Author : Miss Hajo Category : Romantic Hausa Novels
/>
Shidai Ashraf bai ce komai ba amma har yanzu ransa ɓace ya ke ya na zaune saudat ta shigo da ƙatuwar akwati ya ɓalla mata harara ta turo masa baki ta na miƙawa Abba Passport ɗin ya amsa tare da cewa”shige ciki abinki ki zaɓi Ɗakin da duk ya yi miki a dafa miki abinda kike so ki samu bacci ki huta Allah miki Albarka”
Ta amsa da “Ameen Abbanmu”
Ta na nufar ciki da sauri ta na murmushi,
Ummy ta yi murmushi ta na girgiza kai ta san don ya ƙara ƙular da Ashraf ya ke haka Wanda ko zuciyar Ashraf ɗin kamar ta fashe don haushi ciki-ciki ya yi musu sallama ya fice”
Lokacin wata kyakyawar farar budurwa mai matuƙar kama da ummy ke saukowa daga stairs Ɗin bene kai tsaye wajen Dad ta nufa ya na wara mata hannu da murmushi a fuskarsa ta ƙarasa ta na ƙarasawa tare da basa hug ya ce”I really miss you Auta na since yesterday at 9 pm rabon da na saki ido na”
Ta na sakin rungumar tare da zama gefensa ta na kama hannunsa duka biyu ta ce “i miss you too Abba yau tun asuba akace ka fita kuma na tafi school sai yamma na dawo Abba gobe ina son zanje Hospital gaishe da marar lafiya daga scool”
Da damuwa a fuskarsa ya ce “waye ba lafiya”
Ta ce “Abba ka tuna Besty Safa Aminiyata “
Ya ce “eh waye bai san Safa Aminiyar Auta ba a gidan nan”
Ta ce “To Cousin sister ɗin ta ce Ba ta da lafiya kwana biyu ba ta zuwa school shine jiya ta ke sanarmun jinya suke a asibiti Cousin ɗinta ba ta lafiya shi ne ɗazu na kira na ji ya me jikin na ji ta na kuka wai kwana ukku ba ta farfaɗo ba Abba karkaga yanda safa ke son sister ɗin nata ko ni ta na yawan yimun hirarta ban taɓa ganinta ba amma Abba na tausaya mata shiyasa zanje na duba ta gobe”
Abba ya ce “Ya Allah ya Bata Lafiya ohh nima koda bansanta ba na tausaya mata Allah bata lafiya to amma me ya sameta har kwana ukku ba ta farka ba”
Ta na ƙara narke Fuska ta ce “nima bansani ba Abba “
Ya ce “to Allah ba ta lafiya”
Ta amsa da “Amen “
Ummy ta kalla da ta tashi ta na miƙowa Abba abun sha ta ce “Ummy bakice komai ba”
Ta ce”Allah ya bata lafiya Auta ai ya kamata kije ki kwanta da wuri tunda kince tun 7:30 kike da C A”
Ta na shagwaɓe fuska ta ce “Nidai Ummy sai yaya yazo tun da akace ya dawo Ƙasar ban gansa ba”
Ummy ta ce “to Allah sa yadawo da wuri”
Ta ce “amen ta na juyawa sun cigaga da hira da Abba,
Minti talatin saiga Sallamar marzouq tare da Ahmad da ke goye da Tasnem da tagaji da kukan bayan sun biya ya kai su shan ice cream a hanya ta yi bacci”
Da sauri Lena ta ruga da gudu ta na rungume sa ta ce “Missing you alot yayana “
Ya na shafa kanta ya ce “Miss You too Autan Abba “
Ummy na kallon Ahmad ya ce “itafa wannan na ga fuskarta duk hawaye ta yi bacci haka”
Ya na tura baki ya ce”Ummy daga fa mun raka Daddy duba marasa lafiya shine ta haɗu da wata yarinya age mate ɗinta suka dinga wasa wai da zamu taho ta dinga kuka ita saidai a bar ta a chan “
Ummy na amshe ta ta ce “Allahsrk Tasnem akwai son ƴa mace ko dan ta ga ita kaɗai ce mace a yaran ba ri na miƙata wajen mamanta kafin ta kalli Lena da duk ta maƙalƙale Yayanta daƙyal ma ta ƙyalesa suka gaisa da Abba ta ce “ba surutun banzan zaki zauna kina masa ba ki kai masa abinci part ɗinsa tare da Fruit salad ɗin Da na haɗa masa mu kwana lafiya”
Ta na barin wajen Marzouq ya ɗanyi murmushi ya san har yanzu ummy fushi ta ke dashi akan maganar aure da tayi masa kafin ya bar ƙasar a ransa ya ce”za ma ki sauko ummy amma aure kam ni da shi har Abada”
Lena ta miƙe ta ce “muje yaya na kai maka sai ka cinye tas a gabana kafin na ƙyaleka”
Abba ya ce”idan ya ƙi cinyewa kiyi masa ɗure Autana”
Marzouq ya yi murmushi ya na sallama da Abba ya fice Lena ta bi bayansa da Warmers ta na ta masa surutu ya ƙyaleta don ba ya iyawa da surutun Lena yau agajiye ya ke,
Tsarin part ɗinsama kaɗai abun kallo ne domin wasu ƙasaitattun kujeru da carpet tare da labulaye sai Frames da lamps da centre table da ƙatuwar plasma wacce ni tsawon rayuwata ma bantaɓa ga irin ta ba ,Part ya matuƙar haɗuwa da ƙayatuwa,
saida Lena ta tabbatar ya ƙoshi kafin ta ƙyalesa shima don gyangyaɗi da ta fara ta na miƙewa ta ce “yaya saida Safe Gobe da safe daga school zanje hospital duba cousin ɗin ƙawata”
Ya na miƙewa tare da shigewa bedroom ɗinsa ya ce”Allah ya kaimu”
Wanka ya yi bayan ya sauya kaya ya na Feffeshe jikinsa da mabanbanta Turaruka Ya kwanta domin akwai gajiya tattare da shi ya na buƙatar hutu Ga mamakinsa Yarinyar da ke kwance gadon asibitin maƙale da na’urori take masa gizau Da ya rumtse ido sai ya ganta lokacin da ya je dubata “
“Me hakan ke nufi”?
“Tausayi”?!
Wata zuciyar ta ba sa amsa ,
“Ciwon Zuciya “Maganganganun Sanata Bashir Dikko game da ciwon nata ya ji suna masa gizau a kunne ,
“Me zai haɗa yarinya ƙarama da larurar Ciwon zuciya”?
Me ya haifar mata da ciwon meye Sila “
Sanin bashi da mai bashi amsa ya sanya wa zuciyarsa ƙoƙarin sharar da batun
Ya kai 30minutes kafin wani bacci mai cike da gajiya ya kwashe sa cike da mafarkai Kala-kala,
Kamar yanda ya saba bayan sallar asuba Al-Qur’an ya ke ta karantawa har gari yayi haske kafin ya yi shirin fita exercise a 30minutes ya yi ya dawo kafin ya yi wanka ya shirya cikin wani blueblack yadi da yayi masifar masa kyau sai baza ƙamshi ya ke,
Kallon agogon dake maƙale a hannunsa ya kalla ya ga 8:30 sashen iyayensa ya fita lokacin Abba na shirin fita suka gaisa kafin ya ƙarasa ya na jiran ummy tadawo daga raka Abba,
Ya na zauna ya na latsa waya har ummy ta dawo ya ɗago ya kalleta ta haɗe fuska cike da ladabi ya ce “ina kwana Ummy antashi lfy”
Ta na zama ta ce”lfyqlau ya gajiya “ya ce “Alhamdulillah”
Ta ce”masha Allah”
Daga nan duk sukayi shiru a hankali ya ke satar kallon Ummy kamar bazatayi magana ba sai chan ta dubesa fuska ba wasa ta ce “Kai yanzu haka zakayi ta Zama Marzouq babu aure hakan da ka zaɓa ka na ganin shi zai fishsheka “?
Cike da ladabi ya ce “Kiyi haƙuri Ummy matan ne sam basa burgeni sannan har yanzu bansamu wacce nake ganin zan iya aura ba amma na baki zaɓi kamar yanda kika zaɓamun a baya a wannan karin ma ni mai yimiki biyayya ne”
Ta katse sa da cewa “Har Abada Na gama maka zaɓin mata Marzouq ina fatan Allah ya haɗaka da zaɓin ka ba zaɓi na ba Allah ya maka Albarka ya azurtaka da mata tagari tare da zuriya mai Albarka”
Ya amsa da Ameen tare da cewa “Banji Motsin Auta ba”
Ta ce “ba ta jima da fita ba wai zata biya school ta yi C a kafin ta wuce dubiya Asibiti”
Ya ce “Allah dawo da ita lafiya Ummy ni zan wuce Majalissa”
Ta miƙe tare da cewa “Allah ya bada sa’a ya baka Halal mai Albarka ya haneka da cin Haram”
Ya amsa da” Amen Ummy na”
sukayi sallama ya na fitowa cikin sauri security suka nufa tsadaddiyar motar sa ƙirar Marcedes-Maybach Exelero da ta haura 1B wanda shine mutum na farko da ya mallaka motar daga shigowarta a Ƙasa Nigeria,
suna buɗe masa tare da gaishe sa cike da girmamawa ya amsa a Kame ya na shiga baya aka rufe masa driver ya shiga ya ja motar inda ta gaba Security ne haka ta baya ma suka tada motar suka bar wajen Ya ciro jarida ya na fara karantawa har yanzu Yarinyar Faɗo masa ta ke a rai tabbas Abar tausayawa ce lokaci guda ya ji ya kwaɗaitu da son sanin Labarin halin da ya jefata a wannan ciwon mai hatsari”?
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*11*
Daga majalisa Kai tsaye gidan Marayunsa ya nufa sosai na yi mamakin yanda yaran duk suka rungumeshi suna murna da ɗokin ganinsa,
Yaran ya dinga ɗauka ya na musu dariya tare da musu wasa bantaɓa tunanin ya iya dariya har haka ba sosai ya ke nishaɗi da annashuwa cikin yaran bai bar Wajen ba sai gab da Magrib ya tsaya Masallacin Ƙofar gidansu ya gabatar da Salla kafin ya nufa ciki kamar yanda ya saba sai ya fara zuwa sashen ummy ya yi sallama da su kafin ya wuce na sa sashen,
Ummy ya samu ita da Lenah da Saudat tare da Matar Sadeq Zenat ,suna ta hira tamkar suna hira da mahaifiyarsu ba suruka ba,
Duk suka gaishe sa cikin girmamawa kafin ya zauna su gaisa da ummy ta tambayesa ya al’amuran ya amsa mata da “Alhamdulillah “ya na kallon Lenah bayan ya amsa gaisuwarta ya ce “me ya sameki na ga kinyi shiru”
Ta na narke fuska a shagwaɓe ta ce “Yaya Ka tuna jiya nace maka zanje asibiti Dubiya”
Ya ce “uhm”
Ta ce “to Wacce na je dubawarce ta bani Tausayi gaba ɗaya jikina duk ya yi sanyi wai yaya ciwon zuciya ne da ita Kuma kar kaga gatanta ko me ya haddasa mata ciwon Zuwa na ta farka amma ba ta iya ko magana saidai ta bi mutane da ido karka ganta yaya Kyakyawa kamar ita ta yi kyanta ni tunda nake ma wlh ban taɓa ga kyakyawa kamarta ba ga da ga zani zatayi kyan hali ni wlh gaba ɗaya ta shiga raina lokaci guda “
Shiru ya yi ya na Nazarin maganganun na ta Kamar bazaiyi Magana ba Sai kuma ya ce “Allah ya bata Lfy”
Ta ce “Amen yaya gobe ma zanje na ƙara dubata”
Ya ce “Allah Kaimu take care “
Ta ce “insha Allah “
Yayiwa Ummy sallama ya na barin Palon su Saudat suka saki jiki suna cigaba da hira Lena na kallon Saudat ta ce “Wai Aunty Saudat me ya haɗaki da Yaya Ashraf yanzu kuma Na ga Sai Fushi ya ke fuskarsa ba fara’a “
Ummy ta ce”Ina ruwanki uwar son gulma Umara ce zamu tafi tare shiyasa ta dawo muke shiri”
Lena ta miƙe ta na nufar sama domin ita a chan take ita ummy ta ce ciwon ƙafa gwara ƙasa ta ce “Tab ni za a mayar yarinya wlh faɗa sukayi kuma zan zuga Ashraf idan ba ta koma ɗakinta ba da kaina zan samo masa budurwa”
Saudat ta miƙe a fusace zata Bugeta ta ruga da gudu ta na sama ta na dariya tasan ta taɓo ta don saudat ba dai masifar kishi ba Ta koma ta na huci kamar zata sa kuka ta ce”Allah Ummy autar nan taki Zaneta zanyi ta rainani”
Ummy tayi murmushi ta ce “kunfi Kusa”
Zenat ma na murmushi ta ce “ai gaskiya ta faɗa “
Ta harareta ta na tura baki gaba Ummy ta ce”Ummy ta ce “kinga Maida wuƙar Ai babu Kishiyarku a gidannan insha Allah”
Da sauri saudat ta saki murmushi duk suka sanya Mata Dariya Ummy ta ce “Allahshiryaki”ta rufe fuska ta na dariya a haka Sadeq ya zo ya samesu Bayan ya zauna an taɓa hirar kaɗan dashi don shi mutum ne marar son magana Ba kamar Ashraf ba Kafin matarsa Ta bisa su wuce part ɗinsu bayan sun kira yaran da suke ɗayan palo suna Wasa tare da yaran Ashraf suka wuce ,
*IBTIHAL*
A ranar Ibtihal ta farka saidai ta kasa magana da motsi sai zuwa washegari cikin ikon Allah ta fara maganar saidai ba sosai ba Kamar bata son Magana,
Dukda haka ƴan uwanta sunji matuƙar daɗin ganin haka,
Duk wannan jinyar da take Maman Yusuf ba ta zo ta duba ta ba amma haka tacewa Abba kullum sai ta yi girki ta zo ta duba yanda take jajinta mata batun ciwon da yanda ta damu zata ɗauka har zuciya,
Yinin Ranar Yusuf A ɗakin ya kusan yini wanda baisan a ran Ibtihal ƙara mata Jin haushinsa Yake,
Daƙyal da taimakon Aunty Aisha ta Daure ta kamata har ta iya takawa ta zo alwala ta gabatar da sallolin da ke kanta a zaune domin tunda ta farka aka sanar mata kwananta nawa kwance su ne a ranta,
Lokacin ana Gama La’asr ne ta na sallar lokacin Yusuf ya zuba mata idanu ya na kallonta Aunty Aisha na gefe na haɗa mata fruit salad su kuma sauran ma su jinyar suna waje har momy da hajja da su Aunty Salma Da sauransu,
Safa ce ta shigo tare da Lena Da ke sanye cikin tsadaddiyar Abaya Har ƙasa ta duƙa ta na gaishe da aunty Aisha da ta amsa mata fuska sake tare da tambayarta Ƴan gida ta ce “Duk suna lafiya ya me jiki”
Ta ce “jiki Alhamdulillah gashinan ma Ta na ta salla amma ta kusa gamawa ku zauna”
Suka Zauna,
Lokacin ne Afren ta buɗo ƙofar ta shigo Gadon ta nufa ta ga ba kowa sai ta Koma waige,Safa ta yi mata Dariya ta ce “Auntyn ta Ɓata”
Lokaci guda ta sanya kuka ta na Tirjewa Ƙasa Safa na shirin kamota Lena ta Taso ta ta na Ɗaukarta cike da sigar lallashi ta ce “sorry My Angel Wasa ta ke maki Your aunty She is with you”
Ta na kallonta cikin idanu ta ce “Where is she?
Ta nuna mata inda ta ke zaune ta salamce sallar ta haɗe kai da gwuiwa”
Da sauri ta dire jikinta ta na rugawa ta rungumota ta baya tare da cewa”Aunty mun ɓata da Aunty Safa”
Safa ta sanya Dariya ta ce”Sorry gimbiyata baki san wasa ba”
Ta juyo tare da tura mata baki kafin cikin hausanta ta koyo ta ce”Ba ni ba ke Kawarki ce My friend now”
Suka sanya dariya Aunty Aisha ta ce”Ja’ira yanzu kin iya Hausan Ashe”
Ta ƙyalesu ta na juyawa wajen ibtihal tare da ɗago fuskarta da ta sadda ta na waro idanu ta ce “Aunty What made you cry? What hurts you”?
Ta faɗa a jere “
Safa ta ce “Kuka kuma”
Sai ta taso tare da matsowa gurin har lokacin hawaye ta ke Safa ta ce”Haba Sis meya faru kuma kina Cikin halin ciwon da ba ason kina saka Damuwa a rai don Allah meyasa bazaki cire abunda ya ke ranki ba nasan duk Halin nan da kike ciki bazai wuce akan tsinannen chan Sharef ba So kike ki kashe kanki Ibtihal kiyi mana asararki,Mom ɗinki na sonki,Dad ɗinki ma Ƙaddara ta rabaku kuma insha Allah sai kun dawo kamar da ,Sannan mu ƴan uwanki na sonki,Ƴarki na sonki”duka familynki na ƙaunarki meyasa akan Mutum ɗaya zaki halaka kanki me ya sa sis?Ko dai son Mutumin nan kike………✍🏽
*ZAMU KAMMALA FREE PAGES NA WANNAN LITTAFIN A PAGE 15 KUNA DA DAMAR FARA BIYAN KUƊINSA TUN YANZU 500 TA WANNAN ASUSUN BANKIN 7026166536 OPAY HAJARA ABUBAKAR LAWAL TARE DA SHAIDAR BIYA TA 07026166536*
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
🪅*IBTIHAL*🪅
~MALLAKAR~
*HAJARA L SADEQ*
(miss Hajo)
MARUBUCIYAR👇🏼
Auren wata tara
Ni da yaya arman
Matar uncle
Najmat abiy
Komai mukaddari ne
Khadijatul Sabren
Ribar so
Mata ta ce
*And now*
*IBTIHAL*
*SHAFIN NAN NAKI NE ASIYA SANI FATAN ALKHAIRI GAREKI SIS TARE DA FATAN MIJI NA GARI*🥰🥰🥰
*DEDICATED TO MY HUSBAND*
🅿️…………………………..*12*
Lokaci guda ta ɗago cikin hawaue ta girgiza mata kai sai kuma kawai ta rungumeta ta sanya kuka mai sauti ta kasa magana,
Itama safa hawaye ta ji sun zubo mata,
Itama Afren sai ta hau kuka,
Aunty Aisha Da ta zuba musu ido kawai ta girgiza kai ,
Yusuf ma idanu ya zuba musu cikin faɗa ya ce “Ohh nagano Watau har yanzu Asararren tsinannan chan ne a ranki shiyasa kika kasa amincemum shekara da shekaru amma wlh da kin cika marar zuciya ke da ba ma zan yarda halittar ɗan adam ce ke ba Saidai Dabba Zatayi wannan Rashin Zuciyar Haba Shiyasa Daga Maganar Aurenmu kinbi kin tada Hankalinki to wlh ko mutuwa zakiyi sai an Auramun Gawarki daga baya na binne ki ba ciwon zuciya ba “
A mugun Fusace Aunty Aisha ta ce”Kai wani irin shashasha ne wai yusuf don uwarka to ƙarya kake ba sonta kake ba Da Allah Wuce ka ba mutane guri kuma karna ƙaraga Ƙafarka a asibitin nan daga yau ficemun da Allah”
Ta faɗa a mugun fusace”
Ya fice ya na Huci don yasan ko giyar wake ya sha bai isa tanka mata ba don Abba sai ya kusa tsine