Author : Dijensy Category : Romantic Hausa Novels
Gidansu Reyhana kuwa shiru kukeji kowa yana d'aki dan koda Abba ya dawo Sageer ya zayyane wa Abba komai dan yana jiyo Mommy da Ahmad.
Abba ransa a 'bace ya shiga d'akinsa jira yake gobe tayi ya shawo kan matsalar(Hmm😶).
Reyhana da dare yayi ko bacci ta kasa gashi Nasser tana ta mata kuka koh cikinta yake ciwo ,ita kad'ai take ta lallashinta amma ta'ki shiru hakan yasa itama Reyhana ta taya ta sukaita kuka bame rarrashin kowa.
Ahmad ko gidansa be koma ba yana parlourn Umma sallah yayi koh abinci ya'ki ci tunanin Reyhana da Nasreen kawai yake.
***
Washegari da safe Umma tun asubah bata koma ba ,shiko Ahmad dama jiya beyi wani bacci ba sallah yayi yaita adduo',ise around 4:30am bacci yai gaba dashi.
Tun bayan sallahr Asubah be koma ba dukda kuwa baccine a idanuwansa.
Umma around 8am ta tafi gidansu Reyhana dan hankalinta ya kasa kwanciya,inno ce tayi mata iso.Nan inno taje ta sanarwa da Mommy ,ba dad'ewa ta sakko 'kasa.
Sama-sama ta gaisa da Umma dama tasan meke tafe da ita.
"Mommyn Reyhana meyai zafi haka...". Ko 'kare maganar batayi ba Mommy ta katseta.
" Duk wani abu da zan fad'a na riga na fad'a wa Ahmad saboda haka banga amfanin dawo da zance baya ba".Cewar Mommy ba ko damuwa a tare da ita.
"Ehyi nasan da haka amma dan Allah ki tausayawa yaranannan ki bashi dama ,Ahmad rabuwa da Reyhana matsala ne a gunsa abune me wuya". Umma ta fad'a cikeda tausayawa.
" Itama Reyhana zama dashi abune mey wuya a gunta damu kanmu baza muso ta shiga 'kuncin rayuwa ba".Mommy ta fad'a.
"Dan Allah kiyi ha'kuri ki bar maganar nan". Umma ta fad'a.
Mommy ta 'kosa sosai dan ta fara kad'a 'kafa komai ze iya fitowa daga bakinta.
" Nifa yanzu takardarta nake jira bana san sake jin komai".Mommy ta fad'a.
"Baze sake tan ba".Abba ya fad'a.
Dama ya gano sanda Umma ta shigo gidan a d'akinsa.
" Kiyi ha'kuri Umman Ahmad inshAllahu ma yau zan maido da ita gidanta da kaina.Abba ya fad'a.
"Ba inda zata je, ta gama zaman gidan Ahmad". Mommy ta fad'a.
Umma da take zaune ta mi'ke tsaye taga abun ba na zama bane.
Itako already Mommy tun sakkowar Abba ta mi'ke tsaye.
Ikram datake shirin sakkowa ta hangi abinda ke faruwa dan haka ta shiga d'akin Reyhana da sauri ta fad'a mata.
" Yaya Umman Ahmad tazo ,kinga Abba ma ya fito suna magana Mommy kuma...".Bata 'karasa ba tayi shiru.
Reyhana ko bata fad'a ba ta gano inda ta nufa,da sauri ta tashi zuwa parlour.
Daga can gefen bene suka tsaya itada Ikram suna kallon ikon Allah.
"Ni na fad'a a yau seta koma gidanta". Abba ya fad'a cikin d'aga murya.
" Ba inda zata je".Cewar Mommy.
"Dan Allah ayi ha'kuri". Umma ta fad'a.
Da ace tasan hakan abin ze kaya da bata zo ba,dan haka tayi ta basu ha'kuri.Suna kallo ta fita daga gidan,su kuwa basu fasa ba.
" Ke kike da iko da ita koh ni?"Abba ya fad'a.
"Bani bace,kayi yanda kake so kaji". Mommy ta fad'a cikin fushi.
" Kece kuwa ? ".Abba ya tamabaya .
Yana mamakin yadda ta sauya ,yasanta da zafi amma ba irin haka ba ace yau har a gaban sirika yana fad'a tana fad'a.
Yana cikin wannan batun Mommy tayi wucewarta ta haye sama yaran suna kallo.Sageer da se lokacin ya fito daga d'akin ,wajen Abba Reyhana ta 'karasa tana basa ha'kuri ,ba abinda yake illa jinjina kai.
" Mommy ina zaki je?" Suka jiyo muryar Walida da ta biyo bayan Mommy.Wani irin shock gabaki d'ayansu suka ji ganin Mommy tana sakkowa da trolley.
Ta yafa gyale ga takalmi data saka hannunta key na motarta,hakan ya bayyana tafiya zatai.
"Mommy?" Reyhana ta furta cikeda mamaki.
Har gabansa ta 'karaso ba tare da ta kalli yaran ba tace."Sanda kaga bana nan seka tabbata nice,ga yaranka kaine kake da iko dasu".Mommy ta fad'a fuuu ta wuce.
AR²💖
Jasko💕
Pls share.
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 1⃣6⃣
Gabaki d'aya yaran da sauri suka 'karasa wajen Mommy da ta kusa kaiwa 'kofar fita.
"Mommy dan Allah karki tafi ki barmu". Walida ta fad'a tana ta'be baki zatai kuka.
" Mommy please kar kiyi haka".Reyhana ta fad'a ta ri'ko hannun Mommy.
Se lokacin ta kalleta ,Sageer ma 'karasowa yayi.
Mommy dan Allah ".Ya fad'a muryarsa a raunane.
" Sakeni".Mommy ta fad'a tana mata wani kallo.
Reyhana a hankali ta sauke hannunta dan tasan duk dalilinta hakan ta fara.
Suna ji suna kallo ta fita ,Walida take ta buga 'kafa tana ta kuka tana kiran Mommy.
Abba da tun d'azu be kalli inda take ba duk da kuwa abun ya damesa sosai ,seda yaga ta fita ga Walida tana kuka.Fita yayi ,yaran zasu biyosa yace su tsaya.
"Maryam". Abba ya kira sunanta.
Yana 'karasawa inda take ya fisge trolley d'in daga hannunta.
" Mey kike tunanin yi? Idan kin tafi ina zaki je"?" Ya tamabaya.
"Gidan kawu na". Ta amsa.
" Ki shiga ciki nace".Abba ya fad'a yana nuni da 'kofa.
"Kusha zaman ku kaida yaranka muddin baze saketa ba ni kuma bazan dawo gidannan ba". Ta fad'a.
" Adalci kenan ,ki raba auren yarannan?"
Shiru tayi bata ce komai ba tana tsaye ita bata shiga motar ba kuma bata koma ba.
"Ki duba kiga yarannan,haka zaki tafi ki barsu wani hali zasi shiga? Abba ya fad'a a sanyaye.
" Nide na fad'a maka muddin na koma toh seya saketa".Mommy ta fad'a.
"Muje ki shiga ciki". Abba ya fad'a.
Tana huci tabi bayansa yaran suna kallo ta shigo da sauri suka je wajenta.
Reyhana kuwa komawa tayi d'aki jiki a sanyaye. A zuciyarta tana tunanin mafita " Yanzu a kaina yau Mommy take 'ko'karin barin gidannan!" Reyhana ta fad'a a zuciyarta hawaye na gangarowa a idanuwanta.
***
Umma tana komawa gida Ahmad ya 'karaso inda take.
"Umma ta ha'kura Mommyn" .Ya tambaya muryarsa a raunane.
Kallonsa kawai tayi amma ta kasa cewa komai.
"Umma ki fad'a min". Ya fad'a.
" Ahmad sede mu cigaba da addu'a ,Mommyn ta ta'ki amincewa mahaifinta ne de ya goyi bayanta ba". Umma ta fad'a.
Labarin duk abunda ya faru ta zayyane masa,hannu yasa ya dafe goshi kansa yana sarawa.
"Ha'kuri zakai Ahmad duk abinda kaga ya faru Allah ne ya tsara". Umma ta fad'a.
Seda tayi da gaske yaci abinci kad'an koh fita ya 'kiyi,wayarsa ya d'auka bayan yayi sallahr zuhr yayi dialing number na Reyhana.
Seda ta kusa katsewa tayi picking.
" Reyhana ".Ya kira sunanta.
" Uhmm".Ta amsa dan idan tayi 'kwakkwarar magana kuka zatai.
"Reyhana dan Allah karki rabu dani ,bazan iya zama bake ba ina 'kaunarki Reyhana". Ya fad'a muryarsa na rawa.
Jin haka yasa ta shiga kukan da take dannewa." Ahmad taya zanso na barka kaima kasan bazan so na rabu da kai ba".Ta fad'a.
"I know Reyhana". Ya fad'a.
" Yaya ina tsoro".Ta fad'a.
"Reyhana inshaAllah muna tare". Ya fad'a duk da kuwa zuciyarsa ta karaya.
Labarin abunda ya faru bayan tafiyar Umma ta basa, hakan ba 'karamin tsorata sa yayi ba.
" Yaya bazan iya bari Mommy ta bar Abba a dalilina ba".Ta fad'a.
Kai kawai ya kad'a kamar yana kusa da ita,sun d'au lokaci kafin Ahmad ya sake magana.
"I love you so much that I can't afford lose you Azizaty".Ya fad'a.
" Idan na rabu dake ya zami da Nasreen ? Reyhana I can't do this".Ya fad'a zuciyarsa na sake karaya.
Kud'in wayar ne da suka 'kare yasa basu cigaba da magana ba ,Reyhana wani sabon kukan ta soma yi Allah yasa Nasreen bacci take.
Kowa rayuwar ta'ki masa dad'i ,dukansu sun shiga damuwa gashi idan yaje gidan baya samun ganinta yanzu Mommy ma wayar ma so take ta hana su kuma.Reyhana jikinta yayi sanyi dan bata jin zata iya bari a dalilinta Mommy tabar gidan dan haka yanzu tana ganin zatace wa Ahmad ya bata takardarta muddin hakan ze dawo da faruncikin Mommy.Dan yanzu Mommy bata wani sakkowa 'kasa idan kuwa Abba yana parlour bata zama.
Ahmad koya kira Mommy ya sake ro'konta bata picking call d'insa sede yayi ta tura mata text amma kamar bayi yake ba.
Reyhana tana d'aki tana shirya Nasreen Ahmad ya kira ,wani tausayinsa taji dan yau kusan kwana biyu Mommy ta hanata picking call d'insa.
"Reyhana". Ya kira sunanta bayan ta d'aga.
" Yaya".Ta kira sunansa itama.
"Are you OK?" Ya tambayeta.
"No am not". Ta amsasa idanuwanta na tsiyayar hawaye.
" Reyhana ki dena kuka please ".Ya fad'a
Bata 'kara magana ba sega Mommy ta shigo.Wata uwar harara Mommy ta watsa mata dan haka ta katse wayar.
Mommy 'karasowa inda wayar take ta d'auka tayi switching off ba tare da tayi magana ba ta fita.
An d'au kusan month da arba'in ,ba abunda ya chanza Mommy haryanzu tana kan bakarta dan yanzu ta gaji da zama a haka da ake so take Ahmad ya rubutowa Reyhana takardarta.
Da kanta yau ta d'au 'kafa taje gidansu Ahmad,Umma kad'ai ta samu a gidan.
Bayan sun gaisa Mommy take fad'a mata abinda ya kawota.
" Mommyn Reyhana ba wanda yasan gobe gabaki d'ayanmu,shiyasa nake ro'konki da ki sake bashi dama ko ze samu wani aikin".Umma ta fad'a.
"Umman Ahmad banzo nan ba dan mu sake tattaunawa akan maganarnan ba ,takardarta nazo kar'ba".Mommy ta fad'a.
Hakan ba 'karamin 'konawa Umma rai yayi ba ,tasan ta d'areta nesa ba kusa ba danma bata haifi Ahmad da wuri ba amma shine take mata irin wannan maganar cikin kakkausan harshe sekace 'yarta ko si'arta.
" Amma yanzu de ai kinga yaron baya nan koh?" Cewar Umma.
"Toh ai shiyasa na zo sanar wa da mahaifiyarsa wata'kila koya rubuta". Mommy ta fad'a.
" Shikenan inde takardarta ce ze kawo mata da kansa".Umma ta fad'a ranta a 'bace.
Tashi tayi Mommy ta fita disappointed dan taso ace Ahmad yana nan.
Umma kawai bin bayan ta da kallo tayi ta girgiza kai.
Ahmad yana wajen aikinsa amma hankalinsa yana gun Reyhana baida tunani sai nata.
Wajajen 4pm Ahmad ya shigo gidan dan yanzu kusan koyaushe yana gidan kwana ne yake maidashi gidansa.
Umma seda taga ya kammala cin abincin sannan tayi masa maganar zuwan Mommy.
"Ahmad yaushe zaka bata takardarta?"Umma ta tambaya.
"Umma ya kike fad'an haka?" Cewar Ahmad.
"Kai baka gaji da wannan abun ba ,lokaci yayi da zaka ha'kura Ahmad babu yanda zami da 'kaddara". Umma ta fad'a.
" Umma saki fa ba abune mey sau'ki ba".Ahmad ya fad'a.
"Ka fiso a cigaba da zuwa ana cimin mutunci ko,har yanzu baka gaji da wula'kanci ba? Kokuwa so kake se an kai maganar kotu?" Cewar Mommy, daga yadda take maganar ya gano tana cikin 'bacin rai.
"Umma mey tace miki?" Ya tambaya lokaci guda zuciyarta ta fara tafasa dan zaey iya jure komai amma banda wulan'kanta mahaifiyarsa
"Jin mey tace mini ba shine ba kawai kayi ha'kuri ka sawwa'ke mata kowa ya huta". Umma ta fad'a.
Kai kawai ya kad'a ba tare da yace komai ba ya fita.
Gidansa ya nufa,d'akinsu ya shiga ya bud'e wardrobe d'in wasu kayan Reyhana da bata tafi dashi ba ya d'auka yana sha'kar 'kamshin turarenta ,take hawaye ya gangaro fuskarsa.Tun farkon had'uwarsu da ita ya tuna da auren su,sanda tana laulayi,da tafiyarta gida.
" Shine 'karshen zamanta a gidana kenan?"Ya tamabayi kansa.
Tuna maganar Umma da yayi yasa ya janyo drawer ta gadon ,takarda da biro ya d'akko ,se 'karewa takardar kallo yake a zuciyarsa yana jin nauyin rubuta mata saki.
Ya shafe kusan 20min kafin ya d'ora biro a kai.
Ni Ahmad Yusuf, yau laraba ././... Ya rubuta date.Na saki mata ta Reyhana saki d'aya.
Yana gama rubutawa yai folding d'inta.
Seda yasha kukansa tukun ya fito daga gidan,be tsaya a ko ina ba se gidansu Reyhana. A 'kofar gida ya tarar da Sageer ,cikin mutuntawa suka gaisa ya mi'ka masa takardar dan bayajin zai iya bata hannu da hannu.
Yana bashi ya tafi,shikanshi Sageer jiyake kamar yai kuka.Ko ba'a fad'a ba yasan mene,a d'aki ya isketa tana ta lalla'ba Nasreen tayi bacci.
Ganin Sageer 'ki'kam a tsaye ya kasa magana amma fuskarsa da damuwa.
"Sageer meya faru?" Ta tambaya.
Takardar ya mi'ka mata ba tare da yace komai ba ya fita.
A sanyaye ta bud'e takardar gwiwarta tayi sanyi...
AR²💖
Jasko💕
Pls share.
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 1⃣7⃣
Safar da take hannunta ta Nasreen ta saki a 'kasa,kukan ma ta kasa.
"Ahmad ya sakeni?" Abinda take ta nanatawa kamar zautacciya.
Kuka mara sauti ta soma,ita kuwa Nasreen se wuri wuri da ido take tana d'aga 'kafafuwa sama.
Ahmad kuwa daga gidansu Reyhana gidansa ya koma yai zaman dirshan ,hotunan bikinsu ya d'auko yana ta kalla harda murmushin yake.
Umma tayi tsammanin dawowarsa amma taji shiru,da ta kira wayarsa a kashe taji dan kuwa baya son jin kowa komai kawai yafison ya zauna shi kad'ai.
Mommy da maghrib bayan tayi sallah ta shiga d'akin Reyhana lokacin tana toilet.Har zata fita ta hangi takardar a kan gado.
A hankali ta 'karasa ta d'auka,koda ta karanta wani sanyi taji ya ratsa ta a zuciyarta tace"Alhamdulillah,an rabu da 'kaya".
Hannunta ri'ke da takardar Reyhana ta fito fuskarta ba annuri da ka ganta za kasan tana cikin damuwa.
Mommy ita kanta rasa abinda zata ce mata tayi dan tasan a wannan lokacin tana tare da 'bacin rai saboda haka Mommy ta ajje takardar ta fice.
Abba kuwa da ya dawo Mommy ko kunya haka ta shiga d'akinsa ta sanar masa.
"Toh yanzu hankalinki ya kwanta koh?" Abba ya fad'a
Mommy shiru tayi bata ce komai ba se turo baki datai a zuciyarta kuwa tana mey jin dad'i.
Ahmad se wajen 10:30am tukun ya koma gidan Umma da hankalinta ya tashi.
"Kai kuwa ina ka shiga ina kiranka a kashe wayar?" Umma ta tambaya.
"Naje gida neh". Ya amsa ciki ciki.
" Du ka tayar min da hankali". Umma ta fad'a.
"Kiyi ha'kuri". Ahmad ya fad'a.
" Abinci fa?" Ta tambaya.
"Na 'koshi ". Ya amsa ya shige d'aki.
Kai kawai ta girgiza ta koma d'aki.
Daren ranar daga Reyhana har Ahmad ba wanda ya iya bacci,daga ya fara gyangyad'i seyai mafarkin Reyhana tana kuka a firgice yake tashi.
***
2weeks later
Mommy itada Anty Asma'u sukaje gidan Ahmad suka sa aka kwaso kayanta ,dama kud'in hayar ya kusan 'karewa dan haka suna kwashe kayansu Ahmad ya dan'kawa mey gida gidansa.Shi kuwa ya komo gidan Umma.
9:46pm yana rigingine ya 'kurawa ceiling ido yana tuna last maganar da sukai da Reyhana a waya.
** Waiwaye**
" Reyhana am so sorry, I have no choice ".
" Yaya na fahimta,stop apologizing ".Reyhana ta fad'a.
"Wannan itace 'kaddararmu". Ahmad ya fad'a.
Da'kyar ya iya rintse idonsa ba isashshen bacci yake ba yanzu.
Mommy kuwa abin Reyhana ya fara isarta tun sanda Ahmad ya bata takardar ta ta dena sakin fuska ,fitowa parlour ma wataran se a wuni bata fito ba.
Tana gyara gado dan shirin kwanciya Mommy ta shiga d'akin.
Waje ta samu ta zauna,bayan data d'auki Nasreen da har lokacin idonta biyu.
" Reyhana ".Ta kira sunanta.
" Uhm".Ta amsa tana cigaba da abinda take.
"Reyhana saboda nasa Ahmad ya rabu dake shine bakya son yi mini magana?" Cewar Mommy.
"Mommy ba haka bane".Ta fad'a tabar abinda take.
" Toh yayane?"Mommy ta tambaya.
'Karasowa tayi kusa da Mommy ta zauna gefen gado ta zauna opposite da Mommy.
"Mommy taya za'ai na'ki yi miki magana akan haka". Reyhana ta fad'a.
"Toh ya akai kin chanja bakya shiga cikin 'kannanki ko abinci ma bakya ci damu kinga dole nayi tunani ko kina gab..". Mommy bata 'karasa ba Reyhana ta katse ta.
" Mommy kidena fad'in haka,dan Allah kiyi ha'kuri amma banyi hakan dan na 'batamiki ba ,na bari ".Reyhana ta