Chapter 3 Reading AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf Arewa Novels

AKWAI LOKACI 1 BY UMMU AFAN .pdf

Author :  Ummu Afan Category :  Arewa Hausa Novels

Chapter   3 / 15

6K to 9K   out of 44.6K words

hafsat

Mummy hafsat tace kubace min daga gida yanzun nan insake ganin kafarki agidan nan kiga
abinda zaifaru

Da gudu suka fice agidan kuwa harsuna tun tube

Suna zuwa parking space
Zasu shiga mota sai ga motar abdulhakeem aikuwa Laila washe baki tayi tace biky Gashi nan
fa biky tace waw wannan

Zazzafar motar shice

Laila tace kadan ma kika gani indai Hakeem ne kinga zomuje musameshi karyashiga


Hakeem kuwa shida Ahmad ne
Ahmad yace wa Hakeem ya kaman kunyi baki Hakeem yace maikagani

Ahmad yanuna mashi su wurinsu laila
Hakeem yakai idonshi gurin
aikuwa yana ganin sun nufosu yadaure fuska

Ahmad yace kai harda bakin ma zaka nunawa halinka ko
Hakeem dai baice komai

Laila suka karaso gurin su Hakeem din
Sai Ahmad yadan durkusa yace anty ina wuni

Cikin tashin hankali Laila tace wace ce antyn taka
Ahmad yakalleta cikin rashin mahimta danshi yadauka yayar Hakeem ce dangin su

Danshi baitaba sanin laila Ba tunda Hakeem bazuwa yakeba

Abin yaba wa Hakeem dariya amma yaci fuska sosai dan kar laila taga hakorinsa da sunan
dariya

Yarufe motarshi ya kalli Ahmad yace mujeko

Laila ta tari gabanshi tace haba Abdul kasanfa gurinka nazo ko

Hakeem yakalleta ya watsamata wani mummunar kallo yace gurina kikazo namiki me

Abin yaba Laila haushi dan ya tsinkata agaban babbar kawarta

Ta daure tace naga har yanzu baka zo gida munyi maganaba kuma baka kuma tambayeni
abinda nake bukata na game da harkar bikinba shine mama tace nazo nakarbi kudin dazan yi
hidima dasu


Sai a lokacin Hakeem yayi wani killer smile yace lalle kuwa bazakiyiba
Kikoma gurin wacce ta hada abin sai tabaki
Nikam kwandala ta bazaiyi ciwo akanki Ba

Nan ya wuce ta Ahmad yabi bayansa suka shiga cikin gida


aikuwa da gudu Laila tafada mota
Dan tunda take Ba a taba wulakantata irin wannan Ba

Kawarta biky tayi ta rarrashinta kasa driving tayi biky ce tayi


Hakeem da Ahmad suna shiga falon mummy
Suka ganta zaune kan kujera
Hakeem yasaki murmushi yace mummy na yadai naga kaman antaba minke

Ahmad yanemi guri yazauna yace mummy an wuni lafiya

Cikin fara a mummy hafsat tace lafiya qalau Ahmad ya su hajiyartaka
Ahmad yace lafiya qalau tace zata zo anjima

Mummy hafsat tace aikuwa kaman tasan inason ganinta Allah yakawo ta lafiya

Hakeem yace mummy shine wato kinga Ahmad ina miki magana kina wani basarwa ko


Mummy tayi murmushi tace ai matarka ce taba tamin rai shiyasa

Hakeem yadaure fuska yace daliba zakifara ko

Mummy tayi murmushi takalli Ahmad tace Ahmad katayini da abokinka dan Allah matarshi tazo
ta bata min rai dan Allah basai na huce akanshi Ba

Ahmad yayi dariya yace kinyi dai dai mummy

Tace a to kaima kafada dai

Hakeem ya harari Ahmad ya kalli mummy yace daliba bazaki daina kiran wannan Mara kunyar
yarinyar da mata ta bako

Mummy hafsat tace toya zamuyi komunki ko munso sai anyi

Nan tabasu labarin yadda sukayi da su Laila dasuka shigo
Hakeem yatashi ya suri key din motarshi yayi hanyar fita

Mummy hafsat tace dagata dan albarka ina zaka yace mummy kibarni naje naci ubanta har

tana da gost da zata zo gidan nan tasaki magana haka


Mummy hafsat tace kalesu nima din ai sunsan wacece ni zata je tafada wa uwarta

Zasu sake sabon shiri mu basusan shirinmu yafi nasu dan muda Allah muka dogara

Hakeem yace wai mummy maiyasa daddy yakasa gane mutanen basa kaunarshi Ba sonshi
suke ba fa

Mummy hafsat tace nima abun yana damuna wallahi hakurin mahaifinka yayi yawa wallahi


amma bakomai duk mai hakuri wataran yana tareda riba

Mummy tace kutashi kushiga kuci abinci

Suka tashi zuwa part din HAKEEM

Suna shiga dariyar dayake cin Ahmad yafito dashi

Yayi sosai Hakeem yace wai kai kuma wakake wa dariya

Ahmad yace wallhi matarka da nacewa anty

Hakeem yace karkasake cewa matana kace kawai matar kaddara


Ahmad yace narki gaskiya man na tausaya ma wannan yarinyar wallahi kokadan wallahi bakuyi
marching ba kokadan

Da zanbata shawara data nemi mijinta a wani wajen tabarka

Hakeem yayi dariya yace akai man shine wannan dariya haka amma nima naso nayi dariyar
Dan bakaramin dariya abin yabani ba
Kawai dai banson rainine yasa na make kawai

Ahmad yace oh baruwana fa randa zaka angonce ina ina Dan haka nayishiru Allah yabada
zaman lafiya

Tsaki Hakeem yayi yace katashi muje muci lunch idan kuma baka gama surutun ba to

Nan dai sukayi hira amma Rabin hirar tsokanane Ahmad yakewa Hakeem

***
Bayan komawar su Laila gida tana kuka tana bawa mamanta labarin abinda mummyn Hakeem
da Hakeem din suka mata

Ran hajiya rukayya yabaci
Tadauki waya takira uwarta hajiya suwaiba ta fada mata komai abinda Laila tafada mata

Nan itama hajiya suwaiba ranta yabaci tace bakomai ai sunkusa shigowa hanunmu

Tayi hidimarta da kudinta kawai zata fanshe ai

Hajiya ruakayy tace amma hajiya kinsan wallahi bakudi a hanu na sosai

Hajiya suwaiba tace kwantar da hankalinkki
Kituro min ita jikallen sai nabata wasu kudi

Nan hajiya rukayya tayi godiya ga mahaifiyarta kafin takashe wayar takalli 'yartata dake kukan
wulakancin da akamata

Tace kidaina kuka kitashi kitafi gidan hajiyata zata baki kudi konawane sai kufara hidimarku na
kawaye

Nan Laila ta washe baki tace kai Allah yabarmin kakallena yanzu ita zata bani kudin

Hajiya rukayya tace kwarai kuwa aiba abida bazatayi miki ba kece fa jikarta tafarko


Nan dai Laila suka tashi suka tafi karbo kudin """"



Ranar daurin aure dasafe hajiya suwaiba takira alhaji abubakar tace mishi yau daurin aure
amma haryanzu basuga kayan lefe ba

Alhaji abubakar yace ai mun sha afa ne hajiya kaman nawane za a hada lefen dashi

anzo inda takeso tace million biyu sun isa

Alhaji abubakar yayi signing a cheque yabata tace yauwa Allah yayi albarka

Alhaji abubakar yace Ameen hajiya

Nan yatashi yashige wajen mahaiginsa alhaji shuaib

Yanashiga yasameshi yagama shirin daurin auren ne ma

Yace a a abubakar kaine tafe kohar kafito gurin daurin auren ne

Alhaji abubakar yayi murmurshi yace
ai hajiya ce takirani akan maganar kayan lefen Daba akawo ba

Alhaji shuaib yayi dariya yace wargi ma guri yakesamu

Tamin magana nace tawa angon magana shine taki kai dayake sunga kana da hakuri shine
suka bita kanka ko

Alhaji abubakar murmushi kawai yayi baice komai ba

Alhaji shuaib yace yadda yaron nan yake yana burgeni suna mugun shakkarsa

Dan ina mata maganar ta tambayi Abdul Hakeem dakanta bakaga yadda ta yiba

Alhaji abubakar yace ai yaron nan nima yana bani mamaki wlh gashi karamin yaro amma
koyanzu nasake mishi komai zai riqe sosai

Alhaji shuaib yace ai Allah ne yama sakayyar biyayyarka gareni da wannan d'anaka
ABDULHAKEEM

Zakayi alfahari da haihuwar Abdul Hakeem saboda kaima nayi alfahari da haihuwarka Allah
yajikan mahaifiyarka amina

Alhaji abubakar yace ameen Abba

Nan sukayita hirarsu har lokacin daurin aure yayi suka fita zuwa gurin daurin auren



Hajiya suwaiba ta kira yarta hajiya rukayya tafada mata yadda sukayi da alhaji abubakar

Wani irin ihu hajiya rukayya tayi tacikin waya tace million biyu fa kika ce hajiya

Hajiya suwaiba tace to meza afasa

Hajiya rukayya tace aikin ki nakyau hajiya ta

Kinga munfara bambara tun yanzu ko

Hajiya suwaiba ta ce kidai bari yarinya dai Allah yakashe yabata





****

Bayan andaura auren Abdul Hakeem da Laila usman



Daddyn Hakeem ya dawo gida bayan yazauna
Mummy hafsat takawo mishi abinshi yaci sannan yabata labarin yadda sukayi akan kudin lefe

Mummy hafsat tayi murmushi tace a lalle sun wankeka

Yanzu zasuga kaman shirinsu yafara aiki kenan

Murmushi Daddyn Hakeem yayi yace Hafsat mata agurin abubakar maman Abdul Hakeem

Rigimar ki yana bandariya kefa baki yarda dawannan auren bako

Mummy hafsat tayi murmushi tace ai Dana baiyi aureba

Dan banmasan anyiba wallahi kawai dai za aiya kiran aurn da kaddara

Daddyn Hakeem yayi murmushi yace zanso kimishi fatan dacewa kamar yadda nadace dake
Dan ko zabin kaina nayi ba lalle nayi dacen danayi akankiba hafsat


Next page

Your comments is needed fan's 踫踫踫

踫踫踫踫踫
潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤
[30/04, 5:48 PM] UMMU AFAN 潤撕: BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM


潤HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN 潤

DEDICATED THIS PAGE TO LOVELY SON AFAN
手手手手手手


潤GORGEOUS WRITERS FORUM潤

潤G.W.F潤


HOME OF GORGEOUS INTELLIGENT AND EXPERTS WRITERS WE ARE THE AMONG
THE REST




潤A KAWAI LOKACI潤




潤PAGE 21 to 25 潤



Ankai amarya Dan kararen part dinta dake gidan su Hakeem .

Mummy hafsat kam a ranar ma gidansu taje wa wuni
Saboda batason damuwa """"'


HAKEEM suna zaune shida Ahmad

Ahmad yace kai kasan karfe nawa yanzu katashi muje narakaka dakin amarya fa .

Cikin halin ko inkula Hakeem yace lalle kuwa su amarya manya bari ma kagani

Ya kashe phone din shi ya gyara kwanciyarsa akan bed din Ahmad .

Ahmad yace banganeba mekake nufi badai anan zaka kwana ba

Hakeem yayi banza dashi yayi baccinsa Ahmad yace OK halin ya motsa ko

ai wannan amarya taja wa kanta data waye. Hakeem da bata kanta wahala ba wajen auranka
ba


Nan shima yakwanta abinshi Dan yasan duk yadda zaikai ga magiya Hakeem bazai tashi ba .




Amarya Laila tana ta zuba ido taga ango yashigo shiru kakeji malam yaci shirwa kawayenta ma
sun gaji suntafine


Idonta biyu har wajen karfe uku ba ango
Tadauki waya takira Maman ta Maman tace yadai laila naga kiranki yanzu


Kingane dai yadda akace kiyi anfani da maganin ko karfa kiyi wani abin da zaisa yaki kusantarki
kinsan maganin na yau ne kawai

Duk hanyar da zakibi yakusance ki
Kiyi shi karmuyi asara makudan kudaden da muka narkar wajen karboshi

Laila tace yanzu dai dakin tsaya na fada miki abinda zanfada miki

Hajiya rukayya tace inajinki meyafaru

Laila tace haryanzu fa bai shigo gidan ba ma

Cikin tashin hankali hajiya rukayya tace munshiga uku
Yanzu soyake muyi asarar makudan kudaden nan

Ki kirashi a waya mana
Laila tace ina naga numbarsa

Hajiya rukayya tace shikenan munyi asarar kudinmu

Dan malam yace maganin kwana daya yakeyi idan yakusanceki zai zaima rakumi da akala
bazaiji maganar kowa ba sai abinda kikace mishi


Kuma zai tsani iyayensa

To gashi Hakan su bai comma ruwaba

Har kuka sai da hajiya rukayya tayi Dan maganin nan naira million daya haka suka caske wa
malam


Gashi yanzu wannan Dan ban zan yaron yaja musu asara


Daga laila har uwarta basuyi bacci ba


*********

Washagari da misalin karfe goma Hakeem yafito daga wanka daga bathroom din Ahmad

Yashirya cikin wasu kananun kaya sun balain mishi kyau ya fesa turare

Kafin nan yakalli Ahmad da yariga yashirya Dan yariga Hakeem tashi tunda suka dawo daga
sallar asuba shi Hakeem sai yanzu yatashi


Hakeem ya kalleshi yace yace muje mukarya zanje naga dalibata fa

Ahmad yace to ango muje dining din ko
Suka wuce zuwa dining area na Ahmad

Sukayi break fast
Kafin suka dauki hanyar zuwa gidan su Hakeem

Suna hanya kafin sukai gidan su Hakeem sai daddyn Ahmad yakirashi akan yazo zai aikeshi

Ahmad yace man sauke ni kawai nakoma gida idan na dawo daga aikan dad zan shigo
mugaisa da amarya

Hakeem bai kalleshi yajuya da motar yamaida Ahmad gida kafin shikuma yakoma gida
yanazuwa yayi parking a gurin parking dinsu """"


Laila tana jin shigowar mota tabude labulen window din ta
ai kuwa taga shine
Harfitowarsa tagani

Yamata kyau kuwa Dan Hakeem mai kyau ne bakarya
Da badan son kudin dayamusu yawaba ai Hakeem miji ne na nuna wa sa a

Hakeem ya kulle motarsa yayi part din mummy
Yanashiga yaga bata falo ya haura bedroom dinta

aikuwa tana can tana ninkin kayan ta tana jerawa a sif

Yashigo yace assalamualaikum mummy na

Cikin murmushi mummy tace Dan mummy yakake

Dafatan dai katashi lafiya ko

Hakeem yace lafiya qalau daliba kawo kiga ni koma kawai kizauna muyi hira

Mummy hafsat ta nemi gefen bed din ta tazauna

Tsaf Hakeem yagyara wa mummy kayan ta yasake gyara mata bedroom din kafin yace mummy
kinci abinci kuwa

Mummy tayi dariya tace kaima dai tsokanata kake yaushe zankai har wannan time ban ci
abinciba "'''

Hakeem yayi dariya yace acici
nasan ai dama agurinki na dauko ci

Mummy tayi dariya tace a a nikarka min sharri

Mummy tace ba wannan ba ma
Dama inason magana dakai

Hakeem yadawo da hankalinsa kanta

Tace Dan albarka jiya ba agida ka kwanaba hakane

Hakeem yace hakane mummy a gidansu Ahmad na kwana


Mummy tace ai baka kyauta ba
Tunda anriga andaura dole zamu rungumi kaddara
Yanzu dai Laila tariga zama matarka

Dan haka ina umartarka da karka wulankanta aure

Aure ba abin wasabane duk kuma wani sharrinsu zai koma kansune da izinin Allah bazasu
taba tasiri akanmu ba

Hakeem yace ai mummy ki kwatar da Hankalinki adduoi na tsarin jiki ba Wanda bamayi agidan
nan dai
Dan haka ba abinda zasu iya mana

Mummy tace Allah yasa Dan albarka acigaba da kula da addua Dan ina tsoron sharrin mutane
""""""


Bayan sun gama magana yace Mum zanje wajen Daddy a office Dan kinsan jibi mukeson
dagawa fa Hutu yakare zamuje mutattauna


Mummy tace kadage dai sai katafi ajibinko

To da amaryar zakatafi Hakeem yace Allah yasauwake tayi zamanta ba inda zantafi da ita

Mummy tace bazan maka doleba amma ka tabbatar komai kabari a kafin tafi

Hakeem yace insha Allah mummy

Yace barinje gurin daddyn

Mummy hafsat tace a a kafara shiga kaduba yar mutane tukun ko
Koba komai fa yar uwarkace

Yace to mummy sai na dawo
Tana jin dadin inda Dan nata baya mata musu

Hakeem yashiga part din shi
Direct bedroom din shi yawuce
Yaje yadauko wani file kafin yasake fitowa

Laila kuwa basan shigowarshi ba fitanshi tagani
aikuwa kafin yakarasa fita tasha gabanshi

Yace lafiya kuwa zaki sha gabana haka

Laila cikin yanga tace Haba Abdul ya kake min wasu Abu kaman ba mijina kuma Dan uwana ba

Dan Allah kadawo muzauna kona minti biyar ne .

Hakeem ya watsa mata wani kallo Wanda dakanta tabashi hanya yawuce abinshi zuwa office
din dad dinsa

Hankalin Laila yatashi tace anya kuwa wannan
Mutum """


********
Da daddare bayan daddy da Hakeem sundawo sunci abinci can wajen karfe goma
Mummy tace Dan albarka tashi katafi kabar Laila ita kadai

Badan yasoba yamusu sai safe ya wuce part dinsa ,
Yana shiga falon Laila ta na kashe wayarta dasukaga gama da gawarta

Ko kallo bata isheshiba ya wuce abinsa zuwa bedroom dinsa

Yanashiga wanka yafada

Yana fitowa sukayi ido hudu da Laila cikin wasu arnar kayan bacci wato sleeping dress kenan

Kallo daya yamata yakau da kanshi
Danshi idan ya raina kasuwa ko sauto baya mata

Ya goge jikinsa yashafa mayukansa masu kamshi kafin yasaka night Wear din shi

Ya kwanta tare da kashe wutar dakin """""


ai kuwa Laila tafashe da kuka
Tun abin na bashi haushi har yagaji yace dalla malama kitashi kifita min adaki

Cikin kuka tace Haba Abdul yanzu wannan shine zumuncin da iyayenmu suka hada muyi kenan

Hakeem yayi wani uban tsaki kafin yajuya ya kwanta abinshi

Can tace ai idan kai baka bukatata ni ina bukatarka

Bai kamata kahanani hakkina da Allah yarataya a wuyarka ba """"'

Tabbas yasan hakane kuma mummynshi ma ta mashi tuni akan haka
Koba komai gwamma yafita a hakkinta

Yajuya yace mata damuwarki kenan yasa aka miki aure ko
Kafin tayi magana ya bajadda ita akan bed din

Yacire sleeping dress din nata yayi wurgi da shi bako romance

3 / 15