ARZIKI RABO Complete Hausa Novels by Dijensy.txt

Author :  Dijensy Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   12 / 21

33K to 36K   out of 61.6K words

    "Uhmm". Ta fad'a.

      Ji take kamar ta kurma ihu,hirarsa tamkar kukan sauro haka take ji.

      " Thanks". Ya fad'a.

     Thanks d'in ma cikin wani murya da bata so ya fad'a.

       Dinner d'in ma seda tayi regretting zuwa saboda Sameer,ya cika ta da surutu iya kaci tace "Eh ko a'a.

       10:39pm na bugawa ta kira Ikram suga tafi,kafin su tafi a wajen ma seda ya isheta.

     A hanya tayi ta balbale Ikram da masifa har suka is a gida ,Nasreen tuni tayi bacci da sand'a suka shiga d'akunansu kar Abba ya jiyo su.

       Sameer tun kafin tayi aure yake son Reyhana ,amma fafur ta'ki shi.Bata dad'e da aure ba ya tafi America ,befi shekara  d'aya da dawowa ba yaji labarin mutuwar auren Reyhana shine ya sake komowa har yanzu beyi aure ba ,yana da shekara 32 a yanzu.Ba fari bane chan yana da kyau shima kuma dogo ne,ba 'karamin son Reyhana yake ba gashi duk yadda takai ga shunning d'insa baya ha'kura.

    Cyprus***

         Zaune kan kujera a falo,su Imran sun d'an fita.Ahmad yanzu sun zama 'yan gari sun saba da abubuwa ,Imran dashi sun zama abokai sosai shi kad'ai yasan ya ta'ba yin aure,hakan ma wani lokaci ne daya ga pics na Nasreen a wayarsa kuma yana yawan ji yana maganarta a waya idan sunyi waya da Umma.

        Babu wani chanji sosai gameda shi na shekaru sede fatarsa data 'kara yin haske, ga gashin kansa ma da yanzu ba sosai ya fiya askeshi duka ba ,yananan luf-luf hakan yana daga cikin amsarsa da weather d'in 'kasar tayi.

       Kiran daya shigo wayarsa ne yasa ya ajje cup d'in tea dake hannunsa.

    Number ne daga Nigeria ya gani amma besan mey shiba.

            "Assalamu Alaykum". Ya fad'a bayan yayi picking.

            " Waalaikumussalm". Yaji muryar mace ta amsa.

   AR²💖

         *Toh! Readers guess who?*

   Jasko💕

       *Comment,share and vote, luv u all😘*
      
       
       

         

       

      

     

       
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍


*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣9⃣

        "Ya Ahmad ina kwana".Aka fad'a daga d'ayan 'bangaren.

         " Lafiya lau".Ya amsa yana so yayi recognizing muryar me magana.

            "Zainab ce". Ta fad'a.

             " Oh! Zainab, ban d'auki muryar ba ya gida?" Ya tamabaya.

              "Lafiya lau,ya karatu?" Ta tamabaya.

              "Alhamdulillah". Ya amsa.

              " Ina gidan Umma fah".Ta sanar masa.

             "Ok ,kuna hutu ne??" Ya tambaya.

              "Uhh ai mun kammala ma". Ta amsasa.

        " Good,Allah yasa albarka". Ya fad'a.

           "Ameen,ga Umma zakui magana". Ta fad'a.

         " Ok bani ita".

        Umma da take kusa da ita ta mi'ka mata.

        "Ahmad kaji wayata shiru koh?" Cewar Umma bayan ta ma'kala a kunnenta.

        "Eh na kira bana saminki". Ya amsa.

         " Wayar ce ta samu matsala shine nasa Zainab ta kira ka ,tazo nan gida dayake ta samu admission a B.U.K  zata fara zuwa".Umma ta fad'a.

     "Ok,yanzu take fad'a mini sunyi graduation ashe har ta samu admission". Cewar Ahmad.

      " Ehh,na sami mey taya ni zama".Umma ta fad'a.

        "Gaskiya kam,zan kira sadiq seya kai maki gyaran wayar taki".

        Hira kad'an suka ta'ba sannan sukai sallama.

                ***
     Ta 'bangaren su Reyhana kuwa Inno ta tafi garinsu anyi rasuwa,yau kowa daya tashi seya nufo dining yaga wayam.

        " Mommy kuwa ta fito?" Reyhana ta tambayi bassam da yake falo shida Walida suna kallo.

       Bassam a shekaru ukunnan ya 'kara girma sosai dan ya kere Reyhana a tsaho yana 18yrs a yanzu,Walida ma ta 'kara tsaho se siranta kamar a 'balla ta😂

       "A'a". Suka amsata.

       " Tohh! 9am fah,kace yau za'a sha yunwa kuwa".Reyhana ta fad'a tare da shiga kitchen d'in.

      Ruwan tea ta d'ora a tea pot ta komo falo tai joining d'insu.

     Ba jimawa Mommy ta sakko."Ina kwana ".Suka gaisheta a tare.

      " Lafiya".Ta amsa had'e da yin hamma.

     "Bade baku d'ora wani abu ba?" Mommy ta tambaya.

      "Ina fa,yanzu kowa yake tashi". Reyhana ta amsa.

      " Aiko yau kowa ya d'and'ana inno kunsan bata nan nima yau hutawa zanyi kwasan yadda kukai".Mommy ta fad'a.

    "Nide na d'ora tea,Ikram da Walida kuyi saura". Reyhana ta fad'a.

      Ikram tana bacci Walida ta taso ta se turo baki take ita batason aiki.

       Sageer yana fitowa daga d'akinsa yaji kiran Reyhana, sasu tayi a gaba har bassam suka shiga kitchen Mommy tai zamanta a falo.

      " Oya jeki d'ebo dankali keda Walida zaku fere"Reyhana ta fad'a.

      Sageer shi dariya ma abin ya bashi saurayi dashi wai za'a had'a da girki.Gefe guda ya tsaya ya nad'e hannunsa  yana kallan ikon Allah ,jira yake yaga shi kuma nashi aikin.

      "Toh su Sageeru se'ai blending pepper da onion". Reyhana ta fad'a tare da dire kayan miyan data d'ebo a bowl.

      Wani dariya ya fashe da ita harda ri'ke ciki." Haba kema da wasa kike ki dubi kamar ni kice nayi wani blending sekace cooku".

     "Kana mamaki koh,karkayi yaro in kasan wata bakasan wata ba".Ta fad'a tare da d'an matsowa kusa dashi ta rad'a masa yadda  su Walida baza suji ba.

       "Koh kayi ko kuma na fad'a wa Abba da Mommy d'ansu ya girma har Beb yana da ita".

         Sageer da sauri ya zaro ido yana mamakin yadda akai ta sani,what if da gaske zata fad'a ? Ya tambayi kansa.

     " Naji".Ya fad'a.

    Murmushin da yake ma ya koma ciki,turn d'in Reyhana ne se murmushin mugunta take.Su Ikram da suke jira suga zeyi ko baze ba take suka hau 'kunshe dariyarsu.

     Bassam kuma aka had'ashi da 'bare spices da za a had'a sauce d'in.

      Kowa aikinsa yayi facing Ikram se masifa take wa Walida wai tana fallatsa mata ruwa idan zata saka dankalin a ruwa.

     Sageer wai dan yayi sauri se wani cakumar attarugu yake yana cire 'ya'yan attarugun da hannu yana cillawa a blender d'in.

     Bassam mey spices har ya gama yana shirin fita ta tsayar dashi."D'an albarka  a soya wa 'yata indomie da 'kwai mana".Ta fad'a tana masa winking eye.

     Buga 'kafa yayi ya dawo se 'kun'kuni yake.

       Sageer bayan ya gama blending har ze fita yaji saman idonsa na 'kai'kayi, yatsansa ya d'ora ya sosa wheui!

    Lokaci guda ya fara dancing a tsakar kitchen d'in, Reyhana da ta d'ora kaskon suya taji 'kara.

     Kallone ya dawo kansa,Mommy da take falo ma seda ta jiyo ta shigo kitchen d'in.

      "Lafiya?" Ta tambaya.
   
      "Mommy idona!" Abinda yake fad'a kenan.

       "Kai mey ta kaika sa yaji a ido sekace yaro". Mommy ta fad'a tana dafa ha'ba.

        " Zoka tara idon a fanfo ka wanke".Reyhana ta fad'a kamar mey shirin yin dariya.

        "A daddafe ya 'karasa sink d'in yaje ya tara fuska ,duk da ya wanke idon be fasa dafe idon ba.

       " Ka tsaya mana a hure ma".Reyhana ta fad'a tana d'age ta dafe kansa sekace 'kan'kanin yaro.

      Ba su Ikram ba har Mommy seda tayi dariya,'kwace kansa yayi ya tsaya yana gogewa da hannun rigarsa.

     Ficewa yayi daga kitchen d'in ya barsu suna dariya."Maganinka kenan".Reyhana ta fad'a.  

     Kafin su gama girkin seda suka 'bata kitchen d'in, se 10:30am suka chi abincin.

     Nasreen da ta dad'e da tashi amma bata fito ba tana toilet ta saki fanfo se wasan ruwa take.

        Seda Reyhana ta koma d'aki ta jiyota,fito da ita tayi ta 'kwa'k'kwad'eta tayi ta kuka seda Abba ya rarrasheta.

       Har Reyhana tayi wanka ta shirya Nasreen bata sake hawowa saman ba,a falo ta iskesu ita da su Mommy.

      "Zo muje nayi miki wanka".Ta mi'ka mata hannu.

      Kafad'a ta ma'kale ita bazata yi ba,Reyhana ta mance ma fushi take.

      " Ki zauna hakan ina ruwa na,ki fara zuwa makaranta kowa ma ya huta".Cewar Reyhana tare da zama daga gefen Walida.

     Ba jimawa wayarta tayi ringing, tana dubawa taga Sameer.

        "Mtchww!". Tayi tsaki ta ajje wayar.

         Mommy data kula da ita tace " 'Kalau?"

       "Sameer ne". Ta amsa.

        "Toh kuma seki 'ki picking? Ni bana son wula'kanci".

         " Mommy damuna zeyi kawai".Reyhana ta fad'a.

      Se a kira na biyu neh tayi picking,bayan sun gaisa take ce mata yana bakin gate.

      "Toh ka shigo mana". Ta fad'a.

        Bata jira amsarsa ba ta katse wayar,wani haushinsa take ji.Yana shigo bayan sun gaisa ta koma d'aki taja hannun Nasreen da se surutu take masa.

               ***
   Har Sameer ya tafi bata fito ba tana d'aki.Da yamma Aunty Asma'u tazo gidan Mommy.

        " Ya kuwa wannan mutanen har yanzu shiru?" Anty ta tambaya.

       "Hmm har yanzu, duk tsahon shekarunnan da aka shafe shiru koh waya basu sake yi ba". Mommy ta fad'a.

      " Amma wannan basu da mutunci,ace ko kira suji lafiyar 'yarsu bazasi ba balle akai ga ha'k'ko'kinta kuma,wannan akwai mutanan banza,ita Reyhana idan ta kirashi baya amsawa neh?" Anty Asma'u ta tambaya.

      "Toh wayar ta samu tashiga ma tukun,kuma idan ma an sameshi tace masa meh?" Mommy ta 'kare da tambaya.

     "Tuna masa zatai ba dutse bace 'yarsa ,su wannan da wane idon ma zasi kalli yarinyarnan? 'yarda a yanzu idan ance babanta bata sani ba".

     " Ita ajinta kakanta ne Abbanta ai,barsu su cigaba da yanda suke so lokaci zezo zai nemi 'yarsa aikoh".Cewar Mommy tana jinjina kai.

               ***
     2 days later

       Zainab around 9:30pm lokacin tana d'aki Umma ma ta kwanta,wayarta ce a hannunta tana chat a Whatapp.Contact take dubawa idanta ya tsaya kan sunan "Ya Ahmad" kamar yadda tayi saving.

     Tana gwada bud'ewa taganshi online,haka kawai ta tsinci kanta tana son yi masa magana,typing tayi ta tura masa sa'ko kamar haka;

"Assalamu Alaykum,ina yini".

   Seda aka shafe kusan 10min yayi reply dan har ta fita daga profile d'insa.

        Ahmad be kula da message d'in ba da wuri,ganin  "Xynab" kamar yadda yayi saving yayi reply da;   
      
                   "Wa'alaikumussalam,lafiya lau".

      " Ya kke? Ya school ?"Ta tura.      


    "Alhamdulillah,ya kuke ?" Shima ya tambaya.

"Lafiya lau".Tayi replying.

" Ina Umma koh tayi bacci?" Ya tambaya.

    "Eh". Ta amsa.

      " Ok". Ya amsa.

Yatsa ta sa a baki tana tunanin mey zata kuma cewa ,kusan 2min basu sake magana ba.

    "Kin fara zuwa school d'in?" Ya tambayeta.
     
 
Murmushi ta fara yi ganin ya sake mata magana wanda bata zata ba.
     
   
   "Se Monday". Ta amsa.

" Ok,wani course?"Ya tambaya.

"Industrial chemistry". Tayi replying.

" Good👍 Allah ya bada sa'a".Yayi sending.

"Ameen, tnx". Tayi replying fuskarta d'auke da murmushi.

  " It's 10pm right? You should have sleep.

"Yaya by 11:00 dae koh". Tayi sending.

" 😱 it's late ,what will you do?"

"Ha! Chatting with you mana". Ta tura.

     " Are you sure? "Yayi sending.

    " Yes mana don't you believe me?"

"I do believe, ok am quitting now".Ya tura.

" Ok,nima yanzu zan kwanta".

"Gudnight ,recite du'a before sleeping".

" Tam night,bye".Ta tura.

Kamar yadda yace tayi addu'a tukun ta kwanta,shima ajje wayar yayi ya dauro alwala ya tada sallah.
     

AR²💖

     *Comment,share and vote pls.Luv u all😘*

Jasko💕      
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍


*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣0⃣


    Alhamdulillah we reach page 20,happy page twenty🎈🎈   Umeeyr tace "Zainab want to snatch our ya Ahmad " 😂
Juma'at Kareem.

     Reyhana kwance a kan gado ,Nasreen na manne da jikinta ta zagaye hannunta a bayanta da hannin damanta na hagunta kuma tana shafa mata gashin kanta,Nasreen da tayi nisa da bacci hankalinta kwance.

       Babu rana da zata wuce Reyhana batayi tunanin Ahmad ba,idan ta tuna shekarun da aka shafe basu sake had'uwa ba kuma ba waya seta ji haushinsa wani 'bangaren zuciyarta kuwa har yanzu da gurbin sa a ciki."Meyasa ze guji 'yarsa? Mey Nasreen tayi masa a duniyannan daya watsar da ita?" Abinda kullum take tambayar kanta wanda amsar hakan ta gagara.

       Bata yi aune ba taji danshi a fuskarta,hannun ta sa da goge hawayen ,the more tana gogewa the more yana sake fitowa dan haka ta dena mah,gam ta sake ri'ke Nasreen a jikinta tare da d'ora ha'barta lightly a goshinta ,idonta ta rufe gam ba jimawa bacci yai gaba da ita.

                 ***

    Zainab 8am ta tashi dan bata fiya bacci dayawa ba bayan subh,kamar kullum a nitse tayi shara ba tare da Umma ta tashi ba,haka toilet ma ta wanke sannan ta koma d'aki.

       8:20am,wayarta dake jone a charge ta zare.Chat da sukai da Ahmad jiya ta shiga dubawa a hankali step by step tana sake karantawa tana murmushin.

       Data tayi switching on ko zata ganshi online,koda ta duba taga be hau ba tun jiyan.

       Tana jiyo fitowar Umma daga d'aki ta ajje wayar ta fita,cikin rissinawa ta gaisheta.

      "Zainab da sassafennan kika tashi harda shara".Cewar Umma.

      Murmushi kawai tayi ba tare da tace komai ba." To sannunki da 'k'o'kari".Umma ta fad'a.

       Har abincin breakfast tare sukai da ita,ko wanke-wanken ma bata bari Umma tayi ba ,haka Umma tayi ta shima ta albarka halin Zainab yana birgeta.

            ***
    Kiran Sameer ne yau ya tashi Reyhana 8:47am taji 'karar wayarta.

      "Hello". Ta fad'a bayan ta d'aga muryarta a cushe.

       " Morning ". Ya fad'a.

       " Morning ". Ta amsa rai a 'bace.

      " Tun d'azu nake jiran 9 yayi sena kira ki amma  I can't even wait,just want to know how you're doing ". Ya fad'a.

      " Am ok". Ta amsa kamar ta sha'ke shi.

     "Nasreen fah is she awake?" Ya tambaya.

      "Ya Allah". Ta furta a ranta dan ta gaji da amsasa ,magana da safe aiki yake mata haka kurum ma balle da Sameer.

       " Bata tashi ba nima bacci nake". Ta fad'a.

      "Oh am sorry na tashe ki,I just can't wait to hear your voice"

        "Uhmm". Ta fad'a.

        " Ok mayi waya anjima,yanzu ki koma bacci kinji bye". Ya fad'a.

         Ko amsasa batai ba tayi hanging taja tsuka.Baccin ma se ha'kura tayi.

      Tun kafin ta 'karasa sakkowa take jin hayaniyar su  Sageer.
  
        "Ku kuma kun cikawa mutane kunne daga tashi". Ta fad'a bayan ta sakko.

         "Hira muke me dad'i". Cewar Ikram.

         " Ni rufen baki". Ta fad'a tare da nufa kitchen.

     Mommy ta tarar tana had'a breakfast, tama kusa gamawa nan ta taya ta suka gama.

   °Cyprus°
 
       Yau Ahmad ba class saboda haka shida Imran suk a fita zagayawa bayan sunyi breakfast.

        Imran ya takura Ahmad seyayi pic,kusan seyace be ta'ba gani ya tsaya yin pic ba a hanya.

        "Kawai d'aya zakai,haba ko Umma ai ka turawa taga d'an handsome d'inta". Imran ya fad'a yana dariya.

       " Malam rabi dani". Ahmad ya fad'a yana cigaba da da tafiya.

        Imran daya tsaya daga can baya ya 'kwala masa kira.Shi ya zaci ko wani abune ,yana juyawa yaga flashing camera.

        "Wow! Kaganka kuwa". Cewar Imran yana 'karasowa inda yake.

         Ahmad a jikin pic d'in ya zira  hannunsa d'aya a aljihu hakan ya bada style sosai gashi fuskarsa da d'an murmushi (If u want to see the pic comment with yesss let me see who fall for Ahmad😂).

      "Let me know idan kana son pic d'in kai magana na turo ma,if not senai posting a insta kaga baza a rasa masu so ba". Ya fad'a.

      Ahmad jin ya ambaci insta yasa ya ciro wayarsa ya mi'ka masa.

           " Ha! Better ". Imran ya fad'a.

           Sun d'an zazzaga gari tukun suka komo gida.

       Su Ibrahim kuwa dama jiran dawowarsu suke coz suke da kitchen😂

         " Alhamdulillah gashi ya dawo".Ibrahim ya fad'a.

       Shi Ahmad ma ya manta shaf inba yanzu da sukai magana ba.

       "Maza yau mey za'a dafa mana neh?" Idris ya tambaya.

        "Se abinda kuka gani". Ya amsa.

         "Nikam yau d'an wake nake son ci". Cewar Ibrahim.

          " Nikuma sakwara".Idris ya fad'a shima.

         "Nikam dambu". Imran ya fad'a.

         " Kun dad'e baku ci ba".Cewar Ahmad ya watsa musu harara.

        Dukansu dariya sukai daman salan sashi magana ne.

         D'aki ya shiga ya rage jacket d'in daya d'ora kan kayanshi sannan ya fito zuwa kitchen.Seda yai kusan 5min yana tunanin abinda ze girka, idea ya d'auke yau da gobe ta'ki wasa sun gaji da abinda suke dafawa.
   

12 / 21