Chapter 7 Reading AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf Arewa Novels

AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf

Author :  Ummu Afan Category :  Arewa Hausa Novels

Chapter   7 / 15

18K to 21K   out of 44.6K words


🎗AKWAI LOKACI🎗



🎗PAGE 46 to 50🎗



PROFESSOR HAKEEM yace ina sauraronka malam shamsu

Ya shamsu yayi murmushi nan yabashi kadan daga cikin tarin rayauwarsu

Hakeem yace kace kai din dai har yanzu dai gaurone murkusheshen gaurone

Ya shamsu yayi murmushi yace a nakusa fita a layin gaurayen tunda nasamu abinyi

Hakeem yace hakane

Ya kalli kudin da ya shamsu ya ajiye mashi akan tebur

Yadauko wani rafar ya hada mashi dasu yace

Kadauki wannan kudin kaje kamuku cefane

Sannan kuma ka Isar min da gaisuwata wajen Abba da umma
Da kuma yar kanwarmu

Ya shamsu yace amma ai kudin sunyu yawa yallabai

Hakeem yayi murmushi yace karkadamu

Malam shamsu kana da sha awar cigaba da karatu ne

Shamsu yayi murmushi yace
Zanyi kokari bayan aure na ga nasamu ko degree na samu insha Allah

Hakeem yace Allah ya nuna mana ya shamsu yace nagode Allah yasaka da alkairi


Hakeem yace godiyan yana yawa kuma.banason godiya malam shamsu

Ya shamsu yayi murmushi yace ai ka canci hakan ne yallabai

Nan dai suka Dan taba hira har lokacin tashin Hakeem yayi suka tafi shida Ahmad

Ya shamsu kuwa yana fita yaje kasuwa yamusu cefane sosai har kaji da lemuka masu sanyi


Yana isa kofar gidansu mai adai daita sahu ya tsaya yabiyashi yafito da ka yansa

Yashiga cikin gidan da sallaman shi


alokacin Husnah tana alolar La asar

Tana ganinshi ta karasa wanke kafarta ta zo takarbeshi tana mishi sannu da zuwa

Yace alolar mekikeyi tace LA asar ya shamsu yace haba Husnah yazaki bari lokacin sallah ya
wuce kina da lafiyanki

Kafin tayi magana umma daga kitchen tace ai yau Husnah bataji dadiba ne

Tun da tadawo daga makaranta take kwance kanta naciwo

Ya shamsu yace ashsha barin je nasiyo miki magani
Yanzu zandawo

Husnah ta rike rigar ya shamsu tace wallahi naji sauki yaya

Dama abin da ya haddasa min ciwon kan ma

Wani taro akayi a school dinmu kuma nice presenter

Hayaniya ce yasani ciwon kan amma Dana dawo gida umma tabani magani nasha na kwanta
yadaina

Ya shamsu yace kinta tabbata
Husnah tadaga kai alamun ta tabbatar


Abba ne yayi sallama yashigo
Da Leda a hannunsa Husnah ta ajiye Wanda ya shamsu yakawo akan taburma tayi saurin
karbar na Abba alkamace Abba ya auno Dan Abba akwai son tuwon alkama dashida ya
shamsu


Bayan sun zauna ne ya shamsu yace Husnah dauko kayan can kiraba mana

Husnah ta tashi ta dauko

Plate guda uku da tasawa Abba kajin da kuma Irish potato wato dankalin turawa
Ta ajiye mashi maltina Dan tasan zaifi sonshi

Kafin tasawa umma itama maltina tamata

Sai ta hada musu itada ya shamsu ta dauki lacasera

Ta dauka wa ya shamsu fanta dantasan abinda kowa yakeso

Umma ta ce yau fa shagwaban yatashi Abba yace a din tayi baruwanki ai sunfi kusa yakarasa
maganar yana dariya

Husnah tace yauwa Abba fada mata dai

Ya shamsu yayi murmushi Dan yanason yadda suke rayuwarsu cikin son juna acikin gidansu

Suna gamawa Husnah ta tashi tadauko Dan karamin kula tasaka naman da komai yadda
sukasha sai wannan lemu sunkai uku

Tasaka a Leda tace ya shamsu wannan na anty kubra ne idan kaje kace mata inji sweet
kanwarta


Umma tace kai wannan soyayya da Husnah takewa kubra

Inba auren nan akayi ba hankalin Husnah bazai kwanta ba ba


Abba yace ai soyayyar Dan uwantane yashafi khadijan

Husnah tace gaskiya Abba kana da ganewa wallahi yadda anty kubra takeson ya shamsu yasa
na ke ganin girmanta

Shidai shamsu inbanda murmushi ba abinda yakeyi

Nan yawa mahaifinsa da ummansa bayanin yadda sukayi da maigidansa

Abba yace Allah yasa hakan shine mafi alkairi

Kaga girman alkawariko

To haka akeson mutum aduk inda yake ya rike gaskiya

Ya shamsu yace hanekam
Nan yabawa mahaifin nasa kudin gabadaya yace ya ajiye agunsa


Ya tashi yashiga wanka Wanda Husnah ce takai mai yana fitowa yayi alwala zuwa sallar
magriba


Bayan ya dawo daga isha ne yadauki kayan da Husnah tabashi yakaiwa kubra

Ya fesa turarensa mai Dan arha duk da talaucin su ya shamsu baya rabuwa da turare danshi
mutum ne mai tsafta sosai Dan gado sukayi a wajen iyayensu

Saikuma Husnah tace matsa kaban guri akan tsafta kokadan Husnah bata son datti

Yana isa gidansu kubra ta fito da hijabinta dogo

Duk yadda takai taboye abinda aka mata agida kubra takasa sai da yagane

Yace Lafiya naga fuskarki haka kubra

Kubra tayi yake tace bakomai wallahi abune yafada min a idona amma nacire

Kafin ya shamsu yayi magana wata kanwarta wadda suke uba daya tazo tace wai kizo inji
mama kicigaba mata da abinda tasaki

Kubra tace kice inzuwa yarinyar tajuya takoma zuwa cikin gidan

Tausayin kubra Yakama shamsu sosai yace kiyi hakuri kinji watarana sai labari nasan duk
akaina kikaganin wulakanci Dan kin ki bada hadin kai


amma namiki alkaqarin komai yazo karshe insha Allah

Yace karbi wannan inji kanwarki tace nakawo miki

Kubra tace Allah sarki Husnah Dan Allah kace mata nagode sosai

Yaciro dubu uku a aljihunsa yace karbi wannan kirike a hanunki

Kubra ta kalleshi ta kalli kudin tace haba sahibina ya daga samun aiki zaka fara barna da kudi
kawai kabarshi

Yace ai duk abinda zansamu kina da kaso aciki kikarba kawai kubra idan baki karba ba zaki
bata min rai


Cikin sanyin jiki kubra ta karbi kudin
Tace nagode Allah yakara budi yace amin

Maza koma gida kikarasa abinda aka saki karkiyi laifi ko

Tace to sai anjima ko kuma saigobe ba inji ya shamsu



Washa gari dasafe ya shamsu yagama shirin zuwa aiki bayan sun karya

Yafito yace wa Husnah muje ko

Husnah tace to yaya suka wa umma sallama

Suna futa kuwa suka yi sa ar keke napep yaya shamsu yatare musu sukashiga

Suna tafiya suna hira yace inga jakanki tabashi bata kawo komai a ranta ba

Ya shamsu kuwa yafaketa yasaka mata 1000 a ciki dubu daya kenan

Suna zuwa dai dai gate din su Husnah ya shamsu yace wa driver tsaya ta sauka nikuma kayi
dani BUK Husnah tasauka tana daga wa ya shamsu hanu

Yayi dai dai dannowar motar copper bash

Yaji lokacin datace ya shamsu kanan ya shamsu ne acikin keke napep din nan
Inkuwa shine zanbisa namishi bayanin komai


aikuwa copper bash yayi ta bin yaya shamsu abaya har yasauka a gate din BUK

Bayan ya shamsu yabiya kudin yayi gaba abinsa

Copper bash yayi parking yafito
Yabi bayan ya shamsu
Har yaje yayi signing yazo kafin yaje can kujerashi kofar

PROFESSOR HAKEEM yazauna

Copper bash yamishi sallama ya shamsu ya amsa yace kozan iya taimakonka

Copper bash yace a daman taimakon nazo nema

amma a gurinka ya shamsu

Yadda copper bash yakirashi ya shamsu yasan duk yadda akayi yasanshi ne

Ya shamsu yanuna mishi kujera
Nan copperbash yafada wa yaya shamsu irin son da yake wa kanwar shi

amma taki bashi dama hakan

Ya shamsu yace bazata ta taba amince maka har sai nabata izini

Umarni nabata nima kuma bazan taba amincewaba har sai nayi bincike akanka kafin nan kuma
na tabbatar tana sonka na uku kuma zakamin alkawarin barin ta tayi karatu bayan kinyi aure
amma wannan zaizone bayan nayi bincike nagar tarka


Copper bash yace wallahi ya shamsu indai akan asali ne bana shakku aje ayi bincike fata na
kawai idan kabincika bani da matsala ka amince min nakawo sadakina gidanku shikadai ne
zaisa hankalina yakwanta

Ya shamsu yayi murmushi yace karka damu Allah yashige mana gaba

Nan yawa ya shamsu sallama yatafi



*******

HUSNAH zaune kan kujerar class dinsu teacher din dazata shiga musu ta haihu shiyasa suka
samu Free time

Meenat tace gaskiya Husnah baki da kirki yanzu kakan dad dina da mummy na ya mutu amma
kikasa Neman gidan mu kije kiwa kakata ta aziyya


Husnah tace afuwan aminyi insha Allah ranar asabar zanzo gidanku nawa kakanmu ta aziyya

Meenat tace kai amma danaji wallahi har na matsu asabar tayi

Hajiya ta taganki labarinki kawai takeji agurina


Husnah tace aikuwa zanzo nagaisheta

Tace amin Allah yasa daddy ma yazo sai kigaisheshi

Kinsan tun yadawo kano aiki duk Saturday yake zuwa yaganni

Husnah tace to Allah yakaimu ranar

Suna haka wata junior tashigo tace anty husnah wai kizo inji uncle bash

Husnah tace OK kice ganinan zuwa

Meenat ta kebe baki tace wai meke tsakaninku da copper bash ne

Husnah tace sirrine amma zakiji nan gaba tashi muje kirakani kawai

Meenat ta tashi jiki a sanyaye tabi Husnah zuwa office din uncle bash

Suna shiga suka gaishe da bash ya amsa idonsa akan Husnah

Takaici Yakama meenat

Dan ita ba namijin datakeso irin copper bash
Tayi shishigin amma bata samu karbuwa ba

Ya kalleta yace zaki iya jiranta a kofa magana zamuyi

Meenat cike da bakin ciki ta fito

Copper bash ya kalli Husnah yace munhadu da ya shamsu

Cikin sauri husnah ta dago kanta da sauri tace meyace maka shikenan nasan yaya zaiyi fishi
dani

Copper bash yace karkidamu ba abinda zai miki shima naga alama yana da fahimta
Nan yafada mata yadda sukayi da ya shamsu

Cike da jin dadi Husnah ta tashi tayi hangar waje

Yana kiranta amma taki juyowa saboda kunya

Tana shiga sukacikaro da meenat

Kuka shabe shabe a fuskar meenat

Husnah cikin tashin hankali tace lafiya kuwa meenat cikin rashin sanin mezatace tafara in inna

Tace wallahi bansan menayi wa copper bash ba ya tsani yaganni aguri sai yakoreni

Husnah tace kiyi hakuri zanmishi magana kuma I sha Allah zaiyi dai dai

Meenat ta share hawayenta tace Husnah na tambayeki meketsakaninku da shi baki fada min ba

Husnah tayi murmushi tabata labarin komai

Meenat tace yanzu kinaso kice min kun Dade kuna soyayya da shi

Husnah tayi murmushi tace a
Amma ni banbashi daman zuwa gidan mu ba

Shine yanzu yake cemin ya wa yayana magana


Meenat tarike kai alamun jiri nason yarda ita

Husnah ta taimaka mata tazauna tace Amina Hakeem anya lafiyarki kalau kuwa

Gaskiya kitashi mu dispensary
Abaki magani

Meenat tace gida ma zantafi tai maka min da phone dina acikin bag

Husnah tabude jakar meenat taga wasu hadaddun wayoyi masu tsadar gaske kuda biyu aciki

Ta kwaso duka tace gasu meenat ta karbi daya takira driver din ta

Taba wa Husnah wayar ta mayar mata dashi jaka



******

Bayan kwana hudu ankai sadakin yaya shamsu gidansu kubra

Sannan kuma Abba yasai block da yashi ma aikata sukafara aikin gyaran inda ya shamsu zai
zauna acikin gidan ne amma ciki da fall da bayan gida acikinshi

Har Dan karamin kitchen dinta basai ta fito tsakar gida ba


Komai nasu aciki yake

Umma da Husnah sukaje kasuwa suka nemo akwatunansu masu kyau guda uku

Aciki akafara zuba kayan lefe

Wanda yanzu kusan duk asabar sai sunfita kasuwa


Dai dai gwargwado dai aka hada lefen ya shamsu

Aka kai gidansu kubra

Nan da sati biyu za adaura auren



Dubu ashirin ya shamsu yaba wa kubra tayi hidiman biki dashi



*****
Hakeem zaune kan kujerar yana hada wani muhimman file

Sai Ahmad yashigo yace wai baka gama ba har yanzu kasan time kuwa

Hakeem yace nagani ai nan da Kaduna dai insha Allah komai dare

Ahmad yace Allah yasa nidai kai nake jira kawai nagama shirina


Hakeem yayi dariya yace bantaba ganin ango merawankai irinka ba Ahmad

Ahmad yayi dariya yace ai gwamma ni kai inkatashi karawa ai bansan dokin dazakayi ba


Hakeem yayi murmushi dayake kara fito da zallan kyanshi

Yace tabbas kuwa lokaci yakusa zuwa inji ajikina nakusa samun choice dina sai dai bansan a
inabane


Ahmad yace kai amma fa akwai rigima Dan madam Laila zatayi rikici bakadanba

Hakeem yayi murmushi yace zatawa kanta danzan iya komai akan matata da zan aura Dan
itace zabina
Kaga kuwa ta taka a sannu

Ahmad yace wallahi man I like your style gaskiya zanso Gina gidana kaman yadda kake
handling naka


Hakeem yayi murmushi yace banbaka shawarar hakanba
Dan na tabbatar Aisha ba halinsu daya da Laila ba

Kagakuwa ba za amusu hukunci iri dayaba ko

Ahamad yace gaskiya Dan hankalin Aishat nagani yasa har nayi shaawar aurenta



Ya shamsu yashigo ya musu sallama suka amsa suka mika mishi hanu suka gaisa


Ya shamsu yace wa Hakeem gani yallabai

Hakeem yace dama zanfada maka ne zamu tafi Kaduna

Sai nan da sati daya zamu dawo

Hakeem yadauko invitation card na auren Ahmad

Yabawa ya shamsu yace muna gayya tarka daurin aure

Ya shamsu yayi murmushi yace masha Allah
Allah yabasu zaman Lafiya

Sai dai ranar yazo dai dai danawa auren


Hakeem yakalleshi yace har ansa rana baka fada minba malam shamsu

Dama bakayi niyyar gayya tarmu bakenan kokana ganin inka fada ma bazamu bane

Ya shamsu yayi murmushi kawai yace aikuna kokari ma da aiki
Kuma har ga Allah bani tunanin inna Baku invitation zakuzoba

Saboda matsayinmu badayaba

Hakeem da Ahmad suka kalli juna

Ahmad yace haba malam shamsu karkace haka saikasa muga kaman mu ba mutane bane

Ya shamsu yace to afuwan

Nayi kuskure

Hakeem yace to yanzu dai bazamu samu zuwaba amma muna maka fatan alkairi


Tace ban account number din ka inbada nawa gudumawar asiyawa amarya kaji

Ya shamsu yace wannan yana daga cikin dalilin dayasa naji fada muku zamanin yanzu kowa
yana fama da kanshi

Dan Allah kabarshi karka damu kanka


Hakeem yace karka damu ni nayi niyya kuma kasan bakyau maida hanun kyauta baya

Ya shamsu yace hakane yakaranto wa Hakeem number account din

Shima Ahmad yanaji kuma ya kwashe number.



Hakeem yace zakaji alert Allah yabada zaman Lafiya

Ya shamsu yace ameen nagode

Sukayi sallama har wajen mota



*****

Da daddare suna zaune tsakar gida ya shamsu yace Abba da ina son ba wa manemin auran
Husnah dama yaturo iyayensa

Kaga tana gama makaranta sai aiyi aurenko

Baban yace ai nalura yaron nan bashir kaman da gaske yakeyi

Umma ta ce sau biyu yana kawo mahaifiyarsa muna gaisawa

Shamsu yace alhamdulillahi gaskiya konina yaba da bashir

Kara shigowar sako yaji a wayarsa yaduba yaga alert ne na dubu Dari biyardaga professor
Ahmad


Kafin yayi magana wani alert din yasake fadowa daga boss dinshi a office

Wato professor Hakeem

Shima dai dubu Dari biyar dinne yaturo

Sun hada mishi 1 million NIRA cas su biyu suka bashi

Nan shamsu yakalli mahifinsa yafada musu


Abba yace kai amma wannan uban gida naka Allah yasaka mishi da alkairi
Umma tace ameen wallahi ko a mafarki bamutaba tunanin samun dubu Dari nan kusaba

Ballantana har million daya Allah yasaka musu da alkairi

Kai kuma saika kazauna dasu da zuciya daya

Nan dai ya shamsu yakira Hakeem a waya yace ga Abba na zai muku godiya

Hakeem yace haba shamsu yanzu saboda kyautar da baitaka kara ya karya ba zaka wahalar
da Abba wajen gode mana

To gaskiya indai Dan inbari Abba yagode min ne zankashe wayata

Insha Allah idan nadawo zanzo nagaisheshi da ka ina amma banda godiya tsakanin malam
shamsu

Ka gaida umma da kanwarmu

Sai da safe
Dif
Hakeem yakashe wayarsa


Dama wayar ya shamsu a handsfree take duk su Abba sunji komai

Abba yace gaskiya duk inda akeneman shugaba nagari wannan yaro ya kai
Allah yarabashi da sharrin duniya Lafiya

7 / 15