Chapter 14 Reading ARZIKI RABO Complete Hausa Novels by Dijensy.txt Arewa Novels

ARZIKI RABO Complete Hausa Novels by Dijensy.txt

Author :  Dijensy Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   14 / 21

39K to 42K   out of 61.6K words

ta shigo take fad'a mata Sameer yazo.

      "Kije kice ganinan".Reyhana ta fad'a.
   
      Mayafi ta d'auka ta yafa sannan ta fita.

      A falo ta tarar dashi shi kad'ai ko Nasreen bata nan,zama tayi opposite dashi.

       Bayan sun gaisa Sameer ya fara magana"Uh..Reyhana bakya ganin it's the right time?".

      " Right time for what?" Ta tambaya.

        "To give me chance, Reyhana baza kice bakisan abinda ke raina ba   duk iya tsahon shekarunnan ,at first nayi losing and now ga second chance na sake samu i don't want to miss it you know ,I so much care about your life,  everything yours you are always in my mind ,my love for you  will never vanish from my heart you are the only one i ever loved,  you are my first love and no woman can ever take your place in my heart, yet I never find someone like you  ,Reyhana you are different from others, you are unique, if am to stay here for years I can't stop describing how i valued you and the love that I have for you,Reyhana please consider".

       Reyhana sam kalamansa beyi tasiri a zuciyarta ba dan be hanata fad'a masa;" Sameer,a yanzu inaso na koma karatu and i need to wait for Nasreen to start schooling".

       "Kina nufin kice se ta fara makaranta and se kin kammala masters right?"

      "Yes". Ta amsa.

        Jira take taga mey zece ,zuciyarta tana fad'a mata " Shikenan kin kawo 'karshen abin,Sameer baze iya jira har wannan lokacin ba".

       D'an guntun murmushi yayi kafin yace"Reyhana how many times do i have to tell you i am always your supporter I promise to be by your side always and forever, wannan ba wani matsala bace I promise to wait for you no matter how long it wiil take us".

         "Sameer taya zaka jirani har wannan lokacin b..." Bata 'kare ba ya  katseta.

      "I promised Reyhana".

       Shiru tayi bata sake cewa komai ba ,shigowar Nasreen  tasa basu cigaba da magana ba.'Karasowa tayi wajen ummienta tana mata hira,daga baya ta koma gun Sameer.

            °•° >3 years Later <°•°

   " Nasreen!" Reyhana ta kwala mata kira tana daga d'aki.

         Seda ta kwashi minti kusan 5 ta shigo d'akin,tana manne daga jikin 'kofa ta 'ki 'karasowa se zazzare ido take cikeda tsoro.

       "Zonan!" Ta kira ta tsawace.

          "Ummie dan Allah karki dakeni". Ta fad'a cikin rawar murya.

           " Ayyo! Watoh kinsan mey kikai? Zonan nace".Reyhana ta fad'a tana mata nuni da yatsa.

     A hankali ta 'karaso gurin kanta a sunkuye.

      Rigar uniform d'inta ta makaranta ta d'auko ta nuna mata.

       "Waya yanka wannan?" Ta tambayeta.

        Shiru tayi bata amsa ba yanzun ta d'ago kanta.

       "Ba magana nake ba?"

        "Ummie kiyi ha'kuri na dena". Ta fad'a kamar zatai kuka.

        Reyhana da hanzari ta tashi tana shirin fizgota sega Abba ya shigo d'akin.

     Da gudu taje ta ma'kale a jikin Abba.

      " Toh meya faru kuma?" Ya tamabaya yana d'ago kanta.

     "Dukana ummie zatai".Ta amsa.

     " Ya da haka?" Cewar Abba yana kallon Reyhana.
  
      "Abba rigar makarantarta ta yaga saboda karta je gobe".Ta amsa tana nuna masa.

       "Ayi mata afuwa yanzu bazata 'karaba ,uniform d'in ba biyu bane?" Abba ya tambaya.

    Se lokacin ta tuna biyu ne da idonta ya rife,Nasreen jin ance biyu ta tur'bina fuska dan bata son zuwa makaranta.

      "Ungo chocolates d'inki". Abba ya fad'a tare da mi'ka mata nylon dake hannunsa.

     Tsalle ta shiga yi tazo wajen Reyhana tana nuna mata.

     " Toh nagani seki ce kin gode".Ta fad'a.

      "Abba thank you". Ta fad'a.

       " Yawwa 'yar baturiya".Abba ya fad'a.

      Tare suka sauka 'kasa da Abba ta ruga a guje  wajen su Walida tana nuna musu.

         Walida da anzama 'yan mata da ace dane da seta ce ta bata, yanzu kuwa kau da kanta tayi ta cigaba da abinda take.

       A shekaru ukunnan abubuwa da dama sun gudana.Reyhana ta kammala masters d'inta,Nasreen kuwa an sata makaranta 2yrs da suka wuce yanzu tana nursery 2 koyaushe fama ake da ita wajen shiryawa school.

      Sageer tuntuni ya fara aiki a asibiti as medical laboratory technician ya zama busy ba kasafai suke ganinshi a gida ba se dare.

       Ikram ma ta zama cikakkiyar journalist tana zuwa aikinta itama,se Bassam da saura shekara d'aya ya rage ya kammala degree d'insa,Walida wannan shekarar tayi graduating yanzu admission take jira.

       Sameer kuwa ya koma America amma yana zuwa jefi-jefi kuma wani sa'in suna waya da Reyhana.

       Mommy se kallo dan wani lokacin idan ta gansu full house setaga kamar ba ita ta haifesu ba ,kowa ya girma.

                   ***
Ahmad°•°

        Shigowarshi gida kenan daga gidansu Sadiq yake bayan ya dawo daga aiki ya biya se yanzu ya shigo gida,6:02pm.

        D'akinsa ya shiga ya watsa ruwa tukun ya fito cikin 'kananan kaya blue jean da ba'kin T-shirt.

    A falo ya iske Umma,cikin girmamawa ya gaisheta.

      "Yaushe ka shigo banjiba?" Ta tambaya.

       "Ba jimawa". Ya amsa.

        " Toh abinci fah".Ta tambaya.

       "A'a na 'koshi". Ya amsa.

        " Nikam gajiya akai da abincin nawa yau kusan kwana uku ba a ci".Umma ta fad'a.

        "No kawai bana jin yunwa neh fa anjima zanci". Ya fad'a da murmushi kad'an a fuskarsa.

     "Toh ai shikenan". Ta fad'a.

       Remote  dake kan center carpet ya d'auka ya chanja channel daga Arewa24 zuwa MBC Action.

         " Aikin kenan ,wannan masu damben koh me za'a kalla anan oho". Umma ta fad'a.

       Ahmad kuwa murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba ya cigaba da kallonsa.

       1 year kenan da fara aikinsa ,mahaifin Zainab shi ya taimaka masa ya samu aiki a NGOs(Non-governmental organizations).

     Komai ya sauya tun sanda ya samu aiki,Ya gyara musu gidansu ya koma kamar sabo ba abinda Umma ta rasa a yanzu inde na bu'katar alatu da sauran wani jin dad'i although rayuwa ba koyaushe ake cikin jin dad'i ba no matter how billionaire you are.

       A yanzu haka yana da farmland na noman shinkafa kuma cikin ikon Allah yana samun profit kuma wannan shawarar Umma ce ta sashi yin noman shinkafar.

      Zainab tana zaria, ta kwashe 2weeks a can amma nan da kwana biyu zata dawo tunda wannan week d'in aka koma school.

      Zainab ba abinda ya chanja a cikin ranta gameda son da take wa Ahmad sede har yanzu bata fito tace tana sonsa ba.

     Tun sanda ya dawo gida Nigeria Umma tayi ta tirsasashi yaje gidansu Reyhana amma kullum seya ce mata ba yanzu ba,daya gaji da tunatar dashi da take seyai 'karya yace yaje,idan ta tambayeshi ya sake zuwa seyace mata "Eh" akan haka ya barta.

     Daga yayi attempting zuwa seya fasa, baida kalaman daze fad'a mata(A tunaninsa) from bad to worse da ana maganar 4yrs yanzu 6yrs be saka 'yarsa a ido ba,shikanshi idan ya tuna yana jin haushin kansa.

                    ***

     Reyhana kuwa a zuciyarta tana 'ko'karin mantawa da Ahmad amma kamannin da Nasreen ta d'auko na Ahmad yasa bazata mance da fuskarsa ba,ita tama fidda ran sake ganinsa a rayuwarta.

      9pm lokacin baccin Nasreen,seda tayi addu'a kamar koyaushe Reyhana tana karanta mata ita kuma tana repeating.

     Seda ta tabbata tayi nisa da bacci tukun ta komo falo,duk yaran gidan suna falon amma banda Sageer.Kusan kwana biyu haka yake seya 'ki fito ba kamar da ba dayake fito a d'an yi hira kafin su kwanta.

     "Walida Sageer be dawo bane?" Reyhana ta tambaya.

    "Ya dawo yana d'aki". Ta amsa.

     " Yaci abinci?" Ta sake tambaya.

     "Beci ba ,Yaya Ikram ma tana masa magana yayi banza da ita ya wuce d'akinta".Cewar Walida murya 'kasa-'kasa.

        Kai kawai ta kad'a ta zauna kan kujera.

      
AR²💖

       Comment,vote and share.Luv u all💋

Jasko💕

      

    

    
       

     
 

    

      
     
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍


*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣3⃣
  

Washegari da safe around 8:15am kowa ya hallara a dining seat d'in Walida ne kad'ai empty se Nasreen da tun d'azu driver ya kaita makaranta.

   

"Walida bata tashi bane?" Abba ya tambaya.

"Ta tashi". Ikram ta amsa.

" Toh mey take baza ta fito ba?" Mommy ta fad'a.

"Ikram kije ki kirata". Cewar Mommy.

" Mommy nafa makara is almost 8:30am".Ikram ta fad'a.

"Bari na kirata". Reyhana ta fad'a tare da mi'kewa.

Murya taji 'kasa-'kasa lokacin da ta shiga d'akin,blanket taga alaman Walida ta rufe kanta dashi.

" My Prince ka daure kasha magani idan ba haka ba kanka ze cigaba da ciwone kaji".

Baki Reyhana ta saki jin muryar Walida tana waya.'Karasawa gadon tayi ta cukuikui blanket d'in ta yaye ta.

       Cikin razana Walida ta mi'ke zaune ,wayar ma tayi cilli gefe da ita,a zatonta Mommy ce.Ganin Reyhana ce yasa ta d'an ji relief tasan komai zezo da sau'ki
    
       "Iyye abinda kikeyi kenan?" Reyhana ta fad'a.

     Walida a sukwane ta d'auki wayar tayi hanging sannan ta dawo da kallonta wajen Reyhana.

       "Da 'kawata fa nake waya". Walida ta fad'a.

        " Shiyasa naji kina cewa My Prince ko? Ke bazaki nutsu ba koh ? Shikenan zan fad'a wa Abba kinga se ya aurar dake kowa ya huta naga alamar aure kike so".

       "Yaya dan Allah kiyi ha'kuri bazan 'kara ba". Walida ta fad'a.

       "Waye wannan d'in?" Reyhana ta tambaya.

        "Waseem". Ta amsa tana sosa kai.

         " A ina yake?"
        
          "Uhm..uhh d'an school d'inmu". Ta amsa a kunyace.

          " Class mate d'inki?,'karya yake miki wannan iyayensa ba aure zasi masa yanzu ba har nawa yake,just wannan year d'in fa kukai graduating kuma shine kike kulashi sakarya ,duk sanda na sake gani kina waya dashi sena fad'a wa Abba ya miki auren dole".

       Shiru tayi kanta a sunkuye ta'ki cewa 'kus.

     "Tashi ki wuce ki breakfast". Ta fad'a tare da ficewa.

      Bayanta tabi suka sauka 'kasa lokacin har Ikram ta tafi aiki.Muzurai tayi tayi kar Reyhana ta fad'a wa Mommy.

            ***

     Ahmad yau ko breakfast beyi ba ya fice a motarsa marcedes mey black color, yana hanya sega kiran Zainab.

        " Yaya ina kwana". Ta gaisheshi.

         "Lafiya lau". Ya amsa.

          " Umma tace gobe zaki dawo koh?"

           "Eh".Ta amsa.

            " Ok toh Allah ya kaimu".Ya fad'a ta amsa da Ameen ,daga haka sukai sallama ba tare da sunyi doguwar hira ba.

°°°

   3pm Reyhana da Mommy suna zaune a falo kamar daga sama suka ji an turo 'kofa da 'karfi.

     Sageer suka gani da sauri ya wuce d'akinsa ko ta kansu bebi ba.

      "Mommy wai Sageer lafiyarsa lau kwana biyu?"Cewar Reyhana.

       " Atoh gashinan de kullum cikin 'kunci da fushi".Mommy ta fad'a.

       "Bari naje".Reyhana ta fad'a tare da mi'kewa ta nufi d'akinsa.

         A bud'e ta tarar da 'kofa saboda haka sallama tayi ta shiga.

       A kwance ta iskeci yayi rigingine hannunsa akan goshinsa ya 'kura wa ceiling ido ko takalmin dake 'kafarsa be cire ba.

       " Sageer meyake faruwane wai?"Reyhana ta tambaya.

        Se lokacin ya kula ma tana d'akin.

       "Babu". Ya fad'a ciki-ciki.

        " Amma na ganka haka".

        "Kawai na gaji ne". Ya fad'a.

        " Nifa ba wacce zaka 'boyewa abu bace, meye amfanin 'yan uwa idan bazasu san matsalar ka ba su taimaka maka kayi solving ba?"

      Mi'kewa yayi zaune fuskarsa damuwa 'karara ta banyana.

      "Wannan abun ba abune wanda zaku iya taimaka min ba kuma ina ganin ma na makara". Ya fad'a.

       " Koda addu'a ai mu masu taimaka maka ne,tell me meyake faruwa".Reyhana ta fad'a tare da 'karasowa inda yake.

        Wayarsa kawai ya d'auko ya bud'o wani pic na mace 'yar budurwace kyakkyawa a kai.

      "Fatima". Ya fad'a.

      " Fatima? Itace damuwarka koh?"

      "Ummien Nasreen Allah bazan iya rayuwa ba ita ba,I can't bear to loss her,suna nema su rabani da ita".

       " Suwaye?" Ta tambaya cikin nuna damuwa.

       "Iyayenta ,sune zasu aura mata cousin d'inta".Ya 'kare maganar kamar zeyi kuka.

       Reyhana tausayin 'kanin nata ne ya kamata lokaci guda kuma ta tuno rabuwarsu da Ahmad.

      " Komai zezo da sau'ki Sageer,zan taya ka da addu'a  kaima ka dinga yi".Ta fad'a.

       Kai ya gid'a almar "Toh" tare da fad'in "Amma karki fad'awa Mommy".

      " Don't worry bazata sani ba".

             "Thank you". Ya fad'a.

     Murmushi ta 'kalo tace " Is okay".

             ***

    Ahmad yana komawa gida ya tarar da Imran yazo,Umma tana fita daga falon Imran ya tinti'beshi.

       "Ya ake ciki har yanzu baka Jeba?"

      "Uhm". Ya amsa.

      " Ina baka shawara ka gaggauta zuwa kar kazo kayi da kasani,this is too much 6yrs ba wasa bane Ahmad ya kamata ka gane".

      "Ni kaina nasani Imran tunanin yadda Reyhana zata yarda da abunda zance mata nake"Ahmad ya fad'a.

      " Malam ka cire wannan abun  a ranka,ta yarda karta yarda Nasreen is your daughter ba yadda zasi ,dan haka gara ma ka mi'ke ba wajensu zaka ba 'yarka kaje gani".

      Sosai maganar Imran ta shigeshi,yaji 'karfin gwiwa a yanzu ya shirya zuwa gidansu Reyhana.

    
     Da daddare Umma take fad'a masa gobe ze d'akko Zainab daga tasha.

      Beso kasancewar hakan ba saboda lissafinsa ze ruguje na zuwa gidansu Reyhana.

°°°
      2days later

       Daga aiki koh gida be komo ba Ahmad direct ya wuce gidansu Reyhana around 5pm lokacin.

     Daga can nesa yai parking a zuciyarsa yana sa'ke-sa'ke iri -iri ,ya shafe kusan 30hrs be fito ba se shawarwari yake,gashi bega ko mutum d'aya na gidan ba a waje.

        Ya dafa hannunsa a steering ya maida kallonsa gate d'in gidan ,mota ya gani ta sauke yara guda uku ta juya.

       Biyu daga cikinsu mace da namiji d'ayar kuwa Nasreen ce suna sanye da uniform na Tahfiz.

      Guda biyun gidan dake gefensu Reyhana suka shiga ita kuwa Nasreen bye tayi musu da hannu tsayawa tai gate ta hau kan wani tudu se cisgo flowers da suka shingid'o ta bango take.

     Sam ya kasa bawa kansa amsar abinda zuciyarsa ke tambaya."Is she Nasreen? My daughter ?"

      Baro 'kofar gidan tayi tana nufowa inda motarsa take,daya kalli direction da takeyi ya kula ashe ita mage ta biyo takeson d'auka.

     A sanyaye ya fito daga motar ya bita da kallo magen ta gudan mata ,komowa tayi zata shige inda yake ya tsayar da ita.

       "'Yar yarinya". Ya kira ta.

       Waiwayowa tayi ta kalleshi" Ni gida zan tafi ummiena ta hanani magana da wasu a waje".Ta fad'a.

      "Eh yanzu ai zan tafi,amma ya sunanki?" Ya tambayeta.

      "Nasreen, Aisha Ahmad Yusuf". Ta amsa.

      Amsar data bashi ya isheshi tabbatar da abinda yake tunani.

     Ma'kwat! Ya had'iyi yawun daya tokare a ma'kgoronshi.

       " Kaji kunya 'yarka bata sanka ba".Zuciyarsa ta fad'a.

      Daurewa yayi yace" Ni sunana Uncle".

     "Uncle ? Koya min karatu zaka yi?" Ta tambaya.

     Fuskarsa d'auke da murmushi yace "Eh".

      " A nan?" Ta sake tambaya.

       "A'a ,ya sunan school d'inku?"

       Amsa masa tayi sannan tace"Ummiena zata jamin kunne idan ban koma ba".

      "Eh kije gida yanzu". Ya fad'a.

      Da sauri ta wuce ta shiga gidan yana tsaye har ta shige tukun ya koma mota ya tafi.

      Nasreen kuwa tana shiga gida ta soma bada labari taga wani sunansa Uncle.

      " Ban hanaki yiwa mutanen waje magana ba?" Cewar Reyhana.

     "Shine ya fara yimin magana wai ze koyan karatu".

     " Toh karki sake kinji koh".Reyhana ta fad'a.

      "Toh ummie". Nasreen ta fad'a tana cire hijabi.

     Reyhana tunani ta shigayi wannan waye?

AR²💖

Comment,vote and share.love u all💋

Jasko💕
       

  
    
 
   
     

      
        
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍


*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*


🅿 2⃣4⃣


      Lokacin da ya dawo gida su Umma na falo yana jiyo su ita da Zainab,d'akinsa ya shiga ya zauna yana ta tunano Nasreen.

      Se yanzu ya sake gane rashin kyautawar da yayi na rashin bata kulawar da ta wajaba a kansa.

  °°°
Se wajen maghrib daya fito zeje masjid Zainab ta ganshi.

     "Laa dama ka dawo gida".

      " Eh ai ban jima da dawowar ba". Ya amsa.

      "Masallaci zaka?" Ta tambaya.

      "Uhm". Ya amsa.

      " Toh seka dawo". Ta fad'a.

          Zainab bayan fitarsa ta shiga kitchen had'a abincin dare.

                   ***
  Reyhana

14 / 21