KAMAR DA WASA HAUSA NOVELS COMPLETE PDF.doc

Author :  Nil Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   12 / 36

33K to 36K   out of 106.8K words

ji shiyasa babu bata lokaci yazuba yafara ci saida yakoshi sannan yashiga wanka agurguje domin yaga kamar yakusa makara, kayan ball dinsa yasaka dark blue yadauki combos dinshi a hannu yafita, sallama sukayi dasu Hindu dan yasan dakyar idan zai dawo yasamesu, sai bayan da yatafi sannan bilkisu ta dauko jakar kudinta tabawa su meenah su kirga mata tanata basu labarin abubuwan da suka kasance lokacin da tana gidansu fahad gaskiya abin ya kayatar dasu bama ita kadaiba dan abinda suka lissafa kudin da aka tara mata dubu talatin da bakwai da dari biyar har dari biyar din da ta baiwa su mariya dazu dubu talatin da takwas kenan, dubu biyar biyar tabasu harda na maama tace itama akai mata.

Daf da lokacin sallar magrib suka tafi ji tayi kamar ta rikesu ta hanasu tafiya amma babu damar hakan domin mijin meenah ne yazo daukarsu zasu bi su ajiye Hindu, ciki takoma tarasa me zatayi saboda babu wani sauran aikin da yarage ma agidan domin su Hindu sunyi mata komai kafin su tafi sai dai dan girkin dare da zata yiwa fahad wannan kuwa indomie ma zata dafa masa, dadinta ma daya da wuta shine tasamu damar fara kallon sabon series din da Bollywood ke nunawa mai suna zahba walam ya'ood, tana tsaka da kallon fahad yadawo, wanka yafara wucewa yayi sannan yazo yayi sallar magrib daga nan bai kuma fitaba sai salim da yayi masa waya wai zaizo yagaida anty amarya kafin ishah kuwa sai gashi shiyasa tare ta dafa musu indomie din da dafaffen kwai,kan dining takai musu lokacin suna kallon ball atashar sport +,daki tawuce da yar guntuwar tata indomie din acikin flate taje ta zauna taci koda tagama ma anan tayi zamanta ta bude laptop dinta tashiga YouTube domin yin kallo, sai wurin 9 sannan salim yatafi, duk da haka bata koma falon ba taci gaba da zamanta adaki daga karshe tayi shirin bacci ta kwanta bata san lokacin da fahad yazo yayi nasa shirinba dan yau bai kunna fitila ba.

Haka suka cigaba da zama idan zai shigo daki wai dole sai yayi knocking tabashi izini shima idan yana ciki idan zata shigo sai tayi knocking yabata izini ahaka har sukayi 2 weeks kuma lokacin ne zata fara fita aiki duk da cewa acikin sati biyun nan rana daidai ce da baza suyi baki ba su ayiyah ma itada mamuh sunzo sunga daki sunyi fatan alkhairi, ranar friday maama tazo dama ranar bilkisu bata fitaba amma shi fahad yana shagonsu yan shagon nasu su tj sun hura masa wutar wai dole sai yau sunje gidanshi sunci girkin amarya, daga karshe dai text massage yayi mata yace,

_Princess dan Allah ki taimaka kiyi girkin mutum biyar wallahi yan shagonmu sun dameni wai sai sunzo.... Pls hajjaju._

Lokacin da taga sakon bata yimasa reply ba amma tafadawa maama abinda yaturo ai kuwa maama tazage ta tayata suka shirya shiryayyen girki duk da cewa unguwar ba asaida abubuwa amma saida bilkisu tafita da kanta ta samo almajiri ta aikeshi can bakin titi yaje ya iyo mata siyayyar duk abinda takeso bayan yakawo mata tace anjima can yazo yakarbi abinci,

Bayan sun gama girkin wanka tashiga tayi tasha doguwar riga ta atamfa ta danyi kwalliya sama sama, tana kitchen tana zuba musu abincin itada maama wacce ke daki tana salla suka shigo, fuskarta asake ta karbesu ta kalli fahad dake wani jin kansa asama shi ga mai gida murmushi tayi,

"Sannu da zuwa, table is ready"

"Thank you sweet heart"

Basu hau dinning dinba domin yayi musu kadan sai anan tsakiyar falon suka baje ba karamin dadi fahad yajiba domin girkine na fita kunya su bilkisu sukayi shi white rice and vegetables stew ga hadadden salad yasha dafaffen kwai abin dai ba acewa komai sannan ga drinks agefe mai dan Karen sanyi kowa saida abin ya burgeshi, tafiya tayi wurin maama tabasu wuri bayan sun gama ya leko cikin dakin suka gaisa da maama yakara gaba bashi yadawo ba sai magriba saboda yau babu zuwa filin ball ita tarasa me yake ji a ball dinnan da kullum sai yaje ranar juma'a ne kawai baya zuwa. Ranar litinin tafara fita aiki sai dai wannan karon karfe uku take tashi sabanin da, zamansu da fahad normal babu wata matsala tayanda take so yake bida ita kullum kuma afalo yake kwana aikin gida kuwa wannan almajirin data samu shine yake yimata shara da mopping idan da aike ta bashi amma fa har yau fahad bai san dashi ba saboda lokacin da almajirin zaizo baya nan wani lokacin kuma kafin yatashi daga bacci dasafe zaizo yayi aikinsa yatafi amma banda falon sai tace wannan yabarshi zatayi yau dai da Allah yayi za ahadu fahad na gidan baije ko inaba dama weekend ne yana da dinkuna ashago amma baya jin zai fita yanzu sai yamma yana kwance afalo daga shi sai three quarter iya gwiwa da riga armless yana kallo sai yaji anbude gida anshigo harda sallama tashi yayi yafita jin muryar namiji yana fita yaga saurayi zaiyishi atsaye hakama ahaife kilama yafishi ahaifen,

"Lafiya? Ya akayi?"

"Ehh nazo aikine.. Nine meyiwa hajiya aiki"

"Aiki? Aikin me?"

"Shara nake yimata da iyo cefane"

"To daga yau karka kara zuwa na sallameka, karka yarda ka kara dawowa"

Saida yaga tafiyar almajirin sannan yarufe gidan yasa sakata yashiga ciki, yau kam babu maganar neman izini kawai yafada mata daki tana kan gado da bra ajikinta da skirt tana kwalliya da alama daga wanka tafito,

"Menene ma'anar wannan abun da kikayi maigado? Ya zaki kawo min almajiri gidana batare da sanina ba..."

Tuni ta dauki hijabinta tasaka tana kallonshi,

"Almajirin ne wani abu? Yaron da na girmeshi"

"Ke kike ganinshi yaro amma ni awurina ba yaro bane, ya zaki dauko wanda ko atsaye yana daidai dani, ai sai akasa banbance dani dashi wanene mai gidan, wannan ma ai tsaf zaiyi min duka"

"To yanzu me kakeso ayi wai?"

"Ai narigada na sallameshi..."

Har yajuya zai tafi tariko rigarshi,

"Da ka koreshi din to yanzu wa zan rinka aika?"

"Ni ki aikeni mana, ai gara ni kisani aikin kuma kiyita aikena da ki kawo min wancan gardin ki ajiye min agida wanda ko adake tsaf zaiyi min duka yanda nake dan kadan dinnan dani..."

Sakinshi tayi yafita yanata yi da bakinshi wanda kusan rabi kishine acikin maganganun nashi. Aranar da yamma suka shirya sukaje gidan Anty Fauziyya suka gaisheta acan sukayi sallar magrib sannan suka dawo gida da zummar gobe ma zasu jewa yaya asabe da su anty kubra. Yau da zaiyi wanka da daddare rasa kayan baccin da zai saka yayi saboda shi baya maimaita kaya idan yasaka guda daya sai anwanke yake sakawa gashi tunda yazo gidan sakawa kawai yake yana tarawa ba awankewa dama ayiyah ce keyi masa wankin inner wears dinshi manyan kayan kuma wanki yake kaiwa to yanzu babu ayiyah, tsayawa yayi agaban drewar din bayan yarike kugunshi da hannunshi guda daya......


*Dan Allah idan har kin san baki siyaba to karki karanta.*



*_Ummi Shatu_*


? *HASKE WRITERS ASSO.*


*KAMAR DA WASA...!*


_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*22*


***Shagwabe fuska yayi ya juya ya kalli bilkisu wacce ke sanye da hijab ajikinta amma aciki sleeping dress ne riga da wando iya gwiwa,hankalinta gaba daya yana kan system din da take dannawa,

"Wai yau wanne kayan zan saka...?"

Dagowa tayi ta kalleshi sannan ta maida kanta kan laptop dinta,

"Da nice nake fada maka wanda zaka saka?"

Shiru yayi mata zuwa can yayi kwafa,

"To wallahi yau karki fito bayan na kwanta dan babu mamaki tsirara zan kwana..."

Tabe baki tayi,

"Kayi duk yadda kaso..."

Jallabiya ya dauka daga cikin kayansa yanufi bathroom yanata kukkumburo baki,

"Wai haka kawai mutum yanada mata amma komai shi zai yiwa kansa..."

"Magana kake yine?"

Yaji tafada yana kokarin shiga toilet din,

"Ni ba dake nake ba"

Tana nan zaune tana aikinta yafito sanye da jallabiya kalar ruwan kasa har lokacin bai daina kumbura ba, kayan shimfidarshi ya diba ya fita zuwa falo bai sake komawa cikin dakin ba sai asubah daga nan bacci yakoma bayan yayi sallar asubah bai tashiba sai karfe 9, wanka yayi yasa three quarter da t shirt ya tattaro kayan baccinshi da kananan kayanshi yakai tsakar gida, duk sai wani cika yake yana batsewa tana ankare dashi, yajima tsaye kan kayan yana kallonsu kafin yaje ya dauko bucket da sabulun wanki yazo gaban fanfo ya debi ruwa yafara wanke kayan yanayi yana yarfe hannu kamar wanda ake yankar naman hannunshi,

"Hajjaju yanzu idan wani yazo ya iskeni ina wanki bazaki ji kunya ba?"

Karasa ajiye kayan wanke wankenta tayi tana kallonshi,

"Au wai kai da nufinka ni zanyi maka wankin?"

Langabe kai yayi yasake bata fuska,

"To ai mata masu neman aljanna har wanki suke yiwa mazajensu"

Dariya ita abun yabata ma amma ta dake ta wucewarta daki, dakyar ya samu ya wanke kayan Amma fa ji yake kamar yayi wani gagarumin aiki gashi ko breakfast baiyi ba, falo yaje ya fada saman doguwar kujera yanata ajjiye numfashi. Saida yahuta sosai sannan yatashi ya yi breakfast lokacin karfe goma da kusan rabi, yana gamawa yasake kwanciya, wurin 12 na rana yakwaso kayan mashi yazauna domin gogesu, yana yi yana jin wakar breaker awayarshi,

"Gaskiya ni ba dan gata bane..., inyi wanki da kaina kuma gugar ma arasa mai taimako na..."

Tana jinsa bata tanka masa ba zuwa can yafara bin wakar,

"Idan zaki kije dani.... Idan nai fushi ki rarrasheni....!"

Nan dinma dai bata tanka ba har yayi yagama, ganin rana tayi express girki tayi musu bayan yaci abincin rana ya tattaro kayan sawarshi masu datti yace itama ta tattaro nata wanki zai kai musu, bayan yatafi itama ta wanke nata inner wears din masu datti, rasa inda zata shanya kayan tayi domin bata son fahad yagani shiyasa ko pant ta wanke boyeshi take inda bazai ganiba wani lokacin ma sai yafita take shanyawa kafin yadawo yabushe ta dauke kayanta amma bata taba wanke bra ba sai yau, babu yanda ta iya dole akan igiyar da ya daura ta baya ta shanya kayan. Kafin yadawo tayi wanka tashirya tana jiran yazo su tafi ziyarar da yace zasuje gidan yaya asabe da su anty kubra domin itama tana son fitar bata son zaman kadaicin nan musamman ma idan baya nan. Bai jima awurin kai wankin ba yadawo,wanka kawai shima yayi yasaka wani yadi mai laushi kalar ruwan toka amma bai saka hulaba yasha turare suka fita, drop din napep suka dauka yakaisu duk inda zasu je dama anty Kubra da anty juwairiyya makota ne domin katangarsu ma daya anty asabe ce dai awata unguwa ta daban, daga karshe gidansu yakaita wurinsu ayiyah ai kuwa ranar taga soyayya domin ayiyah kamar zata goyata dan kauna. Fita yayi yabarta tareda su ayiya yatafi majalissar su ta shan shayi wadda ke kusa da filin kwallonsu dama sunyi waya da salim yasanar dashi yana can.

Acan gida kuwa itama bilkisu tasake da su ayiyah sosai duk aikin da taga zasuyi sai ta karbe tayishi ahaka harsu Mariya suka dawo daga islamiyya suka sameta,Rungumeta sukayi suna tsalle dan tsananin murnar ganinta, itama murnar takeyi domin tana kaunar yaran duk da ba yan biyu bane amma kamarsu daya sannan a shekaru ma tsiran babu yawa, tana nan tareda su sunata bata labarin makarantarsu sai zuba mata surutu suke yi ita kuma tana cin tuwon da mamuh ta zubo mata tuwon biski miyar taushe wacce taji tantakwashi da man shanu ai kuwa taji dadin tuwon nan domin tazage ta ci babu fulako, tana daf da gama cin tuwon fahad yashigo ai su mariya na jin maganarshi atsakar gida kowacce takama bakinta, dariya abin yabawa bilkisu saboda daga jin motsinshi yara har sun daina kwarafniya,

"Meyasa kuka daina yimin hirar ne mariya?"

"Anty ya fahad ya hanamu surutu, duka yake yi sosai yafi ya Abba duka..." Inji Maryam,

"Ga dukanshi zafi..."

Dariya tayi saboda jin abinda mariya tace itama, sake nutsuwa sukayi lokacin da yashigo cikin falon, nan suka fara rige rigen gaisheshi,

"Mariya karbo min abinci awurin ayiyah..."

Tun kafin yarufe bakinshi ta tashi tafita, kallon Maryam yayi ya harareta,

"Ke kuma ina dan kwalinki? Bana hanaku zama babu dan kwali ba?"

Itama tashi tayi dasauri tashige daki domin dauko dan kwalin, sai lokacin ya maida kallonshi kan bilkisu,

"Nikuma akan me za ayi min nawa fadan?"

Dariya yayi ya zauna kusa da ita yana lumshe idanuwa sakamakon kamshinta da ya shaka wato matar nan karshe ce awurin kamshi yarasa wanne turare take shafawa take wannan kamshin shiyasa wani lokacin har kishin fitarta wurin aiki yake saboda baya son wani yaji kamshin nan sai shi kadai,

"Ni na isa hajjaju? Ai ke bakya laifi"

Dan murmushi kawai tayi batace komai ba har maryam ta kawo masa tuwon shima yafara ci ita kuma bilkisu ta dauke kwanikan da tagama ci zata fitar dashi,

"Ke mariya ita zata fitar da kwanikan...?"

Dasauri suka karbeta tana cewa ma subarshi amma suka ki, hannunta taje ta wanke sannan ta dawo tazauna,

"Gaskiya kana takurawa yaran nan"

"Basa jin magana ne..."

"Wallahi bawani rashin ji da sukeyi"

"Bazanyi musu dake ba"

Saida shima yagama cin tuwon sannan suka yiwa su ayiyah sallama suka tafi lokacin har baba yadawo daga kasuwa, yanzun ma kamar dazu a keke napep suka koma gida sun ko yi sa,a akwai wuta dayake side din ana samun wuta sosai, bedroom tawuce shi kuwa afalo yaja birki yacire rigar jikinshi yabar dogon wandonshi da singileti fara yana kallon kwallo, ita kam wanka tayi ta dauki laptop dinta tana kallo daga ita sai towel duk da yanzu tana dan taka tsantsan amma takasa sabawa da zama cikin hijab domin ita agida babu mai shigar mata daki shiyasa take cin karenta babu babbaka dan sai ta kwana da towel ko under wear dama da daddare daga pant har bra babu ruwanta dasu sai idan tana period ne take kwana da pant, bata san kirinkin da yakai fahad baya ba sai ganinshi tayi yafado mata daki dauke da braziers dinta data wanke dazu,

"Ji mana malam, wai meye hakane? Dan Allah karinka knocking before ka shigo"

"Yi hakuri, mantawa nayi"

Tana gyara hijab din datake kokarin sakawa tace,

"Waya saka dauko min shaya?"

Wartar kayan tayi cikeda jin haushi, shi kam yana dariya yawuce drewar domin itace bata saniba amma yafi minti biyar yana kallon braziers din duk saida yayi musu kallon kurulla sannan yakawo mata.

Kayan baccinshi ya dauka yawuce toilet har lokacin harararshi takeyi, sai da taga shigarshi sannan ta tashi taje ta boye kayan acan drewar dinta,dawowa tayi ta zauna taci gaba da aikinta har yafito daga wankan sanye da gajeren wando da riga armless duk farare sol masu santsi, kallonta yatsaya yi yana shafar keya,

"Hajjaju nace yau dinma a falon zan kwana...?"

"A'a akaina zaka kwana..." Tayi masa gatse dama bata gama hucewa daga fushin dauko mata braziers dinta da yayiba, dan tabe baki yayi yai gaba yana kunkuni,

"Da za ayi hakan aini so zanyi..."

Kayan shimfidarshi ya dauka yakara gaba domin yau bacci yake ji, tsabar takaici ko wutar yau bai kashe mata ba yaje yayi kwanciyarsa, itama bata kara bi ta kansa ba saida ta kammala aikinta sannan tafito zataje kitchen lokacin misalin karfe 12 saura nadare, awani baje ta ganshi ya harde hannuwa yadora kafa daya kan daya, murmushi tayi tace aranta,

"Lallai kuwa Prince... Irin wannan zuba mulki haka, baccin ma sai anyi masa sarauta"

Fridge tawuce ta dauko ruwa mai sanyi sannan tadawo takashe masa wutar falon tashige daki abinta. Da safe tanata kici kicin hada abin karyawa saboda tana so tafita office dawuri shi kuwa yanata baccinsa saman katifarsa domin tunda sukayi sallar asubah yasake komawa bacci, har tagama hada breakfast tayi wanka bai tashiba, bayan tagama shiryawa ne tazo tana karyawa yatashi, daga kwancen da yake ya daga ido yana kallonta, leshi ne ajikinta c green colour dinkin riga da skirt, batayi wata doguwar kwalliya ba amma fa akwai kamshi kamar anyi barin turare maida idonsa yayi ya lumshe yana turo baki shi bawai aikin da take fitane damuwarsa ba, damuwarshi shine yanzu duk namijin da ta gifta ta kusa dashi shima dole sai yaji irin wannan kamshin da yake jin tanayi? Kai impossible,

"Allah bazai yuyuba..." Yafada afili tare da tashi zaune,

"Hajjaju har kin shirya ne? Ina kwana?"

Daga kan dining tajuyo ta kalleshi,

"Lafiya lau"

Murmushi yayi domin dama yasan gaisuwar bata wuce haka,

Bathroom yayi sauri yaje yayi brush yadawo ya isketa saman dining din amman takusa kammalawa, kujera yaja ya zauna wacce ke kallon tata,lumshe ido yayi,

"Hajjaju wannan kamshin fa.... Gaskiya...... Hmmm.....gaskiya"

Mikewa tayi tawuce abinta tana cewa,

"Kaga ni malam sauri nake aiki ne dani da sanyin safiyar nan"

"Adawo lafiya, Allah yatsare min ke hajjaju na"

Murmushi kadai tayi tawuce daki ta nado laffaya dinta bayan ta saka safar kafa baka ta dauko komai da take bukata tazo tawuceshi tafita, duk sai yaji gidan kuma babu dadi da baiyi niyyar fitaba amma dole tasa yayi wanka yazo yashirya ganin bata nan da komanta yayi amfani har turare nata yafesa, tsayawa yayi yana kallon turaren,

"Arabian night...uhmm su hajjaju manya"

Duka saida yashafa daga body spray din har performed spray sannan yadauko kayansa yasaka yafita shago. Wurin karfe biyu saura yana shago yagama yiwa wasu yan mata dinki husna na zaune gaban kekenshi sai ga kiran bilkisu yashigo wayarshi, zuba masa ido husna tayi lokacin da yadauki wayar,

"Ranki yadade ya akayi?"

"Kaga dama cewa nayi zan biya ta gidanmu da daddare sai na taho"

"A'a hajjaju ki bari ranar juma'a ko cikin weekend sai kije"

"Shikenan..."

"Adawo lafiya"

Katse wayar tayi tana kwafa wato danma yasamu ta tambayeshi shine harda wani hanawa, bata je dinba ta koma gida ta dan huta sannan ta tada shirin dafa alala domin yau shi take kwadayi, shi kuwa fahad ba karamin fasuwa kansa yayiba bilkisu ta kirashi tana neman izini yanzu sake jin kansa yake yi amatsayin boss, bai lura da fushin da husna keyiba tunda ta fahimci matarsa ce ta kira. La'asar sakaliya yakoma gida bilkisu na falo tana bacci dan kwanciya tayi kuma bacci yayi gaba da ita riga ce ajikinta body hug da yar skirt marar nauyi amma tasa karamin hijab, bai tasheta ba yawuce yazubo abinci alala yagani yasha kwai da vegetables sai kamshi yake guda hudu yazubo yazauna yatashi dasu sannan yashiga wanka agurguje yafito yasa kayan ball dinsa lokacin bilkisu tatashi karar wayarta ne yatadata meenah ce ta kirata,

Kallonsa tayi daga sama har kasa,

"Kai da islamiyya ma kashiga wallahi tafi maka wannan zuwa filin kwallon"

Murmushi yayi yazauna yana saka safa da combos dinshi,

"Hajjaju kenan,

12 / 36