KAMAR DA WASA HAUSA NOVELS COMPLETE PDF.doc

Author :  Nil Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   27 / 36

78K to 81K   out of 106.8K words

ciki shiyasa yajishi yakoshi over, tashi yayi yafita bayan ya gama yakoma dakinsu, salim yaturawa text yana sanar dashi anjima zai rakashi su dubo Bilkisu, wanka yashiga domin yanzu ya danji karfin jikinsa.

Bayan sallar magrib suka tafi asibitin su uku saboda harda ya abba,dukkaninsu sunsha dogayen kaya, babu kowa adakin sai iya Bilkisu da meenah suna zaune kan gadon Bilkisu na shan tea har lokacin tana sanye da hijabinta, jin sallamarsu yasata sake kasa da kanta bata ko dagoba saboda bata son ganin sun hada ido da fahad saboda tasan yanzu bata da wata martaba a idonsa tunda ashe sadaka aka aura masa ita tasan ba kowane yakitsa wannan abunba sai iyallo saboda dama itace ke cewa zata aurar da ita sadaka, yanzu gashi anja mata reni da wulakanci a idon yaro,

Tana ji su Abba na tambayar yamai jiki suna yimata sannu dakyar ta iya amsawa sakamakon kukan da ke kokarin taho mata, lokacin da taji meenah na gaisawa itada fahad sai taji kamar da biyu yake yin gaisuwar nan ta shareshi bata ko dago ba daga karshe su Abba suka fita suna yimata fatan samun sauki haka itama meenah sai ta tashi tafita yarage su biyu kadai cikin dakin,

"Sannu... Yajikin? Ke daga fada miki gaskiya shine zaki kwanta ciwo...?"

Jin abinda yace yasata dagowa ta zuba masa harara saboda ta tsani ke dinnan kafin ta dauke idonta yarama,

"Ni ai ka kira da matar sadaka ko?"

"To da matar meye? Sadaka aka bani kuma nakarba..."

"Wallahi karya kake yi..."

Nuna kanshi yayi da yatsa,

"Ni kike cewa ina yimiki karya?"

"Ehh din...."

Kafin yayi magana meenah tashigo rikeda waya nan ta mikawa Bilkisu tana cemata,

"Adda labour gashi su elmustapha ne..."

Karba tayi suka fara gaisawa dasu elameen suna yimata ya jiki, bata saurari fahad ba wanda ahankali yace,

"Yarinya kuma sai kin biyani jinina da na baki dan ba kyauta nabayar ba..."

Shima bai sake bi ta kanta ba yayi waje abinshi yabarta da kunar zuciya domin maganganunshi sosai yanzu suke bata mata rai,wayar nan kawai tanayi ne bawai dan tana fuskantar abinda take cewa ba......


*_Ummi Shatu_*


*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



46****Daren ranar ma haka ta kwana batayi bacciba saboda tsabar bacin rai da damuwa da zarar ta tuno maganganun da ya yayyaba mata sai taji kwalla ta ciko idonta. Washe gari dasafe aka sallameta suka koma gida, suna zuwa tasamu tashiga wanka tafito domin shiryawa kamar tasaka hannu aka tayi ihu haka takeji idan har tatuno da maganganun fahad, ahaka ta daure tashirya tana cikeda damuwa tana gamawa Hindu takawo mata abin karyawa nan ta zauna tasoma dan kurbar ruwan zafi bawai dan tanaso ba amma sauran kayan karyawar ko tabasu batayi ba ahaka Hindu tadawo ta sameta tana rikeda sultan a hannunta,

"Adda mai gado yabaki ci abincin ba? Saifa kin dan daure..."

Jin abinda Hindu tace yasata dagowa ta kalleta da kodaddun idanuwanta wadanda ko kwalli babu,

"Hindu banida apatite abakina wallahi, sam bana jin dadin komai..."

"Duk da haka ki dan daure mana, sannan dan Allah ki gyara fuskarki kisaka koda powder ne da kwalli... Amma ya fahad yazo yaganki ahakan nan ai akwai matsala..."

Harara ta watsawa hindu sannan tamaida kallonta kan sultan wanda ke miko mata hannu yana yimata gwaranci, mika hannu tayi zata karbeshi amma Hindu taki sakinshi tana cewa,

"Kai bari kar kaje ka karasa mana addarmu kaga dazun nan tadawo daga gadon asibiti..."

Murmushi Bilkisu tayi ta karbeshi sakamakon kukan da yafara yi, ita kuma haka Allah ya dorawa yaran kannenta kaunarta duk sun shaku dasu babu wanda yake yimata kiywa,

"Dan Allah adda labour ki daure kici abincin nan kar yayi sanyi sannan ki gyara fuskarki saboda tsaro..."

"Ke hindu idanma fa akan fahad kiketa wannan damun nawa bazan yiba..."

"A'a wallahi Adda labour ni basaboda shi bane kawai dai ai kinga idan kika saka kwallin fuskarki zatafi fitowa amma yanzu Allah baki ganki ba duk kin canja kin sake fadawa..."

Bata sake yin magana ba ta jawo abincin gabanta ta bude tafara ci tanayi tana bawa sultan, saida tagama tsaf ta zauna gaban mirror tana shafa powder sai tajiyo sallamar khulsum, tana jiyosu sunayi itada hindu atsakar gida hindu nacewa bazasu amshi uzurinta ba tunda bataje asibiti ba saida suka dawo gida. Anan gaban mirrior din khulsum tashigo ta sameta tana zizira kwalli,

"Labour patient har an warke anfara coda ado za atari oga?"

Harararta Bilkisu tayi ta taso daga gaban mirror din tadawo gefen gado kusa da khulsum,

"Zaki fara ko? Allah yakawo ki ai kuma..."

"Ah to ai gaskiya ce anwarke mana me kuma yayi saura banda akoma bakin daga..."

"Sai kiyi kuma..."

"Yawwa wai ke yaushe zaki tare ne? Allah kinga labour ki tare tun kafin abinnan ya bayyana dan wallahi ni harga Allah ban yarda da wannan ciwo ciwon nakiba.... Laulayi kika fara ko?"

"Wai ke meyasa ba a abun arziki dake ne? Ni dan Allah kinga karki bata min rai..."

"To yi hakuri, sorry kinga jiya banzo asibiti na dubaki ba ko? Wallahi khalifa ne nima baida lafiya... Amma yaji sauki yau"

"Babu komai ai da kinyi zamanki ma kin kula dashi"

"Ai yaji sauki yana can tare da babanshi"

"Allah yakara masa lafiya..."

"Amin... Yawwa wai mutuniyar kin kuwa taba gwada hadin nan dana turo miki rannan?"

Dariya Bilkisu tayi saboda ita wallahi ma sai yanzu tatuna da sakon da khulsum din ta turo mata,

"Madam kedai kije kiyi tayi amma ni wallahi bazan yiba..."

Kallonta khulsum tayi cikin jin haushi,

"Allah yashiryeki labour maza dai ki tsaya kallon ruwa kwado yayi miki kafa wallahi idan baki kama mijinki a hannunba... Hmmm zaki ganene"

"Toh Anty..."

Dariya khulsum tayi sannan tayi kasa da murya tace,

"Wai dan Allah laulayinne da gaske?"

"Ban saniba..."

Kafin khulsum tasake magana suka jiyo sallamar fahad atsakar gida amma ahankali kamar wani marar gaskiya, mikewa khulsum tayi tana cewa,

"Bari na kwashi yanmatan kafafuwana inbarku kusha morning show dinku, ga wata gumba idan kinaso sharp sharp ce wallahi...."

"Banaso akai gaba..."

"Kedai kika sani wallahi, ni sai anjima"

Mikewa tayi ta kwanta bayan fitar khulsum tana jiyo lokacin da khulsum din suke gaisawa da fahad atsakar gida mintuna kadan tsakani taji shigowarsa ta hanyar bude kofa da yayi bata ko motsa ba ayadda take bare ta dago ta kalleshi, daga dan nesa yatsaya yana kallonta, riga da skirt na leshi tasaka wanda aka yiwa simple style yayi dass ajikinta, dakin gaba dayanshi sanyayyen kamshine ke tashi cikinsa,

"Yajiki......?" Yafada yana murmushin da bazata ganeba,

"Da sauki" ta amsa kamar bataso domin badan shi din mai jin magana ce komai kankantarta ba da bazai jiba,

"Dama nazo dubaki ne, hope kinji dadin jinina dake jikinki?"

Juyowa tayi afusace ta harareshi,

"Dadinta ma dai banice nanemi da kabani jinin ba, badanma lokacin da aka saka min bana cikin hayyacina ba da me zanyi da jininka.... Wa yasani ma ko guntun sikila ne..."

Murmushi yayi yana kallonta yasan dai maganar dayace wannan matar sadakar da yakirata dashi ne yaketa sosa mata zuciya har take neman hanyar mayar masa da martani,

"Kiyi hakuri bani na kar zomon ba rataya aka bani, kuma ratayar ma ban karba ba......"

"Idanma ka karba idanma baka karba ba ruwanka, sannan da kake cewa sadaka aka aura maka ni ai yanzu ma kanada damar da zakace kafasa... Tunda ba adole"

"Akan me zance nafasa? Ai narigada na karba"

"Duk da ka karba ai kasan hanya mafi sauki wacce tadace da zakabi ka mayar da sadakar...."

Tabe baki yayi yasamu kan bedside drewar yazauna yadora kafa daya akan daya,

"Ni yanzu ba wannan ne yakawo ni ba inada abin yi dubiyace ta kawo ni..."

Wani kallo tayi masa yana sanye da kananan kaya amma yadora lab coat asama kafarshi rufe cikin bakar safa, takula akwai shi da saka safa akafa sai kace wani marar lafiya,

"Yanda kake da abinyi haka nima nake dashi, nidai kawai ka datse igiyar auren nan kowa ya huta..."

"Ban ganeba.... Wai kina nufin ni fahad na sakeki? Idan hakan kikeso zan yimiki amma abisa sharadi guda daya..."

Mikewa yayi daga kan bedside drewar yaje yatsaya mata aka dukkan hannahensa yasaka su cikin aljihu,

"Kifara sanar dasu Abba irin zaman da mukayi dake dafarko da irin gangancin da kika sakani nayi harna sakeki lokacin da wannan shedanin tsohon dan duniyar yake tsaka da hure miki kunne, sannan sai kisake fada musu abinda ke faruwa ayanzu idan har kikayi haka to wallahi zan yimiki yadda kike so...."

Sosai kalamansa suka bata haushi ta lura yanzu baida magana saita hamood magana daya sai ya jefo hamood aciki, takasa gane tsakanin shi da hamood waye yafi wani tsanar dan uwansa saboda shima hamood din lokacin da tana gidansa baida magana sai ta ya kira fahad da karamin yaron nan marar kunya, shi kuma fahad yanzu magana kadan zaice tsohon dan duniya,tana can duniyar tunani har fahad yawuce yabar mata dakin yayi tafiyarshi kawai sai bude ido tayi taga baya nan,

Tagumi ta rafka tana tunani, ai ko giyar wake takesha bazata taba gigin aikata wannan abun da fahad yafada ba, ai idan ta kuskura abba yaji cewar itace ta kashe aurenta karo nafarko dan ta auri hamood wallahi kashinta yabushe,

"Ai yanzu bakida mafita banda wacce tawuce kiyi hakuri ki zubawa sarautar Allah ido...." Zuciyarta tafada mata, shiru tayi kawai tana tunani, yanzu ita shikenan haka zatayi rayuwarta da yaro karami wanda baya ganin girmanta? Tunfa daga yanzu ya rainata to inaga wani abu ya hadasu ai sunanta sorry kawai, tsaki taja takoma ta kwanta tana istigfari acikin zuciyarta.

Tun daga ranar har takarasa warwarewa takoma aiki fahad bai sake zuwa gidanba ita anata bangaren hakanma yafi mata kwanciyar hankali saboda baizo inda takeba bare yafada mata bakar maganar da zata hanata bacci kamar yadda yasaba, kokari ma take tayi tasamu ta yakice matsalarshi daga zuciyarta. Shi dinma yayi hakanne domin yabarta ta sarara kuma ta huta sannan shima aiki yasakoshi gaba koda yaushe cikin aiki suke mutum baida lokacin kansa,

Ana saura kwana uku abbanta zai dawo daga tafiyar da yayi masu hayar gidan fahad suka tashi wato wadannan turawan da suka karbi gidanshi dama already sun gyara gidan sai dan gyare gyaren da baza arasa ba. Ranar laraba da daddare Abba yasauka wanda da tunima yajima da dawowa dan dai kawai yabiya ta wurinsu elmustapha ne yagansu, dawowarsa da kwana biyu fahad yarako babansu domin yiwa Abba sannu da zuwa dama awurin maama yake jin komai yanzunma itace tasanar dashi dawowar Abba,

Tunda fahad yagaida Abba yakoma gefe ya zauna yana saurarensu suna tattaunawa cikin fahimtar juna da mutuntawa, ahaka ammah tazo ta samesu suka gaisa ta fita, babu jimawa saiga Bilkisu itama tasha dogon hijabi har kasa,durkusawa tayi ta gaida baba sannan tamike zata fita, hada ido sukayi da fahad ta harareshi wannan karon bai ramaba amaimakon hakama sai yayi murmushi kawai, bayan fitarta ya maida hankalinsa kan maganar da su Abba sukeyi inda abban yake cewa tunda yadawo ai sai ayi maganar tarewar Bilkisu agidanta, dan haka idan har babu matsala nanda sati biyu sai ta tare agidanta nan baba yace babu kuma anyi abu akan gaba saboda dama mutanen da suke zaune agidan fahad din sun fita dan haka ko gobe ake son tariyar babu damuwa, anan dai aka bar zancen azuwan nanda sati biyu zata tare saboda abata dama ta gabatar da dan shirye shiryenta da take son gudanarwa.

Fahad sun bar gidansu Bilkisu cikeda karramawa ga uban kayan tsaraba da Abba yabawa baba, washe gari fahad yasoma gyara gidansa gashi a lissafinsa bazaifi sati daya da tariyar ba zai koma makaranta, haka dai yake ta kaiwa da kawowa danma yayunshi na taimaka masa.

Bilkisu kuwa tun lokacin da abba yasanar da ita maganar tariyar nan take cikin kunci, kullum cikin fushi take hatta khulsum saida ta fahimta har saida ta tambayeta meke faruwa nan ta sanar da ita wai tarewa zatayi nanda yan kwanaki dariya khulsum tayi tace,

"To ai ke gata ma akayi miki wannan uban sanyin dake tunkaro duk wani mai rai ai zakifi more amarcinki tunda gaki ga mijinki.... Danma kun kwafsa kin yarda yayi miki ciki tun kafin ku tare..."

Harararta Bilkisu tayi sannan atunzure tace,

"Dallah ni tashi muje news ko intafi inbarki, ke kika san wani ciki ni ban sanshi ba"

Daga haka tafigi handbag dinta tayi gaba tanata masifa aranta ita daya.

Cikin kwanaki kadan aka gama gyarawa fahad gidansa wannan karon kam komai gaban kansa yakeyi babu maganar tambayar ra'ayin Bilkisu kamar wancan, duk abinda yayi masa shi yakeyi yanzu, babu karya gida yafito yayi das dashi kowa yagani yasan gidan amarya ne, kwana biyu atsakani su maama sukazo da motar kaya aka soma shirya mata kayanta aciki komai sabone fil aledarshi, yana shirin baro cikin asibiti maama tayi masa waya tana tambayarsa wai duka bedrooms din guda biyu nasune?

Dariya ma shi abin yabashi shiyasa bayan sun gama yarawa da maama yakira Bilkisu wadda rabonshi da ita tun sati biyu da suka wuce, har wayar ta tsinke bata daga ba wannan dalilinne yasashi tura mata text massage.

Tun tana cikin bathroom tana wanka take jiyo karar wayarta amma bata fitoba saida tagama tana zuwa taga miss called da massage guda daya massage din tabude bayan ta duba miss called din,

_Ki fadawa kannenki su zaba miki daki guda daya, dayan kuma subarshi empty saboda na matata ne...._

Ganin abinda ya rubuto mata yasata zama agefen gadon tana huci azuciyarta tana tambayar kanta wai ita zai hada da matarshi agida daya? Ai kuwa sam wannan abune wanda bazai taba yuyuwa ba....



*_Ummi Shatu_*


*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*


47**** Kamar a mafarki sai taji abun na damunta, akan me zaice zai hadata da wata agida daya? Ai wallahi bazata taba sabuwa ba idan har yadamu da dole sai yayi auren to sai dai ya nemawa matar tasa wani gidan amma ba wannan ba, cikeda masifa ta jawo wayarta wadda ta cillar kan gado saboda takaici, maama takira amma har ta katse bata dagaba dan haka ta kira meenah wannan dinma saida tayiwa meenah kira biyu sannan Hindu ta daga,

"Meenah kar ku wani bar empty bedroom duka ku saka min kayana ako ina dama ai gado biyu ne ko? So kuyi min jerena ako wanne daki...."

Bata ma jira taji maganar Hindu ba ta katse wayar saboda ita duk atunaninta meenah ce, dukansu dariya abun yabasu lokacin da Hindu ke kora musu labarin fadan da taji Bilkisu nayi,

Ita kam cikin fada da masifa take yin komai tana shiryawa sai babatu takeyi ita kadai,

"Can da iyawarku kaida matar taka...., nidai abinda nasani shine bazai taba yuyuwa ka hadani da karamar yarinya ba salon tazo ta rainani...., kuje can ku karata ka kaita duk inda zaka kaita wannan damuwarku ce ba tawa ba..."

Ahaka ta gama shiryawa tasaka blue din material fitted gown tana daura dan kwali tajiyo karar wayarta, zuwa tayi ta dauka tana ganin fahad ne tayi tsaki ta sake jefa wayar saman gado tafita daga dakin ma gaba daya zuwa dakin ammah wacce ke zaune tana waya da Rabi mai aikinta tana sake karanta mata abubuwan da zata sake hado mata daga kasuwa, zama tayi tana sauraron ammah har tagama wayar ta sauketa daga kunnenta,

"Ammah kunyi waya ne dasu maama?"

Kallonta ammah tayi tana danna wayarta,

"Meya faru?, munyi waya dasu dazu nace musu subar gado daya su saka miki daya saboda wai yace daya dakin idan matarsa tazo anan zata zauna..."

Bata rai Bilkisu tayi kamar karamar yarinya tasoma magana cikin damuwa,

"Kuma shikenan ammah dan matarsa zata zauna aciki ni sai afasa saka min gado biyuna? Ni wallahi yanemi wani gidan yakaita can..."

Girgiza kai ammah tayi tana kallonta,

"Wai dan Allah sai yaushe zaki girmane mai gado? Mijin naki nawa yake da har zakice yayi gida biyu? Shida ba aiki ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????yakeyi ba shine zakice yanemi wani gidan? Kinga.... Tam, maza dai kibari wannan maganar taje kunnen abbanku.... Zakiyi masa bayani nidai babu ruwana..... Karki bari nasake jin wannan maganar kinji dai nafada miki..."

Jin abinda ammah tace yasata sake jin bacin rai ya rufeta yanzu shikenan babu mai goyon bayanta? Haka zata zauna gida daya da karamar yarinya amatsayin kishiyarta? Tun daga lokacin take ta fushi, fushi takeyi da kowa,komai su maama sukace tayi sai tace baza tayiba, kunshi, kitso, gyaran kai duk taki yi bare asa ran zatayi gyaran jiki. Ana saura kwana uku ta tare hajiya iyallo tazo amma wannan karon ita kadai tazo ko yafindo mai gado basu taho tareba wai tana can tana kula da jikokinta wadanda aka yiwa shayi har su shida, ko kadan Bilkisu bata so zuwan iyallo ba wannan karon kamar waccan saboda yanzu abubuwan da iyallon takawo ita ba amfani zatayi dasu ba, kuma haka kawai sai inzauna inta dirkar kayan gyaran jiki saboda wannan yaron? Haka take ta tambayar kanta, tsumi ne hadadde irin na mutanen kauye sai tukudi da gumba amma fafur taki sha sai su maama ne suka rabe atsakaninsu. Lokacin da khulsum tazo kuwa saida suka yi fada da Bilkisu saboda takawo mata hadin kankana da kwakwa sannan kuma tace mata yakamata suje ayi mata kitso da kunshi amma tayi biris, tabe baki khulsum tayi tace,

"Duk dai wannan zille zillen da kikeyi bashi zai hana mu mikaki gidanshi ba jibi ehe... Kuma dole abashi hakkinsa ta dadin rai idan anki kuma ya kwata ta karfin tsiya....."

Shiru Bilkisu tayi bata kulata ba taci gaba da abinda takeyi, nan tasake jiyo maganar khulsum tana cewa,

"Badanma ina tausayawa mutum ba kar dan karamin cikin dake jikinsa ya zubeba ai wallahi da sai na zuga fahad yayiwa mutum lisss..."

"Wai ke kika yimin cikin? Ni kidaina jamin jaraba malama..."

Bilkisu tafada cikin fushi, dariya khulsum tayi taci gaba da tsokanarta, duk yadda sukaso ta gyara kanta da jikinta ki tayi ita kuwa dama ammah bata kulaba tunda tasan rashin yin kitso da lallen bashi zai hana ta tare dinba. Shima fahad bai sake nemanta ba tun lokacin da ya kirata taki dagawa, yasan fushi takeyi saboda yace tare zasu zauna da husnah shi kanshi idan son samune zaifi son ace kowa da wajenta to amma ai baida karfin rike gida biyu shiyasa lokacin da yasamu ayiyah da maganar tace a'a karma yafara saboda bazai iyaba, itama husnan yasanar da ita tare zasu zauna da Bilkisu saboda gara tasani tun yanzu domin so yake Bilkisu tana tarewa yatura asaka musu rana da ita domin shi ya Abba yake jira shima yagama shirinsa tsaf kawai sa ranane yarage. Ranar

27 / 36