Chapter 13 Reading ARZIKI RABO Complete Hausa Novels by Dijensy.txt Arewa Novels

ARZIKI RABO Complete Hausa Novels by Dijensy.txt

Author :  Dijensy Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   13 / 21

36K to 39K   out of 61.6K words

  
      Fridge ya bud'e yana kalle items d'in ciki,idea neh ya fad'o masa ya d'akko wayarsa yai searching nan ya gano stew na cous cous
       
       "Butter nut squash and White bean"
        
     Daya duba yaga suna da items da ake bu'kata,ba tare da 'bata lokaci ba ya fara had'awa.

         Kitchen yayi kaca-kaca everything scattered Maza! anyi girki😂

       1hr later table is complete lunch is ready,Imran shi ya fara serving su Idris da 'kamshi ya bigi hancinsu suma suka d'ibi nasu.Ahmad kallonsu ya tsaya yi yana jira yaga ya taste d'in abincin nasa ze kaya.

       Imran spoon d'aya yakai baki yana tattaunawa still bece komai ba,alama Ahmad yayi masa da gira "yaya?"

        "That's yummy! bro"Imran ya furta yana sake d'iban wani loman.

        " Kai dama kasan da wannan kake barinmu da jollof?" Cewar Idris.

       "Wannan anyi mugun mutum". Ibrahim ya fad'a bakinsa cike da abincin.

       Bece komai ba se murmushi kawai dayake shima yaja plate ya ziba.

       Bayan sun gama ya koma d'aki,in less than 2min sega kiran Xynab.

          " Assalamu Alaykum".Tayi sallama.

         "Waalaykumussalam". Ya amsa.

         " Ina yini".Ta gaishesa.

          "Lafiya".ya amsa.

           " Ga Umma zaku gaisa".Ta fad'a.
           
           "Bari na kira". Ya fad'a tare da hanging.

       Baya so yai exhausting credit nata tunda alhamdullillah ana basu allowances.

         Umma ce tayi picking bayan ya sake kira,nan suka gaisa sun jima suna hira da ita kafin daga bisani sukai sallama.

                 ***

 Zainab  tun chat da sukai rannan basu sake yiba har ta fara zuwa school kuma yanzun an gyara wayar Mommy dan haka bata sake kiransa ba,shima test da yake dashi kwana biyu yasa baya hawa chat.

       Kusan about 2weeks kenan ,Zainab an 'kwame gaban mirror ana tsara d'auri farar fusakarta tasha make up as always bata fiya zama ba janbaki ba se kwalli shima bata fashin sawa ko ba fita zatai ba.

       Zainab itama tana da nata irin kyan most her exciting lips O shape matsakaicin tsaho gareta and ba siririya bace a murje take but not fat whoo! (Don't ask me about her hair fah,idan nace muku Fulani ce you know kawai!
😁)

       Ko breakfast bata tsaya tayi bama,12:30 sun fito daga class a cafeteria suka tsaya it a da friend tata koda taci abinci wayarta ta d'auko ta bud'e whatapp luckily taga Ahmad online wani farinciki ne ya ziyarceta.

Xynab: "Hello"

" Hi".Yayi replying bayan  1min.

Xynab:"Ya school?"

Ahmad:"Alhamdulillah".

Xynab:  " Ni baka tambayi nawa school en ba". Ta tura bayan kamar 3min.

Ahmad:"Ohh ya school? ".

Xynab:" Seda na ro'ka

Ahmad:"Sorry". .



Xynab:" Is OK".

Xynab:"Toh kai wani course make studying?"

Ahmad:"Computer science".

Xynab:" Nyc".

Ahmad:"Where are you now?"

Xynab:"School".

Ahmad:" At school and you are chatting? "

Xynab:"Ai bana class".

Ahmad:" where? "

Xynab:"Guess!"

Ahmad:"Hmm masjid"

Xynab:"No"



Ahmad:"Ok,school compound"

Xynab:"Hhh No"

Ahmad:"Then where?"

Xynab:"So you gave up"

Ahmad:"Uhmm"

Xynab:"Cafeteria".

Ahmad:" Acici"

Xynab:"Am not😞"

Ahmad:"Are you really not?"

Xynab:"Yes"

Ahmad:"I take back my word,Ok for you?"

5min silent batai reply ba,kuma bawai ta fita bane tana so taga ze damu.

Ahmad:"Hello are u there?"

Xynab:"Uhmm"

Ahmad:"I said am sorry "

Xynab:"😝"

Ahmad:"Hmm Xynab"

Xynab:"What??"

Ahmad:"Nothing"

Xynab:"Please say it"

Ahmad"U are acting childish
😁"

     Xynab:  "Am not"

Ahmad:"OK let see,how old are you?"

Xynab:"😯"

Ahmad:"Look at you girl,you think I don't know?"

Xynab:"Yes😕"

Ahmad:"Look at you ,I even..."

Xynab:"Yaya what?"

Ahmad:"Forget about it 🙊"

Xynab:"😱"

Ahmad:"Time up,prayer time"

Xynab:"OK"

Ahmad:"Bye"

Xynab:"✋"

Gaahide ya sauka amma ya kasa dena murmushi,Zainab had seda 'kawarta Siyama tayi tapping d'inta ta dawo daga tunanin data tafi wata duniyar.

       She can't stop blushing yau tayi chat da Yaya conversation d'in ya mata dad'i ."Ashe yana magana haka" Ta fad'a a ranta.

                    ***
    Reyhana koyaushe Sameer seya kira baya damuwa zata d'aga ko bazata d'aga ba.

      Sageer daba school yanzu take zuwa ba tinda ya gama  Ikram da ya rage mata 1yr kullum fama take da Sageer wajen kaita school ,Reyhana idan 'yan mutuncinta sun tashi wasu lokutan tana kaita.Yau ma ta shirya Sageer take jira jin shiru yasa Reyhana ta tashi taso shi dan idan Ikram da kanta zata rashin mutunci yake mata.

        Koda ta Shiga ta tatar yana bathroom ,har zata fito ta hangi wani rose flower akan mirror, dan san gulma da sauri ta 'karasa wajen ,rose d'in ta d'auka taga  greeting card daya sha ado cover d'in da heart kala-kala a ajje.

       "Lover boy". Ta furta a fili.

     " Yaya!" Ya kira ta da 'karfi tare da 'karasowa ya wafce rose d'in da card.

     "Iyee wata za'a kaiwa wannan Sageer?" Ta tambaya tana murmushi.

   "Babu". Ya amsa yana turasu a drawer.

" Idan baka fad'a min ba a bakin Abba Yaro".

   "Kai dan Allah waike.."

    "Yanzu de fara fita ka kaita school idan ka dawo mayi maganar lover yaro". Reyhana ta katseshi tare da fita tana dariya.

AR²💖

            *Whooo! how is the page?? Tell me what is about to happen BTW the two two😂 A&Z, S&R ❤*

choose whoaa!

*Pls comment,share and vote.*

Jasko💕
           
 
    
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍


*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*



🅿 2⃣1⃣



     Zainab yanzu har ta saba ma kanta inde batai chatting da Ahmad ba bata jin dad'i,duk ranar friday kuwa seta kirashi sun gaisa.Umma har ta soma gano wani abun gameda Zainab dan ta tana lura da ita bata da zance sena Yaya Ahmad.

      Har pic d'insa ta saka ya turo mata wai duk sunan Umma ce zata gani dukda kuwa ba haka bane.Tun bata gasgata abinda zuciyarta ta fad'a yanzu ta yarda she fall for him.

                ***
Reyhana ce tsaye  hannunta ri'ke da yarinya ,a hankali ya 'karasa inda suke a tsayen.Koda ya isa wajensu ya tarar sun juya masa baya.

        "Reyhana". Ya kira sunanta cikin sanyin murya.

         A hankali ta juya fuskarta cikeda hawaye da nuna alamar damuwa.Kallonsa ya mayar kan yarinya ,a hankali ta waigo sede fuskarta ba komai(Hollow)

   A razane Ahmad ya farka,lokaci guda ya had'a zufa .Agogo ya kalla yaga 2:30am ,jikinsa a sanyaye ya shige bayi ya d'auro alwala ya tada sallah.

        Ko bayan ya idda sallar ya kasa komawa bacci,mafarkin da yayi ne yake ta masa yawo a kansa.

      " Koh wani abun ne ya faru?" Ya tambaya a zuciyarsa.

       "I have to call Reyhana  tomorrow morning".

        Wayarsa ya d'akko ya shiga gallery,photo na Nasreen tana baby ya bud'o yana kalla,hannu ya d'ora kan fuskarta yana shafawa a ransa yana ta sa'ke-sa'ke.Wayar na hannunsa bacci ya saceshi ,kan 'kirjinsa ya kifata ya soma bacci.

         Washegari da safe bayan yayi breakfast ya shige d'aki.Wayarsa ya d'auko ,number d'in Reyhana ya sa a wayar dan numbern ta baze goge a memoryn kansa ba.Da 'kyar ya samu yai dialing sede bata fara shiga ba ya katse.

      Kusan seda ya maimaita haka yafi sau hud'u amma sam baida courage yana tunanin ta ina zai soma magana kuma mey ze fad'a mata? Ya fad'a a ransa.

      Haka ya ha'kura da kiran ya ajje wayar gefe yana mey jin haushin kansa, da ace be d'au tsahon wannan lokacin ba da ba abinda ze hana ya kirata.

      Umma ya kira suka gaisa se sadiq shima dan sun kwana biyu basi waya ba.

               ***
Reyhana 'kawarta saudat ta haihu yau ake suna last two years tayi aure.

       Nasreen se tsalle take yau za'a unguwa da ita ta ishi kowa da maganar duk wanda ta gani seta fad'a masa Ummienta zata unguwa da ita dan Reyhana bata fiya fita unguwa da ita ba gara ma Mommy.
     
     
    3:30pm ta shirya ,itama Nasreen an shiryata tayi kyau sosai kamar a d'auka a gudu.

       Sallama sukai da Mommy suka fita.Ko barin layinsu batai ba mota ta tsaya yin duniya ta'ki tashi.

       Gashi Sageer baya gida balle ta kirashi ya kaita Mommy kuwa ta dena basu motarta.

      Tana cikin tunanin yadda zatai sega motar Sameer ta doso layin.

       "Shikenan kuma anace yazo". Ta fad'a tare da dukan steering motar.

        Aiko yana ganin motarta ya tsaya,yasan ko ya sauke glass d'in motarsa ba sauke nata zatai ba dan haka ya fito.

      Se da taga yazo daf ta zuge glass d'in.

       "Fita zaki ?" Ya tambayeta.

         Kai ta girgiza masa alamar "Eh".

        " Ok,but amma kamar motarki ya samu matsala koh?"

       "Eh amman zan samu napep". Ta fad'a dan karma yai mata tayi.

       " You don't need that,am here Reyhana senai dropping d'inki wajen da zaki". Ya 'kare maganar da murmushi.

       "No Sameer thanks don't worry zan tafi da kaina". Ta fad'a.

       " Reyhana come on ni nace fah'.Ya fad'a.

        "Sameer..."

          " Please".Ya katseta.

           "Ok". Ta furta.

     Dande ba yacca zatai neh kuma batason missing zuwa shiyasa dole ta ha'kura ze kaita.Baba mey gadi tasa ya kira mata mey gyara kafin ta dawo.

       Se janta da hira yake amma bata wani responding sosai " Eh" ko "A'a" shine abinda take amsasa. Ya rasa gane wace irin mace ita,har yanzu bata chanja ba tana nan da halinta ,sekace yau ta fara ganinsa.

    Rabin hirar ma da Nasreen sukai ,yana kaisu tace ya tafi zata kira Sageer yazo d'aukansu.

      ***

  Zainab yauma taci sa'a Ahmad na online, waje na musamman ta samu ta 'kule 'kuryar d'aki an d'auki pillow an d'ora a cinya ta aza hannunta akai se tapping phone take.

        Xynab: "Yaya an bamu wani assignment naso ace kana nan da ka koya min".

    Ahmad:" Hmm".

    Xynab: .Yaya wai me hmm d'innan take nufi da anyi magana sekace hmm".

    Ahmad: "Sarkin tambaya ".

Xynab: " Eyi ina so na sani".

Ahmad: Haka kike a school? "

Xynab:"Yes 😀"

Ahmad: "Ok, kina nufin kice duk wannan samarin class d'in naku haka kike musu koh"

Xynab: "Laa! 😱 Yaya ni bana kula mazan class d'in mu fa ,ni idan bakai bama ba wanda nake kulawa".

Ahmad:"Hmm".

Xynab: "Ka ganka koh😒"

Ahmad:"Stubborn ".

Xynab:" Naji,yaya saura wata nawa ka dawo?"

Ahmad: "Mey kika tanadar mini?"

Xynab: "I just ask".

Ahmad :"not more than 9"

Xynab: "😱har 9"

Ahmad: "Yayi nisa?"

Xynab: "Sosai,kai bama ka damuwa".

Ahmad:Toh ya zanyi inma na damun?"

Xynab:Umma kam tana kewarka"

Ahmad: Umma kad'ai?"

Xynab:"Uhm.."

   Ahmad :Wannan sister tawa batai missing d'ina ba".

A ranta seda taji ba dad'i ,ita bataso yake ce mata sister gara ya kira ta da sunanta.

Xynab: "I do mana🙈"

Ahmad: "Uhm harda rife ido".

Xynab:"...."

Ahmad: "Mey hakan yake nifi?"

Xynab: "😝😝"

Ahmad: "Kin ganki koh,shiyasa nace maki.."

Xynab: "Kace ni yarinyace koh? Yaya university fa nake kuma wanda yake 17yrs shine za'a kirashi yaro ? nide ba yarinya bace😠"

Ahmad :"Hhh just 17 ,sannu aunty Zainab"

Xynab: "😭😬 kuma an dena chat d'in".

  Kusan 5min bata sake typing ba shima haka,ganin da gaske take dan yaga alamar ta sau'ka seya kira.

      " Hello".Ta fad'a ciki-ciki.

      "Ayya sister sorry am just joking". Ya fad'a.

      Boom! Taji zuciyarta tayi alert ,wani tsantsar sonshi ne ya sake shiga zuciyarta,yanayin yadda yai magana ne yayi mata dad'i  dan bata ta'ba ji yayi irinta ba(Ahmad fa ya manta bada Reyhana yake magana ba😂)

        " Na'ki d'in". Zainab ta fad'a cikeda shagwa'ba.

        "Please". Ya fad'a.

         " Toh a koma chat tukun".Cewar Zainab.

         "No,sekin ha'kura.Ya fad'a.

           "Toh idan na ha'kura baza ka sake cemin yarinya ba?"

         "Bazan 'kara ba". Ya amsa.

           "Toh na ha'kura". Ta fad'a.

           " That's my zee". Ya fad'a shi kanshi besan lokacin ba.

      "Wannan wata irin su'butar baki ce ta sameshi?" Ya fad'a  a ransa.

      Zainab ta kasa sake cewa komai dan ruwan kanta ya 'kone what if shima yanda take ji haka yake ji? Kai amma da tafi kowa jin dad'i.Du ita kad'ai take zancenta a zuciyarta.

       "Zainab are you there?" Ya tambaya.

       "Eh". Ta amsa a hankali.

        " Bacci koh?" Ya tambaya.

          "Uhm". Ta amsa duk da ba baccin take ji ba kawai de over happy yasa wayar ma ba zata iya ba a yanzu.

            " Ok,toh kiyi addu'a ki kwanta". Ahmad ya fad'a.

         "Toh ,seda safe". Ta fad'a.
   
       Shima seda safen yace tukun yayi hanging.Da 'kyar ta iya saita kanta ta kwanta wayarta a gefen kanta tayi bacci dan pic nasa da imran yai masa ta 'kura ma ido tayi ta kalla.

      Yana ajje wayar gefe ya lura da Imran da yai tsaya yana wani murmushin na tarfo ka.

        " Mey kake kai kuma bakai bacci ba?" Ahmad ya tambaya yana wayancewa.

          "Mallam ba abinda zaka 'boyen,na jiyo ka". Imran ya fad'a.

          " Kaji mey? "Ahmad ya tambaya yana nuna be san komai ba.

         " Karka rainan hankali ka gane mey nake nifi,kullum ace sister toh yau 'karyarka ta 'kare".

      "Idan ba sister ta bace taya zance maka haka".

      " Ai shiyasa naji kana kwantar da murya ,ashe kaima ka iya, ko dayake dama ance irin ku.. "

    Be 'kare ba Ahmad ya cilla masa pillow a fuska.Dariya yai tayi sannan yace.

      "Gara ka lalla'bani ka bani labari idan ba haka ba na fallasa magana gun wa'ancen kasan su baza su raga ma ba".

        "Allah Imran ba wasa nake ba ni ba wani abu tsakanina da Zainab kawai na d'auketa a matsayin sister ne". Ahmad ya fad'a fuskarsa ba alamar wasa.

       " Hmm ai daga sister d'in ake zarcewa,kuma ni ai hakan ma dad'i yayi mini kaga du sauran damuwarka na past zaka manta dashi".Imran ya fad'a.

       "Na fad'a maka ni aure ma baya gaba na,koda ace na gama karatu ba aure zan bafa". Ahmad ya fad'a.

      " Kasan kaima hakan baze yiwu ba mahaifiyarka bazata bar hakan ba,akan wata bazaka kashe life d'inka ba".


       "Who knows ma koh ita tayi nata auren,saboda haka kawai ka bawa Zainab dama bakasan irin alkairi dake tattare da ita ba kuma koh a yanzu kasan she is a kind person".

        " Imran please let not talk about this now,bacci nake ji".Ahmad ya fad'a.

      "Ok ,amma kayi tunani". Imran ya fad'a tare da nufar nashi gadon.

      Ahmad sam bawai baccin yake ba kawai de ya kwanta ne ,kalaman Imran sun basa tsoro mussaman maganar " Who knows ma ko tayi nata auren".Abinda ya tsaya masa a rai kenan.

       "What if abinda ya fad'a gaske ne,3yrs zeyi wuya ace bata sake aure ba,but Zainab? toh ita Zainab damage tana da feelings a kaina ne? taya zata so ni? taya zan aureta ma yarinya ce fah? No this is not possible". Da wannan tunanin yayi bacci.

AR²💖

*Please vote, comment and share.Love u all😘*

Jasko💕

         
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍


*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣2⃣


      Ahmad tun sanda sukai chat da Zainab be sake hawa online ba yau sati d'aya.Yana so yayi avoiding d'inta yana mey tsoron kar maganar Imran ta tabbata,d'azunma yana ganin kiranta amma ya'ki picking.

       Littafinsa ya d'auko ya soma karatu su Imran sun fita shi kad'ai ne a gidan.Kiran Umma ne ya shigo wayarsa,da farko yayi tunanin koh Zainab ce seya share,se a kira na biyu ya duba yaga Umma.
  
        "Umma ina kwana". Ya gaisheta.

        " Lafiya lau,ya karatu?"Umma ta tambaya.

        "Alhamdulillah". Ya amsa.

         " D'azu muka dawo daga asibiti Zainab bata da lafiya". Umma ta fad'a.

         " Toh! Meya sameta?"Ya tambaya.

         "Malaria neh". Ta amsa.

          " Allah ya sawwa'ke".Ya fad'a.

          "Ameen". Ta amsa sannan sukai sallama.

      " Shiyasa ta kirani ashe,Allah sarki".Ya fad'a a ransa.

     Dialing number d'inta yayi amma batai picking ba kusan 3× dole ya ha'kura a ransa ya ayyana ko fushi tayi tunda taga ya amsa kiran Umma.

      Karatunsa ya cigaba dayi se bayan 1hr tukun ya sake kiranta ,se a karo na biyu ta d'aga.

      "Assalamu Alaykum"

       "Waalaikumussalam". Ta amsa a hankali.

        " Zainab ".Ya kira sunanta.

         " Uhm".Ta amsa a ciki.

          "Ya jiki?" Ya tambaya.

           "Naji sau'ki". Ta amsa.

   Sunfi 2min ba wanda ya sake cewa komai.

       " Am sorry d'azu bana kusa da wayar lokacin da kika kira".Ahmad ya daure ya fad'a.

       "Uhm na gane".Ta fad'a.

        " Kinsha magani?" Ya tambaya yana so ya chanja topic.

      "Eh nasha". Ta amsa.

      " Toh ki daure ki dinga cin abinci kinji".

       "Tahm". Ta fad'a.

       Daga haka sukai sallama,ta ajje wayarta befi 1min ba message ya shigo.

    " Get well soon Sis"

     Lokaci guda ta saki murmushi ,har cikin ranta taji dad'i ya damu da ita.

                 ***
     Reyhana ce a d'aki ta ciga tayi fam haushin ya isheta saboda Abba yayi mata zancen Sameer.

      Mahaifiyar Sameer da kanta tazo wajen Mommy sukai maganar Reyhana Mommy kuma ta fad'a wa Abba abinda yake faruwa.

     Tana cikin wannan yanayin Walida

13 / 21