Author : Dijensy Category : Romantic Hausa Novels
ta wuce d'aki.Bayan maghrib ta kira Reyhana ta fad'a mata taje gidansu Ahmad.
"Reyhana kema nasan kina..." Bata 'kare ba ta katseta.
"Mommy komai ya wuce dama Allah ya riga daya tsara ba yadda zami ,ki dena tunanin wani abu".Reyhana ta fad'a.
" Toh Nasreen fa zaki fad'a mata yanzu? "Mommy ta tambaya.
" Mommy ni ina ganin a bari nan gaba da kanta zata fahimci hakan".
"Idan yayi aure kina ganin baze kar'bi 'yarshi ba?"
"Mommy ya za'ai ya d'auke ta ,ni bazan yarda ba gaskiya".
" Toh ya zakiyi za'a cigaba da zama a haka ne?,kema wataran ai auren zaki ko wane namiji ne ze ri'ke 'yar da ba ta shi ba?"
Shiru tayi batace komai ba ta tur'bune fuska dan bata so taji ana maganar rabata da Nasreen d'inta.
"Baki ce komai ba?" Mommy ta fad'a.
"Toh Mommy ai bece ze kar'beta ba".
" Lokaci na zuwa,Ummansa ta nuna min wacce ze aura". Mommy ta fad'a.
Wani iri taji jin abinda Mommy ta fad'a, abu de yana shirin tabbata, gaske ne abinda take tsammani Ahmad Zainab ze aura?"
"Kema ya kamata ki kira Umman tashi ki bata ha'kuri ". Mommy ta fad'a.
Se lokacin ta bar tunanin da take ta amsa da " Toh".
Har bayan ta koma d'akinta bata dena tunanin abinda Mommy ta fad'a mata ba.
°°°
Bayan fitar Mommy daga gidan Umma take tambaya Ahmad shirye-shiryen biki ,shi sam baya so take tuna masa.
Duk abinda ta tambayeshi "uhm" kawai yake ce mata, ganin Mommy yasa ya sake karkata wajen Reyhana yana ganin yanzu baida wata matsala gameda dawo da Reyhana tunda Mommy ta ha'kura.
8pm yana d'aki lokacin, number Reyhana yayi dialing ba kamar koyaushe ba yau a kiran farko tayi picking.
"Assalamu Alaykum". Tayi sallama.
" Waalaikumussalam". Ya amsa.
"Nasreen d'in tana kusa?" Ya tambaya.
"A'a". Ta amsa.
" Ok toh shikenan". Ya amsa sannan ya kashe.
Wayar tabi da kallo ta rasa ma mey zata yi,ba abind a ya bata haushi kamar yadda ya kashe maimakon ita ta zama ita ce ta katse.
Washegari kamar yadda Mommy ta fad'a haka tayi, ta kira Umma ta bata ha'kuri.
Tana ajje wayar sega Walida ta shigo d'akin.
"Yaya ga ya Sameer yazo shida sisters d'inshi".
" Yanzun?" Ta tambaya.
"Ehyi suna parlor". Ta amsa.
"Toh kice musu ganinan".Ta amsa.
•••
Yau Ahmad da kanshi ya d'akko Nasreen ze kawo ta gida ,tun daga nesa Nasreen ta hangi motar Sameer.
" Kalli motar Uncle Sameer yazo gidanmu".Ta fad'a tana nuna motar.
"Uncle Sameer?" Ya tambaya.
"Eh Uncle Sameer". Ta fad'a.
Seda suka 'karasa ya lura da Reyhana da take tsaye a 'kofar gidan gefe kuwa Sameer ne suna magana amma besan mey suke cewa ba.
Ita kuwa Reyhana rakiya ta fito koda sisters d'in nashi suka shiga mota Sameer ya tsayar da ita suna magana sega Ahmad.
Yana parking Nasreen tayi sauri ta fito " Ummie yau Uncle ne ya kawo ni!" Ta fad'a tana 'karasawa inda sike.
Sameer se lokacin ya dubi motar ya hangi Ahmad sannan ya dawo da kallonsa kan Reyhana.
"Ahmad, shine mahaifin Nasreen". Reyhana ta fad'a.
Kai ya d'an gid'a sannan ya mayar da kallonsa kan Ahmad.Da Ahmad beyi niyyar fitowa ba amma ganin Sameer yasa ya fito ,a hankali ya tako har inda sike.
AR²💖
Don't forget to tap on the star below, comment and share.Love you all.Tell me if you are ready to see the pic of those three ,four right? Including zee😂
Jasko💕
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 3⃣2⃣
Yana 'karasawa wajensu ya mi'ka wa Sameer hannu su gaisa,beyi musu ba ya mi'ka masa shima.
Sede kowa a zuciyarsa da abinda yake tunani.Ita de Reyhana ido ne nata.
"Sannu koh". Ahmad ya fad'a yana kallon Reyhana
" Yawwa".Ta fad'a ciki-ciki.
Daga haka ya wuce ya shiga gidan,yana gaisawa da Mommy ya fito dede lokacin Reyhana tana shigowa.
Kallo d'aya tayi masa ta d'auke idonta ta wuce ta barshi a tsaye ta shige,shima ba tare da yayi magana ba ya fita ,har ya koma gida be dena tunanin Sameer daya gani ba.
Lokacin daya shiga parlor Umma bata nan se Zainab.
"Sannu da dawowa ya Ahmad". Ta fad'a.
" Yawwa".Ya amsa.
Shiru ne ya ziyarci parlorn kafin daga bisani Zainab ta sake wata maganar.
"Yaya naga sa'ko na gode". Ta fad'a.
" Uhm?" Ya tamabaya cikeda neman 'karin bayani.
"Na agogo da ka bada a bani". Ta fad'a.
"Uh..ok". Cewar Ahmad yana tunane-tunane.
" Sadiq?" Ya fad'a a ransa.
"So ,shine ya bata agogo yace ni na bashi ya bata.." Ya fad'a a ransa.
"Ka dawo kenan" Umma ta fad'a sanda ta shigo.
"Eh na dawo". Ya amsa.
Tashi yayi ya fita ya koma d'akinsa ya d'auki way a ya dannawa Sadiq kira.
" Na zee".Sadiq ya fad'a yana dariya.
"Sadiq zan maka wula'kanci". Ahmad ya fad'a.
" Daga nayi maka abin arzi'ki,dan'kon soyayya na 'kara maku fah".
"Bana son irin wannan ". Cewar Ahmad kamar yana ganinsa.
" Kode kishi kake? Gaya mini in baka so nake mata magana sena dena".
"Ni na saka ka saya mata agogo har kace nina ce ka bata?"
"Beyi kyau bane agogon?" Sadiq ya tambaya cikeda rainin hankali.
Ahmad dan tsabar takaici kashe kiran yayi ,ya ajje wayar gefe.Tunani Sameer da Reyhana ne ya sake dawo masa a take ya d'auki wayarsa ya kira ta.
Seda ya kira sau uku tukun tayi picking.
"Assalamu Alaykum". Tayi sallama.
" Waalaikumussalam,nayi sa'a an d'aga min kira". Ya fad'a bayan ya amsa.
"Eh ai saboda ban gane number d'in ba shiyasa banyi picking da wuri ba". Ta fad'a.
" Au dama har yanzu number ta bata chanchanta ayi saving ba?"
"Eh". Ta amsa a ta'kaice.
" Toh yanzu ina fatan kingane mey magana?" Ahmad ya tambaya.
"Ina fatan bazaka sake yimin irin wannan tambayar ba?"
"Ni na isa". Ahmad ya fad'a.
"Reyhana wannan dana ganku tare waye?" Ahmad ya tambaya dan sam hankalinsa ya kasa kwanciya.
"Ina ruwanka dashi?". Reyhana ta fad'a.
" Kawai inaso na sani neh". Ya fad'a.
"Toh ,shine wanda zan aura". Ta fad'a cikin rashin nuna damuwa.
Shiru yayi na d'an lokaci kafin yace." Toh Allah ya tabbatar da alkairi".
Ita kuwa ta amsa da "Ameen".
" Nasreen fa?" Ya tambaya.
"Tana wasa". Ta amsa.
" Ok,kinji Mommy tace za'a kawo ta wajen Umma tayi kwana biyu koh?"
"Uhm". Ta amsa duk da kuwa bata san anyi hakan ba.
" Kinga daganan semi ri'keta kawai idan tanaso". Ahmad ya fad'a.
"Da fitowa kai fili ka fad'a kana yin aure zaka kar'beta daya fi kwane-kwanen da kake".Ita kanta batasan zata fad'i haka ba,se da ta fad'a taji haushin kanta kar yace koh kishi take.
" Ni nace maki zan kar'beta? A ina kika ji ma zanyi aure".Ya tambaya dan besan ta sani ba.
"Base ka 'boyen ba naji ,wannan be shafen ba kawai de inaso ka sani tunanin ka kar'bi Nasreen ma ka dena dan bazan ta'ba yarda wata tayi mini ri'kon 'yata ba I can do it my self". Ta fad'a.
"Karki damu tare zakui". Ya fad'a.
" Mean?"
"Ga Ummienta ga Auntynta se wadda ta za'ba ai ana tare".
Yanzun ta gano inda ya nufa aiko da saurinta tace" Allah ya kiyaye".
"Zamu zama happy family fa".
" Bade dani ba chan ka samo wata,ka dena wannan tunanin".
"For Nasreen". Ahmad ya fad'a.
" Na fad'a maka ina tare da ita,abinda kake fad'a ma is not possible ".
" Reyhana kina so kice kin mance da rayuwar mu ta da,bakyaso mu komo...."Be 'kare maganar ba ta katse shi.
"Maganar baya ta wuce, am hanging". Ta fad'a.
" Reyhana.. ". Ta katse wayar.
Wani saban tashin hankali ne ya tunkareta,batajin zata iya zama da kishiya haka bazata yarda a d'auke mata Nasreen d'inta ba koda wuni d'aya ne ,imagine ta shiga yi wai gata ga Zainab a matsayin kishiyarta Ahmad mijinsu.
" This is not going to happen ". Ta fad'a tare da dafe kai.
Ko fita parlor ta kasa yi tunani ya addabe ta ji take kamar ta tsala ihu.
°°°
Ita kuwa Zainab koda ta koma d'akinta agogon ta d'akko se kalleshi take tana jin dad'i a ranta." Watoh nauyi yake ji shine ya kasa bani da kansa, my Ahmad kwai miskilanci". Ta fad'a a ranta.
Ciro shi tayi daga box d'inshi ta saka a hannunta se kalla take tana yaba kyan agogon.

***
Kullum abu gaba yake ranakun aure suna matsowa , wata weekend da akai Mommy tasa Sageer ya kai Nasreen gidan Umma tayi kwana biyu lokacin ma Ahmad yayi tafiya.Reyhana a kwana biyunnan kamar tayi musu ihu dan koyaushe tazo kwanciya Nasreen d'inta seta fad'o mata a rai.
Ahmad kam ta 'bangarensa abu sake 'karfafa yake dan a rana idan beyi mata text sau biyar ba toh yayi sau uku shi da gaske yake so yake ta komo,bama ya tuna cewa ga abinda ke gabatowa.
Yau wani weekend d'in ya sake zagayowa ,a cikin yaran Anty Ummi ake bikin d'aya daga ciki su Ikram se shirye-shirye sike banda Reyhana da tana zaune koh kayan fita bikin bata sa ba.
Mommy kuwa tin safe tana gidan uwar biki ,su se yanzu 4pm sike nasu shirin ,Nasreen ma anyi mata kwalliyarta dan yau da ita za'a coz ba dinner bane.
"Ummie ki shirya dan Allah mu tafi". Nasreen ta fad'a.
" Ke ki rabi dani ".Reyhana ta fad'a.
Tana nu'ku-nu'kunta da ta saba a haka ta gama shirin wajen 5pm lokacin, kowa ya gama shiryawa.
Wannan karan da Walida da Ikram ne sukai anko ,ita Reyhana nata tasa daban.Maroon lace tasa wanda ya amsheta sosai tasa golden gyale.
Tana shirin fita daga d'akin ta jiyo muryar Sameer a parlor yazo.Shi besan ma da fita bikin ba seda Nasreen take fad'a masa.
Sam bata so zuwansa ba haka ta sauka suka gaisa.
" Dukanku zaku fita?" Ya tambayeta.
"Eh"Ta amsa.
" Ok idan ba damuwa ai sena kaiku".Ya fad'a.
"Da ka bari ma". Ta fad'a.
" Yaya Bassam seya kaimu kawai a motarki ku kuma..."Bata bari Ikram ta 'kare maganar ba ta galla mata harara.
"Yes shikenan ma haka za'ai". Sameer ya fad'a.
Zata sake magana sega kiran Ahmad yana shigowa a,da farko 'kin d'agwa tayi se'a na biyu.
" Assalamu Alaykum".Tayi sallama
"Waalaikumussalam". Ya amsa.
" Gani a waje".Ya fad'a.
"Toh se akai yaya?" Ta tambaya a hankali yadda bazasi jiyo ba dan ta d'an matsa nesa dasu.
"Nifa ba gunki nazo ba Mommy nazo gaisarwa". Ya fad'a wanda a ransa ba haka bane kuwa itan de ta kawo shi.
" Mommy kuwa bata nan ba".Ta fad'a.
"Nasreen fa?" Ya tambaya.
"Fita zami muma ka bari gobe".Ta fad'a.
" Aiko shigowa zanyi idan bazaki bari tazo ba".Ya fad'a.
"A'a gatanan zata zo". Tayi saurin fad'a dan bata so su had'u da Sameer.
" Am waiting ".Ya fad'a yana dariya dan yadda tayi saurin maganar yasa shi yin dariya.
" Nasreen".Ta kira ta.
"Jeki ga Uncle chan yazo kiyi sauri ki dawo". Ta fad'a.
Da sauri kuwa ta fita tana zumud'i." Uncle kaga nayi kwalliya".Ta fad'a sanda ta 'karasa.
"Inye! Kinyi kyau sosai ina za'a ?" Ya tambaya.
"Biki zamu Uncle Sameer yace ze kaimu da Ummiena". Ta fad'a.
Wani irin haushin Sameer ne ya kamashi " Shine ma ze kaita watoh ,shiyasa bata so ya shiga gidan yanzu Sameer ya fishi a gunta?" Ya tambaya a zuciyarsa.
"Uncle Ummiena tace nayi sauri na koma ". Nasreen ta fad'a.
D'an murmushi yayi mata ya gid'a kansa ,da sauri ta koma tana bye-bye ta shige gida.
Ahmad tunani ya shiga yi ta yadda ze 'bullo da al'amarin,baya jin ze iya jurar ganin Reyhana da wani a mota d'aya ma da sunan za'a kaita biki " Nasan tayi kwalliya ma ,oh shikenan yaga kwalliyanta".Wata zuciyar tasa ta fad'a.
Tunani yayi ko ya tafi kawai ya huta ganin takaici,a sanyaye har ya bud'e 'kofar motarsa ze tafi wani idea ya zo masa.A take ya saki wani makirin murmushi da ban ta'ba ganin yayi ba.
Kalle -kalle ya shiga yi a wajen kamar mey neman wani abu ,can daga gefe ya gano wata 'kusa doguwa me tsini,da sauuri ya dur'kusa ya d'auka be tsaya a ko ina ba se jikin motar Sameer.Tayar baya ya zage ya chaka mata 'kusar har seda ta sace haka d'ayar ma yabi ya sace na gaba kawai ya bari.Allah yaso ba mutane a layin, ba wanda ya ganshi(😂😂 believe me da'kyar na iya typing d'innan saboda dariya ,bansan Ahmad da irin wannan muguntar ba😂😂😂).
Komawa yayi jikin motarsa ya jingina harda crossing arms ya basar.
AR²💖
Don't forget to vote, comment and share pls.
Jasko💕
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 3⃣3⃣
Su Bassam ne suka fara fitowa Ahmad yana tsaye suka wuce a mota,su kuma su Reyhana lokacin suke fitowa da Sameer,Nasreen tana tsakiyarsu.
Wani irin takaici yaji a ransa ji yake kamar ya sha'ke Sameer.Haka ya daure har suka 'karaso jikin motar Sameer.
"Shikuma mey yake be tafi ba?" Reyhana ta tambaya a zuciyarta sanda ta lura da Ahmad.
Kau da kanta tayi tana tsaye jikin motar.Sameer ya sakankance ze bud'e gidan gaba yaga d'anyan aiki.
Taya tayi da'bas kamar ta shekara da sacewa,se yanzu daya waiwayo ya lura da Ahmad da idonsa akan wayarsa yana tapping kamar besan suna wajen ba.
Dubawa yayi bayan mortar ya d'auki spare taya ,nan ya sake ganin tayar d'ayan side d'in a sace gashi spare d'in d'aya ne koya sauya ma seya gyara d'ayan.
Indan Reyhana take ya 'karaso yake fad'a mata abinda ya faru.
"Toh bari ma sami ko Napep ne". Reyhana ta fad'a.
" Ummie mun fasa zuwa unguwar?"Nasreen ta tambaya.
"A'a zamu..." Bata 'karasa ba sega Ahmad tsaye ya 'karaso wajen.
"Da matsala ne?" Ya tambaya yana kallon Sameer.
Shiru yayi masa be amsa shi ba se Reyhana ce tace "A'a".
" Uncle ka kaimu kaga wai motar Uncle ta lalace".Nasreen ta fad'a.
"Ayya! Do you need help?" Cewar Ahmad yana wa Sameer wani kallon tara saura.
"No need". Sameer ya fad'a.
" Ummie mu tafi".Nasreen ta fad'a cikeda 'kosawa.
Sameer ganin yanda Nasreen ta 'kagu a tafi yasa ya shawarce ta Ahmad ya kaisu dan yasan gyarannan bana yanzu bane.
"I think it will be better Ahmad ya kaiku kinga lokaci yana 'kurewa and kinga Nasreen ma ta damu". Sameer ya fad'a.
" Don't worry zami iya jira ma". Reyhana ta fad'a dan ta tura wa Ahmad.
"Don't mind ,it's ok like that kuje kawai". Sameer ya fad'a.
" Ummie mije". Nasreen ta fad'a tana jan hannunta.
"Mije koh". Cewar Ahmad fuskarsa d'auke da murmushi mey nuna fassarori.
Rolling eyes tayi badan tanaso ba ta tafi zuwa motar shi.Ahmad harda bud'e mata gidan gaba aiko ta'ki shiga ta shige baya,Nasreen kuma ta shiga gaban.
Ahmad basarwa kawai yayi ya zagaya ya shiga mota,harda wani gyara morror na ciki yana kallo Reyhana da ta kau da kai tana kallon waje.
Sameer yana tsaye suka bar layin haushi ya isheshi ya daki tayar motar da 'kafa gumm! Ya bige 'kafa." Ahhg!" yai 'yar 'kara.
Tunda ta fad'i sunan gun da zasu bata sake magana ba, tafiya ake shiru bame cewa komai sai Nasreen jefi-jefi tana wa Ahmad hira.
Radio yayi turning on channel d'in da sike saurara akai playing wa'kar india "Zaalima"
Jo tere khatir tadpe pehli se hi,kya usse tadpana🎶
O Zaalima o zaalima🎶
(The one who is already longing for you,
Why torment him even more?
he one who is already misled for you,
Why mislead him even more)?
Jo tere ishq mein behka pehle se hi,kya usse behkana🎶
O Zaalima o zaalima🎶
(The one who is already longing for you,
Why torment him even more?
he one who is already misled for you,
Why mislead him even more?)
Ankhein marhaba 🎶
Baatein marhaba🎶
Main sa martaba 🎶
Deewana hua
(Your eyes are great,
Your talks are great
I am crazy for you a hundred times over)
Mera na raha🎶
Jabse dil mera🎶
Tere hudn ka🎶
Nishana hua🎶
(My heart ceased to be mine,
Since it became a target of your beauty)
Jisku har dhadkan tu ho aise🎶
Dil ko kya dhadkana🎶
O Zaalima o zaalima🎶
(The one whose every heartbeat are you,
Why quicken his heartbeat?
O cruel one!)
Saasson mein🎶
Teri naz deekiyon ka🎶
Ittar tu ghol de-ghol de🎶
(Mix the perfume of your closeness In my breath)
Main hi kyun 🎶
Ishq Zaahir Karin 🎶
Tu bhi kabhi bol de..bol de🎶
(Why I alone should express my love,
You too express your
Le ke jaan hi🎶
Jayega meri🎶
qaatil har tera🎶
Bahana hua🎶
(Your every excuse is a