Author : Dijensy Category : Romantic Hausa Novels
ya kirata 'kin picking tayi har ya tafi bata sakko ba.
Tana zaune Nasreen ta shigo tana murna hannunta ri'ke da leda "Uncle ya bani". Ta fad'a tana nuna mata.
" Toh naji ". Reyhana ta fad'a.
Kayan ciye-ciye ne kala-kala ya siyo mata.
•••
Koda ya koma gida d'akinsa ya shige besan ma Zainab ta dawo ba.
Yana zaune sega kiran Imran." Aboki yane?" Cewar Imran.
"Ya kua". Ahmad ya fad'a.
" Da matsala ne?" Ya tambaya.
"Kaima ka sani ai"Ahmad ya fad'a.
" Reyhanan de?"
"Ehyi ita".Ya amsa.
" Kaima ka bari se bayan wannan auren tukun ".
" For how long?"
"Duk yanda ya kai mana, kai da ka ha'kura da Zainab d'inka ma". Imran ya fad'a.
" Kai baza ka gane ba,tunda mike dake na ta'ba ce maka ina son Zainab? Imran nifa bana son yarinyarnan kawai de saboda Umma shiyasa zan ha'kura". Ahmad ya fad'a.
Zainab duk wannan zancen dayake yi a kunnenta ,tana tsaye jikin 'kofar d'akin sa.Umma ce ta sata kira mata shi ,zuwan da tayi ta riskeshi yana waya kunnenta ya jiyo mata wannan maganar.
Gwiwoyinta sinyi mata li'kis da 'kyar ta iya komawa d'akinta.Kuka mara sauti ta zauna ta shiga yi ba 'ka'k'kautawa.
"For all this long dama Ahmad be ta'ba sonta ba ,so Umma ce tasa ze aureta ashe ? Shiyasa baya nuna damuwa dani ". Abinda take fad'a a ranta kenan.
Umma jin shiru yasa ta biyo sawu ,Zainab na hango tahowar Umma tayi saurin goge hawayen ta.
" Zainab, naji shiru koh baya nan?" Ta tambaya.
"Yana.. yana zuwa". Ta fad'a.
Gid'a kai tayi tukun Umma ta fita ta koma d'akinta. Zainab sake goge fuskarta tayi sannan ta fita taje ta kira shi ,sam bata nuna alamar wani abu ba kuma shima be gano hakan ba.
D'akinta ta koma ta shiga wani sabon kukan ,tana son Ahmad sosai ba 'karamin ciwo abin yai mata ba duk wannan abun da take ashe shirmenta take,bata ga amfanin auren wanda bata so ba.Ta fad'a a ranta.
***
Sameer yau da yamma yazo gidansu Reyhana, da kanta ta kira shi tace tana so siyi magana a ranta ta gama yanke shawarar fad'a masa zata aureshi.
Bayan yazo sun gaisa da Mommy ta tashi ta bar musu parlourn Nasreen dama bata dawo daga school ba.
Bayan sun gaisa Reyhana tayi gyaran murya kafin ta soma magana.
"Ahma..uh..Sameer". Ta kira sunansa shaf ta mance ta kira shi da Ahmad.
" Dama ina so na fad'a maka shawarar da na yanke,uhn..Sameer na..."Be bari ta 'karasa ba ya katse ta.
"Reyhana base kinyi bayani ba na gano abinda kike so kice,na dad'e da fahimtar hakan ni kaina tun sanda naga Ahmad.."
"Sameer ba haka nake nufi ba n.."
"Karki damu kanki ,kada ki manta na fad'a miki duk abinda kike so shi nake so ,Ahmad shi yafi kowa dacewa dake ,ya kamata ku kasance tare".
Shiru tayi ta zama speechless dan bata zaci haka ba daga wajen sa.
"Amma Sameer.."
"Is ok don't worry,Ahmad is the best husband for you I know you still love each other ,you have second chance to be together Reyhana,don't worry about me am really happy for you".
Tausayinsa ne ya kamata sosai Sameer is a very kind person duk wani abu da zatai baya ganin laifinta kuma tasan yana sonta sosai and duk wani abunda take so shi yake so.
" I am so sorry Sameer ". Ta fad'a.
" Don't worry".Ya fad'a.
"Thank you".
" Don't mention". Ya fad'a fuskarsa d'auke da murmushi.
Itama murmushin ta mayar masa tana jin tausayinsa.
***
•°• 4 month later•°•
Reyhana ce zaune a parlour tana ri'ke da wayarta tana chatting da Ikram.
Reyhana: "Ke wannan status d'in fa ? 'boye fuskar mijin naki kike kar wasu siyi miki snatching"
Ikram: " Hhh ,shima haka yake min bara kiga"
Reyhana: "Iyye ,Amaryar Sameer.
Ikram: "Kinji yaya ,kema Amaryar Ahmad"
Reyhana: "Au ramawa zaki"
Ikram:"Toh ku ina naku pic d'in,a turon na gani".
Reyhana: " Kizo har gida tukun"
Ikram: "Nafi kowa son hakan"
Reyhana: "Sorrynki yarinya se nan da 3yrs😝"
Ikram:"Chabb! Nan da wani watan zan duro 9ja"
Reyhana:"Kiyu biyayya se a kawo ki"
Ikram: "Ha ,ina Nasreen 'yan mata?"
Reyhana: "Tana school"
Ikram: "Se ke kad'ai,gaskia ya kamata ayi mata 'kani da wuri"
Reyhana: "Kede mike jira yarinya 😝 da twins zaki duro 9ja"
Ikram:"Hhhh lokacin kinada 4 koh😋"
Reyhana: "Kin manta 7😎"
Ikram: "Lol"
Ikram: "Am waiting"
Reyhana: "What?"
Ikram:"Naku pic d'in"
Reyhana: "Ok"

Ikram: "😱 kinganki kuwa"
Reyhana: "Mey?"
Ikram: "Kinyi kumatu anya😂😝"
Reyhana:"Zan bige ki"
Ikram:"Ummien boy zan ke kiranki yanzu"
Reyhana"Ke kuma Maman girl"
Ikram:"Hehe wayaga"
Reyhana: "Hahaha kallo ze koma kanki yarinya"
Ikram: "Jeki girki kar habeebinki ya dawo💕"
Reyhana: "Ke kai"
Ikram: "Ai tare mike girkin"
Reyhana: "Iyye lovayya😻"
Ikram:"Ha"
Reyhana:"Toh ki gaisheshi inya dawo"
Ikram:"Ok bye "
Daga haka Reyhana ta sauka daga chat d'in ta shiga kitchen domin yi musu girkin rana.
A wata hud'unnan abubuwa da dama sun faru,Zainab da kanta ta fad'a wa Ahmad ta janye aurensa da Umma ta sani ba yadda batai da ita ba suma yayyin Umma da mahaifiyarta suka sata a gama kowa yana mamakin 'kinta na auren Ahmad da suka isheta ma kuka take sa musu haka ba yadda suka iya dole aka rabu da ita suka ha'kura ,Ahmad dama haka yake so. Ta koma Zaria ma dan ta kammala karatunta.
Shi kuwa Sameer ya koma wajen Ikram a kai sa'a ta amince,lokaci d'aya aka yi aurensu,Sameer da Ikram,Ahmad da Reyhana. Sameer ana yin biki suka tafi America,yau wata uku kenan da yin bikin su duka.
Nasreen 'yar Ummienta da Papa(sunan da take kiran Ahmad kenan).
Sadiq abokin Ahmad shima sati biyu kenan da yin aurensa ,se Imran shima yana shiri.
2:30pm,Reyhana ta gama girkinta ta sake gyara fuskarta se turare da ta fesa mey taushin 'kamshi tayi kyau sosai dark blue d'in doguwar riga mey dogon hannu tasa se veil 'karami Pink purple data yafa.
Not more than 10min sega Ahmad ya dawo,kafin ya dannan door bell ta bud'e 'kofar,tsaya wa yayi fuskarsa d'auke da murmushi yana kallonta.
"Come in". Ta fad'a cikin sanyayyar muryarta.
Yana shigowa ta kar'bi briefcase daya ri'ko.
" Welcome back ".Ta fad'a tare da hugging d'insa,shima yayi hugging back.
" My pretty cute Azizaty ".Ya fad'a.
" Kinganki kua". Ya fad'a bayan sunyi breaking hug d'in.
"Kamar karna dena kallonki". Ya fad'a.
" Toh yanzu mije kayi shower,kaci abinci".
"As you said". Ya fad'a.
Bayan kamar 20min ya fito sanye da T shirt fara se jeans blue,tana dinning table ta gama jere abincin.
Kujera taja baya ya zauna tukun ta zuba abincin a plate d'aya." Kinci abincin ?"
"A'a". Ta amsa.
"Har 3 fah ,Allah sarki my Azizaty nasan ni kike jira"
"Bana so kike zama da yunwa fa". Ya fad'a.
" Don't worry ai bana jin yunwa tunda ba da wuri nayi breakfast ba". Ta fad'a.
"Iyye wannan baccin irin na da ne ya dawo koh".
" A'a"Ta amsa tana dariya.
"Zama de mu gano ki gama 'boye-'boyen". Ya fad'a.
" Toh yanzu de muci abinci ". Ta fad'a tare da saka musu spoon biyu a plate d'in.
Basu dad'e da gama cin abincin ba suka ji knock ,Ahmad ne yaje bud'e 'kofar ,ga mamakinsa yaga Nasreen tsaye ita da Nanny d'in makarantarsu.
" Nasreen 'karfe nawa har kin dawo meya faru ?"Ya tambaya.
Tsaye tayi tana kallonsa bata ce komai ba tayi wani kalar tausayi.
"Bata da lafiya tana ta kuka shine aka ce na kawo ta gida". Nanny d'in ta fad'a
" Toh mungode".Ya fad'a tare da ri'ko hannun Nasreen suka shigo ciki.
Reyhana se yanzu ta 'karaso taga Nasreen.
"Mey zan gani ,ita wannan mey take yi a gida 'karfe 3?"
"Wai bata da lafiya".Ya amsa.
" Zonan".Reyhana ta fad'a.
'Karasawa tayi India Reyhana take ,Reyhana ta d'ora hannunta a wuyanta taji ba zafi .
"Anya ba 'karya kike ba".Ta fad'a.
Girgiza kai tayi ta sunkuya ta'ki d'agowa su had'a ido dan dariya ce ma'kale a fuskarta bataso su gano ta.
" D'ago kanki mey kike 'boyewa?".Reyhana ta tambaya tare da d,'ago ha'barta.
Aiko tana d'ago ta ta saki dariya tana ja da baya."Dama wayo nayi wa Anty nace banida lafiya cikina yana ciwo tace a kawo ni gida".Nasreen ta fad'a tana dariya.
Ahmad ya ri'ke baki tsaye yana kallonta ,ya rasa wannan iron wayo na Nasreen 'karama da ita ta iya tsara babba.
"Aiko sekin koma yanzunnan". Reyhana ta fad'a.
" A'a".Ta ma'kale kafad'a kamar zatai kuka.
"Zonan". Ta fad'a.
" A'a rabu da ita ,abinda ta riga da ta tafi".Ahmad ya fad'a.
"Ni da kaina zan maida ta". Cewar Reyhana.
" Dan Allah ki barni bana so na koma".Ta fad'a.
"Ki barta kawai tunda ta riga da ta dawo,karki sake kinji". Ya fad'a.
Kai Nasreen ta girgiza tare da fad'in." Toh Papa".
Gefe ta ma'kale tana yiwa Reyhana gwalo."Sekije ki cire uniform d'in".Reyhana ta fad'a ta bar wajen.
Ba musu ta tafi d'akinta taje ta kwa'be kayan ta zira skirt da shirt ta fito da kayan wasanta dama abinda take so kenan.
"Ai kya samu kici abinci tukun ko".Reyhana ta fad'a.
" Bana jin yunwa".Ta fad'a.
°°°
Bayan maghrib Ahmad ya dawo daga masjid,Nasreen tana ri'ke da wayarsa se game take tun sanda ya fita.
"Ki tashi kiyi Sallah na fad'a miki". Reyhana ta fad'a sanda ta fito parlour.
" Tashi kinji idan kin iddar seki cigaba da game d'in".Ahmad ya fad'a.
"Se a d'auken photo ko?" Nasreen ta fad'a.
"Eh". Ya amsa.
Da sauri-sauri tai alwala ta zira hijab tayi sallar sannan ta dawo ta zauna.
" Papa ayi mini".Ta fad'a.
"Toh zo ai miki". Ya fad'a
Matsawa tayi aka kyasta mata ,sukai tare daga baya Reyhana ma tazo.
" Banda me kuma". Reyhana ta fad'a.
"Ummie dani za'ai"
"No ke ba mey gudun makaranta ba,matsa min". Reyhana ta matsar da it's gefe.
" Rabu da Ummie zatai sake kinji". Cesar Ahmad.
Reyhana ce ta kyasta musu iya su biyu kowannensu fuskarsa d murmushi.
*Alhamdulillah,a nan na kawo 'karshen littafinnan AR💖 ,ina mi'ka godiya ta zuwa gareku masu voting, readers 'boyayyu thank you very much.Ina godewa Allah daya bani ikon kammalawa,ina fatan an amfana da abinda ke ciki.*
Nobody is perfect
Goodbye in this story, till we met again in another story .....
Jasko💕