Chapter 1 Reading ARZIKI RABO Complete Hausa Novels by Dijensy.txt Arewa Novels

ARZIKI RABO Complete Hausa Novels by Dijensy.txt

Author :  Dijensy Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   1 / 21

1 to 3K   out of 61.6K words

 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍


*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*



*Assalamu Alaikum ,we met again a wannan sabon littafin nawa mey suna ARZI'KI RABO Allah ubangiji yasa na kammala lafiya,ina wa masoyana fatan alkairi we are together always and forever💕*


*Note:fiction*



   *Dedicated to our mothers*

         🅿 0⃣1⃣

    
*Kano* 

Gidane madedeci d'aki biyu yake d'auke dashi tsakar gidan ma ba wani fad'i gareshi ba.Sede ba lefi gidan ya tsaru ga shafe da akai hakan ya nuna alamar ba a dad'e da tarewa ba.Cikin sitting room kuwa yanda aka ziba kujeru masu tsada ba za'ace a wannan gidan suke ba d'akin gado ma haka furnitures ne tsadaddu d'akin kansa da'kyar ya iya d'aukan gado ,wardrobe se a d'ayan d'akin aka sa.

      Wata mace na gani a d'akin wadda ke zaune kan kujerar mirror tana tsara d'auri ,mashaAllah kallo d'aya zakai ka gano kyau da take dashi ,fara ce amma ba irin tass d'innan ba gata da hanci dogo haka girarta ma sirira lips nata yasha maroon janbaki ga earings da necklace nata masu stones green,tana sanye da atamfa green me d'auke da ratsin orange da black .Kayan jikin nata sosai sun d'auketa chif a jikinta,koda ta mi'ke bayan ta kammala d'auri na lura da tsahonta medium ce domin baza a kirata gajeriya ba haka baza a kirata doguwa ba  gashi batada 'kiba .

     Wayarta ta d'akko dake kan gado ,call log naga ta shiga inda tayi dialing suna "My Dear".Ba jimawa akai answering ta d'ayan 'bangaren " My Azizaty" aka fad'a.

      "Dear naji shiru baka taho bane?" Ta tambaya murya 'kasa-'kasa.

      "Azizaty sorry! Umma ce ta tsayar dani kinga amma yanzunnan zaki ganni". Ya fad'a.

     " Toh shikenan kagaida min ita".Ta fad'a.

     "Yawwa my azizaty sena dawo".Ya fad'a.

     Bayan ta katse wayar ne tayi hanging tare da sakin murmushi ,fuskarta ta sake kalla jikin mirror d'in sannan ta fita daga d'akin.

     Bayan like 10minute tana zaune a sitting room ta jera tray da sauran jug da cup ga warmers a kai ,tana danne-danne a wayarta tajiyo knock. Ba 'bata lokaci ta tafi bud'e 'kofar ,koda ta isa soron ta jiyo muryarsa yana waya lalla'bawa tayi ta bud'e 'kofar da sauri ta la'be bayan 'kofar.

    Yana shigowa kafin yayi wani motsi yaji an rufe masa ido da tafin hannu ,jin 'kamshin turarenda ke sanyaya masa rai yasa yayi saurin sakin murmushi.

     " Azizaty! "Ya kira sunanta.

     " Na'am Dear sannu da dawowa".Ta fad'a bayan ta sauke hannunta.

        "Wow! Azizaty irin wannan kyan haka ai seki sa na kasa shiga ciki". Ya fad'a harda zaro ido.

      Wani murmushi ta saki wanda ya sake bayyana kyawunta." Toh ka taimaka mu shiga".Ta fad'a.

     Hannunsa cikin nata suka 'karasa har d'aki."Dear wanka zaka fara yi ko abinci zaka ci tukun?" Ta tambaya tana jiran amsarsa.

      "Duk wanda kika za'ba min Amarya ta" Ya amsa.

     "Toh na za'ba ,ka fara yin wanka".Ta amsa.

     Da kanta ta tayasa rage kayan ya shiga wankan,cikin 'yan mintina 'kalilan ya fito.Shirinsa yayi cikin T-shirts fara se jeans blue ,sosai yayi kyau.

    Ahmad mutum ne me tsaho gashi fari ne wanda yama d'ara ta, baida 'kiba sede ba siriri bane yana da murd'ewar jiki dede.Wajen kyau ma ba abarsa ba tsakanin shi da ita banga wanda zai nuna wa wani kyau ba sede fari daya d'areta.

      " Harka gama shirin?" Ta tambaya lokacinda ta shigo d'akin.

   "Iyye Azizaty baki taya niba ina kika shiga?"

    "Daga shigarka toilet nayi ba'ki" Ta amsasa.

    "Ba'ki? Toh yanzu ya za'ai dani?" Ya tambaya kamar wani yaro 'karami.

    Yadda yayi maganar ne yasata murmusa "Nasanki kina yin ba'ki zaki shareni". Ya fad'a.
  
     " A'a bazan shareka ba bari na kawo ma abincin d'akin".Ta furta.

    Sitting room d'in ta shiga ta d'akko abincin ta mayar d'aki,su kuwa ba'kin ta d'ebo masu wani a kitchen. Koda yaga ta dawo d'akin ya tamabayeta"Ba'kin naki fa?"

    "Yara ne fah kuma na zuba masu abincinsu ". Ta amsa.

    " Ok ".Ya fad'a.
  
     Zama yayi a kan sallayar data shimfid'a ,yana kallo ta gama zuba abinci tasa spoon." Dear na zuba ma".Ta fad'a.

     "Toh se yaya kenan?" Ya tambaya yana kallonta.

      "Se ci". Ta amsa.

      " Nikuma hannuna baze iya chiba".Ya fad'a.

    Yana fad'ar haka ta gane me yakeke nufi,da kanta ta d'auki spoon d'in ta fara basa. "Ke fah baza kici bane?"

    "Ni ai naci nawa". Ta amsa.

    " Kefa kika ce zaki jirani mici tare".

    "Toh ba kaine ba se 3 ka dawo". Ta fad'a cikeda shagwa'ba.

    Tana birgesa idan tayi hakan ,kallonta kawai ya tsaya yi " Ayya my Azizaty sorry nima nafiso mike ci tare ".Ya fad'a tare da tallafo ha'barta.

     "Yawwa dear shine baka bari minje wajen umma ba tare koh kayi min wayo". Ta fad'a.

      " Kinsan nikaina bansan zanje ba,ina makaranta umma tayi mini waya wasu 'yan uwanta daga zaria sunzo shine fa naje muka gaisa".Ya fad'a.

     "Ayya da ka kawosu nan mun gaisa".

     " Ai ba kwana zasi ba ba lokaci da na kawo su".Ya fad'a.

      A haka tana bashi suna hirarsu har ya 'koshi,bayan data gama had'a kwaninka takai kitchen ta koma wajen yaran da suka zo.

        Wannan ma'aurata Reyhana da Ahmad sun kasance masu 'kaunar junansu,kafin suyi aure seda aka kai ruwa rana.Mahaifiyar Reyhana fafur ta'ki yarda Ahmad ya auri 'yarta ,ba wani dalili bane illa saboda talaka ne ,da'kyar mahaifin Reyhana ya tsawatar mata haka bataso ta ha'kura akai auren.Ahmad  tun yana 'karami mahaifinsa ya rasu,se dangin mahaifiyarsa ne da'kyar suka d'auki nauyin karatunsa na secondary dan dangin mahaifinsa basuda hali sosai kuma duk cikinsa kowa ya'ki d'aukan nauyin sa.A haka bayan ya gama secondary school yana 'yan bige-bige ya shiga college yayi diploma.Kasancewar halin rayuwa da ake ciki da'kyar ya samu aiki a wata private yake teaching albashinsa ba yawa gareshi ba kunsan private school. Koda yazowa da umma mahaifiyarsa zancen auren Reyhana da farko bata goyi baya ba dan tasan Reyhana ta kere masa, yarinya ce data taso cikin gata ,iyayenta masu kud'i ne gasu 'yan boko. Haka yasa Umma ta tsorata,ganin Ahmad ya'ki ha'kura kuma taga irin son da Reyhana ke masa yasa ta ha'kura ta bisu da addu'a.Momyn Reyhana kuwa da danginta sun tsani auren ,Abbanta ne kawai ya goyi baya, toh wannan kenan.

   Around 8:18pm bayan ya dawo daga masjid ,a d'aki ya isketa ."Azizaty am back ".Ya fad'a tare da zama kan gadon gefenta.

     " Sannu da dawowa". Ta fad'a tana murmushi.

     "Yawwa ". Ya fad'a tare da d'ora kai a cinyarta ya kwanta.

      "Ya labarin school d'in?" Ta tambaya.

     "Azizaty d'alibai rashin ji suna chaza min kai".Ahmad ya fad'a tare da ri'ko hannunta ya d'ora kan cikinsa.

      " Allah Sarki dear gashi kaikuma baka son hayaniya".Reyhana ta fad'a d'ayan hannun nata tana shafa kan sumarsa dake d'auke da gashi yale-yale na Fulani d'innan gashi ba'ki.

     Hakan yasa ya rintse idanunsa kamar me barci."Yes Azizaty dad'inta ma ina dake kinga kece me kwantar min da hankali a kodayaushe that's why kullum position naki a 'kalbi na 'karuwa yake".

    Murmushi ta saki wanda hatta ha'korinta seda ya bayyana ,tana jin dad'in kasancewa da mijinta ita kad'ai tasan halin abinta se Umma kankat ,Reyhana tasan Ahmad d'inta da rashin magana cikin jama'a amma ita a gunta daban ne tasan yadda zata bi dashi.

     "Yaushe toh za'a tsayar da ranar zuwa wajen Umma mu gaisheta?" Ta tambayesa.

     Shiru taji be amsa ba,data kalli fuskarsa kuwa taga yayi bacci ma.D'an murmushi ta saki, wayar ta dake gefe ta d'auka tayi ta 'kyasta masa photo. Itama daga baya baccin ta soma ji ,a hankali ta shafa fuskarsa."Dear 9:30 yayi ka gyara kwanciyar kar wuyanka ya 'kage".Ta fad'a a hankali.

      Kasancewar baida nauyin bacci yasa ya farka"Azizaty amma de 'kafanki beyi tsami ba koh?"

      "Uhmm beba". Ta amsa.

Tashi yayi daga kwanciyar " Toh kema kiyi shirin kwanciya mu kwanta yanzu kema da wuri zaki kwanta".Ya fad'a.

     Tashi tayi ta fad'a toilet dake d'akin tayi wanka tukun bayan ta fito ta sanya sleeping dress,shima already yayi shirin kwanciya."Azizaty let sleep".Ya fad'a tare da mi'ka mata hannu.

     Mi'ka masa nata tayi ,yana sani ya janyo ta ta fad'o jikinsa."Kai Azizaty kinyi nauyi dayawa kinjiki kuwa".Ya fad'a cikeda tsokana.

      "Nid'in ce nayi nauyi". Ta furta tana gyara kwanciyarta.

      " To shiru a kwanta".Ya fad'a tare da kashe light d'in ya jawota jikinsa sannan ya jawo blanket ya rife.

       "Sleep tight". Ya fad'a.

        " Uhm". Ta furta.

     Ba dad'ewa bacci ya kwashesu duka.

                  ****

    Washegari kamar ko yaushe 5:30am sun tashi ,ko Reyhana tayi sallah bata komawa bacci seta ga fitarsa,ita take tayasa shiryawa tayi  breakfast.

       "Azizaty! " Ya kira sunanta .

     Tana kitchen ta taho"Dear kirana kake?"

       "Eh Azizaty kinga wani littafi ajje a kan drawer?" Ya tambayeta .

      Kad'a masa kai tayi tareda nufar inda drawer d'in yake. Jawo drawer d'in tayi  sanannan ta ciro littafin.

     "Gashinan". Ta mi'ka masa.

      " Thanks my wife". Ya fad'a yana murmushi.

       Tana birgeshi yadda take kula dashi haka property nashi ma bata bari ba.

       "Ka gama shirin kenan?" Ta tambaya.

     "Yes Azizaty". Ya amsa.

     " Toh ga breakfast is ready". Ta fad'a.

      "Wow! My wife hancina kina kasheshi da 'kamshi". Ya fad'a sanda ya bud'e sauce d'in ,plate kuma soyayyen dankali ne.

     Da kanta ta had'a masa tea d'in ,danma yayi late shiyasa sauri-sauri yaci.

     " Allah ya kiyaye hanya".Ta furta sanda ta rakoshi soro.

      Sunkuyowa yayi kad'an ya manna mata kiss a kumatu.

     "Sena dawo". Ya fad'a.

     " Bye".Ta fad'a tana waving hannu.

    Bayan data kammala nata breakfast d'in ta tattare kwanukan ta wanke ,se sauran gyaran data 'karasa,kan gado ta hau abinta ta koma barci.

AR²💖

Jasko💕
   
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍


*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 0⃣2⃣

  Reyhana ba ita ta tashi ba se wajen 11:10am,wanka tayi tayi shirinta cikin material blue ya d'auketa sosai.Kitchen ta shiga ta d'ora tukunya tana canki-cankin me zatayi kuma tasan shi Ahmad ba ruwanshi ko ta kira ta tambayeshi ba za'ba zeba.Daga 'karshe de ta yanke shawarar yin tuwon semovita da miyan alayyahu.

     Around 12:00pm ta kirasa a waya,lokacin yana class ya fita tukun yayi picking.

     "Azizaty!" Ya kira sunanta.

    "My dear ya school d'in yau?"

    "Kinganni ina class ma na fito". Ahmad ya fad'a.

     " Ok, toh go back to your student seka dawo". Ta fad'a.

     "Toh my wifey sena dawo". Ya fad'a.

    Daga haka sukai sallama,komawa tayi kan girkinta dama miya ya rage ta gama.

               ***

   2:23pm Ahmad ya dawo gida,Reyhana kuwa tuni ta kammala komai ta sake dusting powder a fuskarta se lipgloss data 'kara a lips d'in.

       Tana jiyo knocking nasa tayi saurin fita,ba 'bata lokaci ta bud'e 'kofar.Bata ankara ba taga yayi hugging nata.

      " My dear mutanen waje zasu hangomu fa". Ta fad'a.
  
     "Ina mutanen suke azizaty banga kowa ba". Ya fad'a dan unguwar ba hayaniya sosai.

     'Kofar ya tura ya rufa tukun yayi breaking hug d'in." Kinyi missing d'ina ma kuwa azizaty? " Ya tambaya.

     "Meyasa kace haka?" Ta tambaya.

     "Ehmana naga kamar baki missing d'ina ba".

     " I do mana".Ta fad'a tana turo baki.

     "OK if you miss me then". Ya fad'a tare da nuni da kumatunsa alamar tayi masa peck.

       Murmushi tayi tukun tayi d'age nan tayi masa peck.

      " That's my Azizaty ". Ya fad'a tare da tallafota jikinsa.

       Kamar koyaushe ta kai masa ruwan wanka toilet,bayan ya shirya kuma ta kawo masa abinci.Yau tare suke cin abincin dan itama bata ciba,suna ci suna hira.

       " Yawwa my d yaushe zami je gaida Umma?" Reyhana ta tambaya.

      "Kede kawai kina so kiji yaushe zaki wajen mommy". Ya fad'a yana mata dariya.

      " Laaa! Ni ba haka nake nufi ba". Ta fad'a.

      "Zaki wayence ba". Cewar Ahmad.

      "Toh shikenan baka amsan tambayata ba". Ta fad'a.

      " Reyhana yau har kwanakin nawa a gidannan ma tukun?"

      "Kwana fa kace? Ana maganar wata fa kenan". Ta amsa da sauri.

      " A'a azizaty baki kaiba de".

      "Toh na lissafa ma?" Ta tambaya.

      "Eh lissafa". Ya amsa tare da tattaro attention d'insa kanta.

      Reyhana kuwa sosai ta fara lissafi tiryan-tiryan hadda yatsu a lissafin nata,yadda take lissafin ya bashi dariya sekace 'yar yarinya." Toh my azizaty na yarda". Ya fad'a.

      "Kaga harna 'kara kwana biyu akai ma". Ta fad'a.

      " Gaskiyarki uwargida". Ya fad'a cikeda zolaya.

      Kallonsa kawai tayi tana jiran mey ze ce akai."To shikenan ki shirya a week d'innan".

     "Toh Allah ya kaimu". Ta fad'a dukda ba haka taso ba tafi so yace ga ranar.

     " Ko bakya so mu bari wani watan? " Ya fad'a yana kallon reaction nata.

      "A'a inaso". Ta fad'a da sauri.

      " Sorry,da wasa nake". Ya fad'a yana mata murmushi.

       Haka suka kammala cin abincin,koda zata d'auraye kwanukan tare suka wanke.Bayan daya je sallar asr ya dawo nan suka cigaba da hirarsu.

      "Nikam yau baza ka duba takardun d'aliban naka ba ?" Reyhana ta tambayeshi kanta akan cinyarsa.

       "Azizaty yau banyi musu test ba ai". Ya amsa ta.

      " Ok toh ya school da students naka?"

      "Ba sau'ki nake fad'a mini,thank god ina da gimbiya mey sani farinciki".Cewar Ahmad yana shafa girarta.

       " Ayya My dear ". Ta furta.

            ****

2days later

      Reyhana  wajen 4:12pm bayan ta idar da sallah tana zaune sitting room tana kallon Bollywood sega Ahmad ya dawo daga masjid.

      " Sannu da dawowa". Ta fad'a.
    
        "Yawwa".

       "Azizaty ki shirya muje mu gaida mommy". Ya fad'a tare da zama gefenta.

     Da sauri ta kallo inda yake" Da gaske?"

       "Bakyaso ne?" Ya tambaya fuskarsa a sake.

       "Wane? Yanzu zan shirya". Ta fad'a tare da mi'kewa tsaye.

      D'aki ta shiga da sauri ta sauya kaya,lace tasa maroon da torches golden, se necklace nata golden me kyau,ta fesa turare me taushin 'kamshi gyalenta ta yafa golden ta zira flat shoe se purse data sa phone d'inta.Duk wannan shirin befi a 10min ba dan gani take lokacin kamar ze 'kare.

      " My dear am ready". Ta fad'a tana murmushi wanda har ha'koranta seda suka bayyana.

       "Iyye! Azizaty kamar wal'kiya har kin shirya?" Ya fad'a yana kallonta.

       "Eh na shirya". Ta amsa.

       " Zumud'i d'in kenan". Ahmad ya fad'a tare da mi'kewa.

    Bayan ya kashe TV d'in ya fito ,seda ta tabbata ta rufo ko ina tukun suka fito.

    Abin gwanin sha'awa da suka jero."Gaskiya next time zamu fita niqab zaki sa". Ya fad'a yana d'an 'bata rai.

     "Haba niqab ". Ta fad'a tana d'an turo baki.

     " Bakiga ana kallemin keba?" Ahmad ya furta.

     Shiru tayi bata ce komai ba ,napep ya tsarar masu suka hau.

      "Gaskiya na dad'e banga gari ba ji nake kamar na shekara". Reyhana ta fad'a tana kallon waje.

       " Just a month d'in ? Aiko ki saba ".Ahmad ya fad'a.

      A haka suna ta hirarsu har suka 'karasa gidan,Ahmad bayan ya sallami me napep d'in suka shiga ciki.Da Baba me gadi suka fara cin karo a gate ,ganin su ya washe baki dama shi mutum ne me barkwanci." Ahh yau Hajiya Amarya ce a gidan".Ya fad'a.

       "Baba ina wuni". Ta gaishesa.

     " Lafiya qalau Reyhana".Ya amsa.

     Ahmad hunnu ya mi'ka masa suka gaisa,daga nan suka shiga.Koda suka shiga makeken parlourn shiru kamar ba kowa,chan kuma bayan sunyi sallama sega Ikram 'kanwar Reyhana ta sakko "Laa! Yaya Reyhana dama kece ? "

     'Karasowa tayi da sauri inda take tana murnar ganin yayartata "Sannu da zuwa yaya". Ta fad'a tana murmushin jin dad'i.

     Itama Reyhana da farinciki fal a ranta take magana " Yawwa Ikram". Ta amsa.

      Tana ri'ke da hannunta suka zauna,Ahmad na d'ayan kujerar Reyhana kuma suna wata daban."Ya Ahmad ina yini". Ikram ta gaisheshi.

      "Lafiya lau Ikram, ya gidan?

      "Lafiya lau". Ta fad'a.

     " Bari na fad'a ma momy". Ikram ta fad'a tare da mi'kewa.

      Momy tana d'aki ta hakimce tana kallon TV Ikram ta shiga.

      "Mommy yaya tazo". Ikram ta fad'a.

       Mama da sauri ta d'ago kanta ta kalleta "Reyhana kuma da yammannan?" Mommy ta fad'a tana sake so ta tabbatar.

      "Da gaske Mommy tareda ya Ahmad ma take". Ikram ta amsata.

     Jin an ambaci Ahmad yasa Mommy ta had'e rai.Kamar bazata tashi ba ta mi'ke zuwa parlourn.
  
     Ahmad yana ganin Mommy ta 'karaso yayi saurin sakkowa daga kujerar." Ina yini Mommy ". Ya gaisheta.

      " Lafiya lau". Ta amsa ba wani walwala tattare da ita.

      "Mommy ina yini". Reyhana ma ta sunkuya ta gaidata.

     Bakinta a ta'be ta amsa wanda duk cikinsu ba wanda ya kula.Tana me mamakin yadda 'yartata ta tsunduma kanta a wannan irin rayuwar dan gani take kamar a takure take.

     Reyhana ce ta katse shirun da d'akin ya d'auka da tambayar" Abba be dawo ba ?"

 

1 / 21