Laila tankalleshi da mamaki
Sai dai kuma tabasar tace a idan zansamu kari ma aizankarba
Yace OK yatashi yaje dakinsa yadauko cheque yarubuta naira million biyar
Yabata aikuwa madam laila data karba taga abinda keciki
Kusan suman zaune tayi agun
Sosai takasa control din kanta
A take ta dau waya takira hajiya rukayya tafada mata kudin da hakeem yabata
Tsaban batan basira irin nasu daga uwa har 'yar suka hau murna
Ta ma mance agaban Prof take da mamaki Hakeem yake kallonta
Kuma godiya haka ta tashi zata fita
Hakeem yace baki jiba zokizauna
Baki tambayeni kudin menene ba
Laila tace aina sani tunda Nina tambayeka kuma ka nunka min fin abinda na tambayeka
Hakeem yace OK wannan kudi kiyi amfani dasu ne naki
Dan nan da two weeks za a daura min aure
Kinga saiki sai abinda kike bukata ko
wani wawan ihu tafashe dashi
Tacire Dan kwali ta yar tace cikin tsananin tashin hankali tace wallahi Abdul baka isa ka cimin
mutunci ba kayi kadan
Kuma wallahi banga 'yar iskar data isa nayi kishi da ita
Wani wawan kallo Hakeem wa watsa mata
Yadawo PROFESSOR ABDUL HAKEEM dinsa data sani yace karkisake kiran matata da 'yar
iska if not zan baki mamaki
aikuwa Laila ta tafa hanu tace auwa harma tazama matar taka to wallahi Baku isaba
Kodayake kaima ba yinkanka bane duk abinda kakeyi saka akeyi
aikuwa tawuce fuuuuuuuuuuu tayi hanyar part din mummy hafsat
Hakeem daya kai cup din coffee baki ganin tafita ya ajiye coffee din
Yace tashin hankali badai matar nan gurin mummy na zata ba
aikuwa yatashi yazare belt din jikinsa yayi part din mummy hafsat
Mummy tana zaune tana waya da hajiyar Ahmad suna shirya yadda zasu tsara komai kafin
bikin ganin Laila tashigo a fusace yasa mummy hafsat tace zankiraki hajiya
Laila ta tsaya agaban mummy hafsat tana girgiza jiki
Mummy hafsat tace ke lafiyar ki kuwa zakizo kitsaya kina girgiza
Laila tace burin ki yacika sai dai ina son kisani wallahi ba aisa akawo min wata 'yar iska gidaba
Nidaman nadade dasanin bakya kaunata kuma wallahi ba yadda kika iya dani
Mummy sake baki kawai tayi tana kallonta
Zata sake wata maganar taji belt ta kota ina ajikinta
Hakeem ne sosai yake sauke mata belt din nan ajiki
Mummy hafsat tashiga tsakani tace barta haka son
Yace mummy kibarni na babballata hartana da gost dazata sameki tana miki rashin kunya Who
is she by the way
To bari kiji bazan dauki raini ba ballanta na ki ma mummy na wacce bani da kaman su aduniya
Kekinsan zamana dake ma ai darajarsu kike ci Dan ubanki
To kije nasakeki kuma yanzu zaki bar gidan nan nonsense '""
Ya kalli mummyn shi yace mummy Dan Allah kiyafemin wallahi nayi da nasanin hada zuria da
hajiya rukayya
Bantaba tunanin zan ajiye matar da zata iya miki abinda Laila tamiki yanzu ba
Mummy tace kayya son kayi sauri da baka saketa ba
aiko wace mata da irin nata kishin idan mijinta yazo mata da zancen Karin aure
amma ni baka min komai ba hasali ma kanuna min kai d'ane Allah yamaka albarka
Tajuya ta kalli Laila dake kurma ihu tana kuka kaman ranta zai fita
Mummy tace kekuma tunda rayuwa da kika zaba wa kanki kenan aishikenan
Mummy ta wuce abinta Hakeem shima komawa sashinsa yayi nan da Laila ta dauko waya
tafashe da kuka hajiya rukayya ta rude tace ke lafiya kike kuka waya mutu
Laila tafada mata abinda kefaruwa
aikuwa itama hajiya rukayyar kusan haukar tayi
Tace ba inda zakije ganin nan zuwa kadunan shidin banza share hawayanki
Kekadaice a gidan mijinki
Kwantar da hankalinki ganin ta howa
Alhaji abubakar daddyn Hakeem yana hanyar dawowa daga office
Hajiya rukayya takira wayarshi tana kuka
Daddyn Hakeem yayi tafada mishi abinda abinda kefaruwa
Daddyn Hakeem yace Abu baiyi kyau ba ammanshima yanzu zaikoma gidan
Tace itama gatanan a hanyar zuwa yace Allah yakawoki lafiya
Ya kashe wayar yacigaba da tukinsa
Hajiya rukayya nazuwa sai da tabi tacan gidansu ta taho da uwarta itama wato hajiya suwaiba
sukazo tare
Laila na zaune tana jiran hajiya rukayya suby kanwarta tuntuni tazo suke zaman jimami tare
Karasowar kowa da kowa aka hadu a falon daddyn Hakeem
Tunda daga kan hajiya suwaiba mummy hafsat hajiya rukayya Laila suby da kuma uban gayya
ABDUL HAKEEM suna zaune gaba dayansu
Daddyn Hakeem yafara gaida hajiya suwaiba tunda itace uwa agaresu bakidaya
Kafin yagaida yayarsa hajiya rukayya
Daga nan kuma yabukaci yasan abinda kefaruwa
Hajiya rukayya tafara magana cike da zafin zuciya
Tace bantaba tunanin abinda wannan yaro zaimana bakenan ya suna zamansu lafiya da
matarsa
Za azuga shi yayi aure wannan ma ai Neman tashin hankali ne
Kuma abin batsaya nan ba sai su hadu shida uwarshi sun mata duka
Sannan kuma tabashi umarnin ya saketa saboda bakin hali da akasha a nono
Ran Hakeem tafarfasa yake saboda bakaken maganganun da akejifar uwarsa dasu
Hajiya suwaiba tayi salati tasanar da ubangiji tace yanzu duk wannan abubuwan dake faruwa
shine ba asanar daniba
Ta kalli Hakeem tace yanzu kai Ashe har yanzu baka daukemu da mutunciba
Kokana ganin Dan bani na haifi ubanka ba
To bari kaji idan bani da iko da kai inadashi da ubanka kuma ai ubanka yana da iko dakai ko
To wannan aure bazakayi shiba
Kuma maganar saki babushi dole yarinya ta zauna gidan ka
Daddyn Hakeem da tun da hajiya suwaiba tafara magana baice komaiba
Yayi gyaran murya yace to hajiya naji duk hukuncin dakika yanke
Maganar Saki tabbas zai maida matarsa kobakomai saboda darajar 'yar da ke tsakaninsu
Maganar fasa aure kuma babushi
Ba fashi
Idan bazaki matanba alokacin dakika zo da bukatar hada su aure sai da Abba na Allah yajikan
rai yafada cewan duk lokacin dayazo da bukatar kara aure bawanda ya isa ya hanashi
Sannan kuma koda SON bashida sha awar kara wallahi sai namishi da kaina
Saboda kugirbi abinda kuka shuka
Hajiya rukayya da Hajiya suwaiba suka kalli juna
Daddyn Hakeem yaciga dacewa
Narayu cikin maraici tunda natashi bansan dadin uwaba sai na uba ga kuma gallazar matar uba
wato ke Hajiya suwaiba narayu a hanunki cikin kunci da gallazawa
Kuma.abinda bakisaniba shine kice silar mutuwar mahaifiyata amina bayan ta haifeni kukamata
jifa da ciwo da haka har Allah yadau abinsa
Kinsan a ina naji kamaku nayi kuna zancen keda Hajiya larai kishiyar ki
Nayi kuka kaman raina zaifita
Dana ji wannan magana daga bakinki
Kunsani maraicin dole kuma kuka kasa rikeni tsakaninku da Allah
Ba irin abinda bakuyiba ganin namutu amma Allah yace saina rayu a duniya
Alokacin da Allah yabani haihuwar ABDUL HAKEEM nadade ina mishi adduar Allah yarabashi
da sharrinku
Dan nasan yanzu hankalinku zai komo kan 'Dana
Kullum cikin mishi addua a ruwa nake inabashi yasha
Wanda nasan ko mahaifiyarshi batasan niyya na ba
Saikuma kwatsam kukazo da gudirin aurawa Hakeem Laila alokacin shekarunsa basu wuce
ashirinba kuka dage sai anyi na amince ne saboda wani dalili
Dan koda din ma abbana bai aminceba inzaku iya tunawa
Saboda haka babu Wanda ya isa ya hanshi aure
Idan kunga 'yarku bazata zauna da kishiya you are free to live with her
Hajiya rukayya da jike sharkaf da zufa
Zatayi magana daddyn Hakeem yadaga mata hanu ba abinda zakice yaya rukayya