Author : Dijensy Category : Romantic Hausa Novels
da d'aya.
2:45pm Saudat ta 'karaso gidan ,Reyhana tana d'aki tajiyo knocking d'inta da sauri taje ta bud'e."Besty!" Reyhana ta fad'a tare da hugging Saudat.
"K'awas kai nayi missing d'inki sosai sosai". Saudat ta fad'a.
" Toh mu 'karasa ciki". Reyhana ta fad'a tare da breaking hug d'in.
Sitting room tayi mata jagora suka 'karasa kowacce farinciki ya mamayeta."Amarya ashe zan sake ganinki".Cewar Saudat sanda suka zauna a kujera.
"Ke d'ince koyaushe sa rana kin kasa zuwa,ya su Mama". Reyhana ta tamaya.
" Duk lafiya suke,sunce a gaisheki".Saudat ta amsata.
"Bari ina zuwa". Reyhana ta fad'a tare da fita.
Abincin da sauran kayayyakin ta jero a tray ta kawo mata." Sakko ki ci se ai hirar".Cewar Reyhana.
"Ohni Saudat du ni kad'ai".
" Ehyi ke kad'ai.Ta amsa.
Sakkowa tayi ta fara da,suna d'an hira tana ci."Ya Mommy kuwa tazo". Saudat ta tamabaya.
"Ai Mommy har na fiddaran zuwanta har yanzu bata zo ba kuma Abba yana so zuzo amma shiru de,su Ikram de sunzo amma ko sisters d'in Mommy basu zo ba,na fad'a maki nifa bana ba'ki shiyasa kika ga ina azar'ba'bi kizo". Reyhana ta fad'a fuskarta na nuna tsantsar damuwa da hakan.
" Ayya 'kawata karki damu inshaAllah komai ze dedeta kiyi ta addu'a,amma kede kina waya da ita koh?" Saudat ta tambaya.
"Eyyi ina wayo dasu".Ta amsa.
" Toh hakan yayi kyau".Saudat ta fad'a.
Bayan ta gama cin abincin sega Ahmad ya dawo ,suna gaisawa da ita ya shige d'aki.
Ranar ta musu dad'i sunsha hira abinsu da selfie,se wajen 5:30pm Saudat ta tafi.
***
Gidan Mommy..
"Bafa inda zaki na fad'a maki". Mommy ta fad'a tana zaune kan sofa na parlour.
Walida dake tsaye ta yafa mayafi ita a lalle seta je gidan Reyhana.
" Mey ke faruwa ne?" Abba ya tamabaya sanda ya sakko 'kasa dan yajiyo d'aga muryarta.
"Abba dan Allah kace Mommy ta barni naje gidan Yaya". Ta fad'a kamar zatai kuka.
Abba Mommy ya kalla da ta 'kura wa TV ido kamar bata san suna gun ba." Mommyn Ikii ki barta taje mana".
"Na fad'a mata ba inda zata gara ma ta ha'kura". Mommy ta fad'a ba tare da ta kallesa ba.
Hakan da tayi ya 'kona masa rai." Walida jeki d'aki zan kira ki anjima".Abba ya fad'a.
Ba musu ta haye steps da sauri, Abba kuwa takawa yai ya 'karasa wajen Mommy ba tare da ya zauna ba yace"Bana son abinda kike yi taya ina maki magana ki kauda kanki ,kuma wannan yarinyar gidan yayarta zata meye aibu a ciki tunda ke kin'ki zuwa seki barsu su dinga zuwa bafa kya kyautawa yarinyarnan duk abinda ze faru ya riga ya faru kowa da kika gani bada arzi'ki aka haifeshi ba a duniya ya samu ki duba mana".
"Allah ya taimaka 'kofa ce a bud'e take sesi ta zuwa suke kwana ma". Mommy ta fad'a ta bar parlourn.
Abba yana tsaye ya kasa ta'bika komai wani hali sena Mommy sam idan taso tsiya sede ya rabu da ita.Girgiza kai kawai yayi" Allah ya sawwa'ke".Ya furta tare da barin parlourn.
Around 4:30pm Reyhana taji knock ya shigo,hijab ta zira ta tafi bud'ewa dan bata tunanin Ahmad ne.
"Abba!" Reyhana ta kira tana me mamakin ganinsa.
"Sannunku da zuwa ku 'karaso ". Reyhana ta fad'a ta bud'e'kofar widely.
Walida da sauri taje ta rungumeta,itama Reyhana haka suka shiga ciki.
"Ina yini Abba". Ta gaisheshi cikin rissinawa.
" Lafiya lau Reyhana ". Ya amsata.
Sageer dake gefe shima suka gaisa,se Walida dake manne da ita.
Allah ya taimaka tana da ragowar cake dayai saura jiya se exotic d'aya ta kawo musu da ruwa." Ikram da Bassam fah?" Cewar Reyhana tana kallon Walida.
"Suna gida su". Ta amsa.
Ba jimawa sega Ahmad ya dawo suka gaisa ya d'an zauna a sitting room d'in suna hira da Abba.
Da suka zo tafiya Walida tayi 'kememe baza ta bisu ba seta kwana.Ba yadda basi da ita ba " Walida ba'a taho da kayanki ba fah".Sageer ya fad'a.
"Abba ku barta ta kwana mana na kawota d kaina". Reyhana ta fad'a.
Haka suka ha'kura suka tafi ,Reyhana taji dad'i sosai ta samu 'yar hira.
***
Suna komawa gida Mommy tana parlour ita da su Bassam sun baje ice cream suna sha.
" Abba sannu da dawowa".Yaran suka fad'a.
"Ina Walidan kuma?" Bassam ya tambaya.
"Mun barta can ta nace seta kwana". Sageer ya amsa.
Mommy ko tanka musu batai ba,illa shan ice cream d'inta data cigaba.
Suma shirin sukayi Abba ya wuce d'aki Sageer ma sashensa ya wuce.
***
Walida kwai surutu har Maghreb tana hira da Reyhana daga baya ta 'karbi wayarta ta fara game. Reyhana se lokacin ta shiga kitchen girki dama kuma taliya zatayi jollof.
Ahmad kuma ya tafi masjid har lokacin be dawo ba.Tana kammalawa ta ziba musu ,suna cikin ci ya dawo.
" Sannu da dawowa".Reyhana ta fad'a.
"Yawwa".ya amsa yana 'ko'karin zama kan kujera.
Ita ma walidan sannu da dawowan tayi masa ta cigaba da cin abincin.
Reyhana tashi tayi ta zubo masa nashi shima tukun ta cigaba da ci tana mata labarin makaranta.
Wajajen 9:30 Walida ta soma gyangyad'i ,d'akin gado ta kwantar da ita kamar yadda Ahmad ya bu'kata shi seya kwanta a sitting room.
Chan cikin dare aka d'auke light gashi weather d'in da zafi kad'an Walida ba son zafi take ba tuni ta farka.
Ga mosquito net shiyasa ta takura,Reyhana fifita ta hau yi mata sannan ta koma, ita kuwa Reyhana se wajen 4:14pm ta koma bacci.
Ahmad koda ya tashi asubah kamar ko yaushe ya tashi Reyhana ya fita.Rashin bacci da bata samu ba yasa ta koma ba tare da ta ankare ba.
Koda ya dawo 6:48am ya tarar bata tashi ba seda ya sake tayar da ita,da sauri ta mi'ke ganin hasken gari.
" Ya salam!" Ta furta.
"Tabb! Kice baccin kika koma har 7 ya kusa fa". Ahmad ya fad'a.
Da sauri ta shige toilet tayi alwala sannan tayi sallah,nan ta yaye net d'in ta tashi Walida da 'kyar dan akwaita da nauyin bacci.
Kafin nan 7:15am yayi, data fito ta tarar ya d'ora ruwan tea hakan ya nuna ya sauke ma na wankan.
Kitchen d'in ta shiga tana tunanin abin breakfast dan potatoes ya 'kare gashi doya ma baze ishesu ba dan kad'an ya ragu ,tuna tana da flour kawai ta fere doyan nan da nan ta soya da ragowar egg dan shima yazo 'karshe.
Flour d'in kuwa ta kwa'ba fanke nan da nan tunda garin da d'an rana.
Doyar ta d'iban masa ta had'a tea ta kaimasa ,sauri-sauri yayi breakfast d'in dan yayi late 7:39am ya fita.
Ragowar doyar ta bawa Walida ta had'a mata tea tasha, ita kuwa seda ta jira ya tashi fanken ta soya taci. Kafin tayi breakfast tayi shara ya rage wanke-wanke da sauran ayyuka.
" Walida a ajje game d'in ga ruwan wanka na had'a maki".Reyhana ta fad'a sanda ta shigo sitting room taga tana ri'ke da wayarta.
"Yaya bari na fad'i sena ajje". Walida ta fad'a hankalinta na kan wayar.
Reyhana murmushi kawai tayi a ranta tana fad'in" Yarinya baki da damuwa".
Wajen 12:00pm ta gama shirinta gida yayi tsaf,saura girkin rana kuma.
Shinkafa da miya ta dafa dan kayan abinci sunyi 'kasa shinkafa ce ta ragu da taliya rabin carton ,se sauran kayan alatun d'and'ano dama kayan gara ne da aka had'ota dasu yanzu kuwa sun kusa 'karewa,gashi har wata ya 'kare ba'a biya albashi ba.
***
Yau Anty Asma'u tazo gidan Mommy nan take fad'a mata Walida tana gidan Reyhana.
"Ai yau d'innan Sageer ze d'akko ta". Mommy ta fad'a.
" Tana wani d'okin gidan Amarya ba uwadda zasu bata se shinkafa".Mommy ta fad'a.
"Hmm yaro kenan ita a jinta za'a had'ota da kayan 'kwalama.Anty asma'u ta fad'a.
Sageer yana jinsu shi haushi hirar take bashi ,besan lokacin da zasi dena aibata Ahmad ba sam basa ta'ba yabarsa.
" Sageer anjima kaje ka d'auko yarinyar nan kajini ko".Mommy ta fad'a.
"Mommy ku barta mana". Ya fad'a.
"An'ki d'in kana kallo yau da akwai school amma Abbanka ya 'kyaleta saboda sangarta". Mommy ta fad'a cikin fad'a.
" Toh ai gobe Saturday ".
" Seta je islamiyya ,na fad'a maka anjima zaka d'aukota".Ta fad'a.
Daga haka be sake cewa komai ba sema d'akinsa daya koma.
***
Reyhana wajen Asr suna zaune da Walida akai knocking.Walida da sauri ta tashi ta bud'e 'kofar."Kai ya Sageer meye na zuwa d'in". Ta fad'a tana turo baki.
Ciki ya 'karaso ita kuwa Walida kamar zatai kuka nan danan ta zauna gefe guda tana turo baki.
"Kai Sageer da wuri haka, ni na zaci koh kayanta ta kawo". Cewar Reyhana tana d'aga labilen d'akin.
" Mommy ce ta takura sena d'akkota". Sageer ya fad'a.
"Kaji Mommy, wai dan Allah meyasa ta'ki zuwa ko su Anty Asma'u ai sa zo sekace banida dangi har kunya nake ji". Reyhana ta fad'a tana nuna alamar damuwa.
" Tana gida na barota ma Anty Asma'un".Sageer ya fad'a.
Tashi tayi ta kawo masa ruwa da zo'bon data had'a d'azu.
Yana zaune Ahmad ya shigo, shiru tayi batace komai ba dan taji ba dad'i be dawo da wuri ba kuma be kirata ba.
Koda suka gaisa da Sageer d'aki ya bita dan yaga mood nata ya sauya.
"Azizaty mey nayi". Ya tambaya.
Shiru tayi masa harta d'auki abinda zata d'auka saboda haka ya shige toilet ya watsa ruwa.
A sitting room kuwa alewoyi da chewing gum da Saudat ta kawo mata ta bawa Walida. Ba dad'ewa yasa kaya ya fito.
" Sageer bade tafiya ba". Cewar Ahmad.
"Gobe da islamiyya ne". Ya amsa.
" OK".Cewar Ahmad.
Har mota Reyhana suka rakasu sannan suka dawo ciki.
AR²💖
*Need you warm comments,vote and shares.*
Jasko💕
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 0⃣5⃣
Koda suka komo ciki bata yi masa magana ba illa zama a kan kujera data yi ta shiga latsa waya.
Zama yayi kusa da ita yace "Azizaty mey nayi?" Ya tambaya.
Shiru tayi bata ce komai ba.
"Please say something ko naji sanyi my Azizaty".
Yanda yayi maganar yasa ta kusa dariya amma seta maze ta cigaba da kallon waya.
" Ayya azizaty inde dan ban dawo da wuri bane ina me neman afuwa ,dubiya muka je da abokaina wayata kuma ba charge shiyasa ban kira ki ba". Ahmad ya fad'a.
"Toh amma kasan zan damu dayawa aikoh da seka kirani da wata wayar". Cewar Reyhana cikin shagwaba.
" Sorry my Azizaty next time haka bazata faru ba kinji".
Kai kawai ta kad'a bata ce komai ba.
"Kin ha'kura?" Ya tambaya tare da tallafo ha'barta.
"Smile my one and only always and forever". Ya fad'a.
Hakan yasa ta saki murmushi ,shi kuwa hugging d'inta yayi tightly " I love you Azizaty.Ya furta
"I love you too dear". Ta fad'a itama ta sake 'kan'kameshi.
***
Ta 'bangaren Mommy kuwa Walida bayan sun koma take nuna wa Ikram alewar da Reyhana ta bata.Mommy ta'ba baki tayi dan tana zaune a palour.
" Wai sunan gidan Amarya aka je shine aka 'kare da wannan mtchhwww!" Mommy ta fad'a tare da tsaki.
Ita Walida bata ji me Mommy tace ba amma Ikram taji tayi gum da bakinta.
Washegari...
Kasancewar weekend Ahmad yana gida throughout be fita ba ,suna sitting room abunsu suna kallo a TV Reyhana ta d'ora kanta a cinyarsa.
Wayar Reyhana ce tayi ringing hakan yasa ta tashi,koda ta duba taga Mommy bayan sun gaisa Mommy take fad'a mata bikin wata cousin tasu Reyhana da za'ai.
"Mommy kisa Ikram ta kawo min invitation dan Allah". Reyhana ta fad'a.
" Idan ba'a kawo ba kenan bazaki jeba?" Mommy ta tambaya.
"A'a ba haka nake nufi ba wai da sena bawa ya Ahmad na d'aurin aure".Reyhana ta fad'a a sanyaye
" Bikin danginki ake ko nashi? dole seya je?" Mommy ta tambaya cikin fad'a.
Allah yasa lokacin Ahmad ya fita daga d'akin da ze iya ji.
"Eyyi baki amsan ba". Cewar Mommy.
"A'a ,toh Mommy Allah ya kaimu"Reyhana ta fad'a kwalla na cika a idanunta.
Daga haka sukai sallama gefe ta ajje wayar takaici ya isheta.Furucin Mommy ya bugi zuciyarta sosai taji ba dad'i koyaushe bata da buri irin Mommy ta dena tsanar mijinta ita da danginta."ko su Mommy basu kawo IV ba ai gidansu Amaryar sa kawo".Abinda ta fad'a a ranta kenan.
Tana cikin wannan batunne sega Ahmad ya shigo da sauri tayi 'ko'karin saita kanta karya gano wani abun.
" Da Mommy kikai waya?" Ya tambaya.
"Eh tana gaisheka".Reyhana ta fad'a.
Toh ina amsawa". Ya fad'a.
" Dama maganar biki ce ranar alhamis za'a fara". Reyhana ta fad'a.
"Ok toh Allah ya kaimu". Ahmad ya fad'a ba tare da ya sake cewa komai ba.
" Ranar friday d'aurin aure kuma". Ta fad'a.
Nan ma Allah ya kaimu yace.Reyhana a zuciyarta haushi ya mamaye dabadan ba da ba abinda zesa ta fad'a masa zancen d'aurin auren dande karya fuskanci ko da wani abun.
Haka abubuwa suka cigaba da gudana an biya Ahmad albashi ya d'anyi musu 'yar siyayya ta kayan tea da sauran 'yan abubuwa haka Umma ma.
Yau take alhamis ranar kamu,Reyhana ba ita ta shirya ba se 4:30pm ,su Mommy kuwa su ajinsu ko zata je da wuri gidansu Amarya idan yaso lokacin kamun yayi se a rankaya a tafi amma suka ji shiru.
Da Ikram tace zata kirata Mommy ta hana ta.Wajajen 5 kowa ya hallara hatta Amarya tazo waje ya cika ana shagali mutane dayawa suna tambayar Reyhana Mommy har ta gaji da cewa tana hanya.
Reyhana ba ita ta 'karaso ba se 5:35pm saboda yanayin hanya.Walida ce ta hangota da sauri ta 'karasa gunta.
Mommy tana zaune kan kujera suna gaisawa da wasu ta hangesu suna 'karasowa.Tun daga nesa Mommy take hararar Reyhana har ta 'karaso.
Seat ta samu ta zauna ta gaisheda mutanen wajen sannan Mommy da ta gama 'kulewa.
"Ina wuni Mommy". Ta gaisheta.
" Bansani ba,sannunki da 'ko'kari kowa ya gama hallara banda ke se tambayarki ake harna gaji da yin magana,kin kyauta kenan?" Mommy ta fad'a rai a 'bace.
"Mommy naga wai da yamma ne". Cewar Reyhana.
" Ke a matsayinki yaci ace se yamma zaki zo sekace ba 'yar uwakki ba".
Ai Mommy tana cikin yi mata fad'a sega Anty Asma'u itama ta fara zazzaga mata nata,Reyhana jitai bikin dama bata zo ba gashi ba abinda ya sake ci mata rai irin yadda rashin zuwan nata ya shafi Ahmad. Shi suka koma blaming suna cewa "Watoh shi kulle yake seya ga dama zaki fito". Mommy ta fad'a.
'Kila ma seda ta gama yi masa girki". Anty Asma'u ma ta fad'a.
Wani zazzafan hawaye ne ya sakko mata ,Allah sarki Ahmad abinda shi ke ta tuna mata tayi sauri ta shirya yamma nayi shine aka la'kaya masa abinda beba.
Ganin ta fara hawaye yasa suka rabu da ita karta tara musu dangi dan idan ta fara kuka ba kanta,kowa seya san tana yi.
Reyhana ko hoto da Amarya batai ba tana zaune gu d'aya Ikram ce daga baya tazo take bata ha'kuri dan su Mommy sun tashi daga gun.
Ganin Maghreb na shirin yi yasa ta tashi,zuwa tayi har inda su Mommy suke tayi musu sallama ta tafi duk cikinsu ba wanda yai maganar tafiyarta da wuri.
Mommy basu suka tafi ba se wajen 9:00pm.Aiko Walida bayan sun koma gida suna shiga ta nufi Abba da suka tarar zaune parlour.
" Abba kasan mey Mommy sukai wa yaya?" Cewar Walida.
"A'a Walida sekin fad'a". Abba ya fad'a tare da tattaro attention kanta.
" Wlhy kuka tayi suna mata fad'a". Ta fad'a harda zaro ido.
Mommy kuwa da tin shigowarsu suka haye sama ita da Ikram dan a gajiye suke.
"Da gaske Babyna?" Abba ya tambaya yana son sake tambatarwa.
"Da gaske nake Abba ka tambayi Ikram ma kaji hadda Anty Asma'u sukai ta mata.." Bata 'karasa ba Abba ya katseta.
"Ya isa aje a kwanta dare yayi kinji". Cewar Abba yana lalla'bata.
Kan kice me ta haye sama abinta Abba kuwa ya shiga tunanin abinda sukaima Reyhana.
Ita kuwa Reyhana sanda ta koma gida Ahmad ya kula da yanayinta amma seta ce ciwon kai take ji.Ko abincin dare bata iya girkawa ba dama akwai ragowar na rana suka ci suka kwanta.
Washegari da safe kasancewar d'aurin auren 11am ne Reyhana da kanta tace wa Ahmad ya ha'kura da zuwa tinda yana da makaranta,ko ba dan haka ba dama bata so yaje dan tana gudun kar a wula'kantashi.
Ita kuwa sunyi dashi zata tafi gidan bikin 12pm amma yana fita ta dawo tayi kwanciyarta koda ta farka aikace-aikacen gidanta tayi ta d'ora girkinta.
Mommy kuwa suna can ana ta hotunan d'aurin aure ,gefe guda ta ware tayi dialing number Reyhana.
" Reyhana lafiya baki zo ba?"Mommy ta tambaya.
"Na tashi banda lafiya ne".Tayi 'karya harda narke murya.
" Bakida lafiya? Har ankon dinner gashi kuma anyi miki".Mommy