KAMAR DA WASA HAUSA NOVELS COMPLETE PDF.doc

Author :  Nil Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   31 / 36

90K to 93K   out of 106.8K words

yakoma nata amma baya nan tun safe yafita shago saboda yataho da dinkuna sosai daga kd, tarba sosai Bilkisu tayiwa nusaiba har husnah tafito suna dan taba hira ita dai bilkisu jine nata saboda bata fiya hayaniya ba ita saima ka zauna da ita awa guda baifi tayi magana sau ukuba zuwa hudu sai dai dasu Hindu da khulsum kawarta tana sakewa sosai tayi hira dasu,wanka ta tashi taje tayi tashirya cikin doguwar gown ta atamfa tafito,tambayar nusaiba tayi me zata dafa mata tace komai ma, kitchen tashiga ta dora girki doya da vegetables sos bayan tagama ta zubo mata takawo mata, zance ta iskesu sunayi wanda ya dangancin kishi sai taji husnah daga ganinta tana cewa,

"Ai kuwa wallahi idan baka rike mijiba wata ce zata shigo ta rikeshi dakyau... Wasu matan akwai sakaci dan watama hatta abin shinfidar miji bata san ta adana ta alkinta ba sai dai idan yanada wata matar tabashi..."

"Ai mata sha'aninmu sai hakuri kishi yayi mana yawa..." Inji nusaiba, ita Bilkisu sarai tasan da ita husnah take sai dai bata da ajin da zata zauna tayi kace nace da ita, ita da wanda ya ajiyeta zatayi, akule tawuni har nusaiba tatafi amma bata tankawa husnah ba, la'asar liss fahad yadawo bata kulashi ba yayi shirinsa yafita ball, da daddare tana shirin bacci sai gashi yashigo tashi tayi tsaye cikin masifa tace,

"Malam bana bukatar wannan bargon da wannan bedsheet din acikin room dina ka fitar min dashi and you better warn your stupid wife wallahi idan tasake attempting yimin bakar magana ko gugar zana sai ranta yabaci saboda ni ba sa'arta bace..."

Tunda yaji haka yasan akwai abinda yafaru ko kuma husnah tafada mata wani abu, fita yayi yamayar dasu blanket din dakin husnah lokacin ma ita tajima da yin bacci, sake komawa yayi dakin Bilkisu yatarar tafito masa da bedsheet da blanket. Zama yayi saman katifar da scissors a hannunshi wanda zai yanka wasu dinkuna,

"Me husnah tayi miki?" Ya tambayeta yana auna atamfar da yaware,

"Meya hana ita baka tambayeta ba?" Tabashi amsa tana kokarin kwanciya,

"Tayi baccine ai..."

"To sai ka bari sai ranar da tatashi saika tambayeta..."

"Allah yabaki hakuri dai zanyi mata magana insha Allah"

Bata cemasa komaiba tayi kwanciyarta tabarshi yana aikin yanka dunkuna, washe gari saida yayiwa husna fada sosai akan koma me tayiwa Bilkisu to kar ta kara aikita irinsa saboda ba mate dinta bace, sannan yace tabata hakuri badan tasoba tabi umarninsa sukaje tabawa Bilkisu hakuri tun daga ranar zamansu yaki dadi saboda husnah gani take kamar fahad yafi son Bilkisu kai kamarma tsoranta yakeyi saboda duk dadin da sukeyi daga Bilkisu tashigo zai daina yauma suna falo suna soyayyarsu yanata goyata amma bilkisu na dawowa daga aiki yadaina da tayi magana sai cewa yayi bata ganin antynta ta dawo ai idan sukayi agabanta gani zatayi kamar sun cimata fuska wannan abu shine yakona mata rai har takasa jurewa saboda ko rikeshi tayi idan Bilkisu na wurin sai ya bata rai ita kuma bayan tadade da fara zargin kamar zamansu akwai wani abu saboda taga duk ranar kwanan Bilkisu da dinkunan da zaiyi yake tafiya dakinta acan zai raba dare yana yankawa amma ita ranar kwananta baya yin abu makamancin wannan. Ita kanta Bilkisu fa kawai tana zaune ne agidan bawai dan tana jin dadin zamanba musamman ma yanzu da taga husnah na neman hanyar da zata rainata tayi mata rashin kunya amma bata shiga shirginta, ranar da fahad zai dawo weekend wato ranar juma'a ranar ne yakama ranar sunan anty Fauziyya yayarsu wacce ta haifi yaronta namiji, su husnah tun safe aka shirya aka tafi sune yan aiki ita kam Bilkisu saida tadawo daga aiki sannan tashirya tatafi dama already tasiyo kayan barkarta. Lokacin da taje su husnah suna dakin mai jego an babbaje itada mutuniyar tata anty juwairiyya wacce ke kara hura mata kai tana zugata tana cewa sai yanzu fahad yayi aure ya auri daidai dashi amma da yawani tashi ya debo yayarsa, ai ko governor yazama itace first lady saboda itace yarinya wacce zasu tsufa tare, zama tayi gefen mai jego wacce keta lale marhabun da ita tare dasu anty asabe da nusaiba matar abba, tana rikeda jaririn anata cika mata gaba da kayan sanyi da abinci,batafi mintuna 20 da zuwaba taji husna na cewa,

"Ni alalen nan ce takasa isata anty juwaira..."

"Amarya ai ke wannan kwadayin mai daliline... Kinada cikakkiyar lafiya"

"Kai anty juwaira nifa ranar girkina ya fahad kwana yake yana yankan dinkuna..."

"Saboda tsabar rashin amfaninki..."

Dukansu da suke cikin dakin dariya sukayi banda Bilkisu wacce tasan da biyu husnah tafadi haka, wato habaici takeyi mata kenan, wai meyasa ita kishiya bata raina abin gori ne? Ta tambayi kanta gaba daya ji tayi gidan sunan ya isheta shiyasa ta yi musu sallama tayi tafiyarta gida, wannan karon bazata fadawa fahad ba amma wallahi takusa nunawa husnah true colour dinta, sai ta nuna mata ita ba sa'arta bace bawai ashekaru kawaiba har awurin mijin ai har gobe tana rikeda tutar soyayyar fahad duk da yayi watsi da ita bawai yana nufin yadaina sonta bane tunda duk lokacin da ranta yabaci agidan nakowa ma sai yabaci. Akule yadawo ya sameta ciki ciki sukayi magana yasake fita, bayan sallar ishah sai gasu tare husnah ya daukota daga gidan sunan dama adakinta yake ranar, bayan kwana biyu yakoma dakin Bilkisu dama akule take dashi saboda gorin da husnah tayi mata na wai kwana yake yi yana yankan dinki adakinta saboda batada amfani, ganin yashigo da atamfa a hannunshi yasata tashi zaune fuskarta adaure,

"Malam yaufa baza kayi min wannan yankan adakina ba... Idan yankan zakayi katafi falo Allah yabamu alkhairi"

Kallonta yayi da mamaki,

"Atamfa guda dayace fa..."

"Ita dinfa, wallahi bazaka yankata adakin nanba, sai dai kakoma can inda kafito kaje kayanka, ko acan din haka kakeyi? Wato saini da aka rainawa wayo ko? To wallahi bazai yuyuba..."

Shi gaba daya yanzu yakasa gane kan Bilkisu kullum awuya take jira kawai take ya tabata suyi rikici duk ta tada masa da hankali shikuma baya son tanka mata saboda husnah yasan tana iya ji ai kuwa kamar yasani dan husnah na labe tana saurarensu,

"Allah yabaki hakuri bari na ajiye"

"A ina? Wallahi kaji narantse atamfar nan bazata kwana cikin dakin nanba mayarta can inda ka dauko...."

Juyawa yayi yafita, husnah najin alamun fitowarshi taruga zuwa dakinta ta kwanta, yana shiga ya jefa atamfar kan akwatunanta yajuya yafita. Zaman dai duk babu dadi gaba daya Bilkisu tasake ramewa duk ta kare atsaye ita wallahi da ace abbanta zai yarda haya zata kama tabar wannan gidan amma tasan ko tafada su Ammah bazasu yarda ba ga yanzu wani sabon iskanci da husnah ta tsira duk ranar girkinta sai ta rinka boye fahad ko Bilkisu nason ganinshi indai yana bacci bazata tasoshi ba sai tace wai dan tsabar rashin tausayi baza abar mutum yahuta ba yaje shago yadawo, shiyasa duk abun yafita ran Bilkisu ko zaman falo bata cika yiba dama kallo ke zaunar da ita da taga abin da rainin hankali sai tasa aka siyo mata babbar plasma sabuwa da receiver da komai aka kafa mata acikin bedroom dinta bayan ta falonta amma fa kallo daya zaka yimata kagane takasa da akiba. Sauki daya yanzu suka samu dukansu basa zama agida saboda husnah takoma makaranta ammafa kusan kullum sai sunzo da kawayenta su Fa'iza suna yadarwa Bilkisu magana sai dai bata fiya jinsuba saboda idan acikin bedroom take zaka isketa ta kunna tv shiyasa bata fiya jiyo hayaniyar da take gudana afalo ba kuma abinda ta lura duk ranar da fahad ke gari husnah bata wannan iskancin bata kawo kowa amma idan baya nan to kullum tare da friends dinta suke zuwa har magrib suna tare, yau ita Bilkisu tana gida bata fita aikiba saboda ciwon mara take yi kamar me kusan tun lokacin da ta fara period bata taba ciwon Mara mai azabar wannan ba shiyasa ko fita batayi ba, saida taji ya lafa mata sannan ta shiga kitchen zata dafa ruwan zafi tana sanye da doguwar riga marar nauyi da hula baka, tana kitchen su husnah suka shigo su uku tana ji husnah na cemusu wai su shiga kitchen su dafa musu abinda suke so, ganin Bilkisu na ciki sai suka fara rashin mutuncin nasu,

"Kawata ya babynmu? Meyake so ne?" Inji fa'iza,

"Ai wai dama kawarmu har mun samu karuwa?" Inji Ruky,

"Tun wanne zamani? Ai ni ba juya bace wallahi kuma sannan matar so ce shiyasa cikin kankanin lokaci aka dirka min ciki, yanzu inajin yayi 2 months da yan kwanaki...."

"Ai wasu ba juya bane kawai duniyancine ke hanasu haihuwa..." Ruky tafada tana dariya, Bilkisu na jinsu tana kokarin juye ruwan zafinta,

"Ehh mana ai dama wasu ba wucema shekarun haihuwar sukayiba kawai tsabar iskancin da suka shuka ne awaje suka yita shan pills suna abortion da haka suka kashe mahaifar...." Husnah tafada tana dariya harda shewa, kashe gas dinta tayi ta dauki tea flask dinta tafita, aganinta rashin class da rashin tunanine zai sata tanka musu saboda yaran da basufi meenah ba karamar kanwarta akanme zata tsaya tayi kace nace dasu? Tana shiga daki tazauna tarasa abinda keyi mata dadi kawai sai tafara kuka kukanne yasaukar mata da zazzabi mai zafi dama gashi bata jin dadin jikinta agaskiya tagaji da wannan rainin wayon dan haka barin gidan fahad zatayi inyaso yazauna da husnan, text ta tura masa cewar ita gida zata tafi, tunda yaga text dinta yasan ba lafiyaba duk da shima din tsakaninsu akwai rashin jituwa amma ai lafiya suka rabu yasan may be itada husnah ne, tun kafin tafada masa abinda yafaru yaji ransa yab?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? aci, aranar yabaro kaduna yadawo gida bayan sallar magrib sai gashi, kowacce na dakinta,dakin Bilkisu yashiga ya sameta zaune tsaf cikin shirinta dama shi take jira tasan yana hanyar zuwa,idanuwanta kadai yakalla yasan tasha kuka,

"Bilkisu meya faru?"

"Kasan me? Nagaji da zama da matarka, kawai ni ka sawwake min inbar mata gidan, ni sa'arta ce da zata rinka kawo kawayenta suna haduwa su zageni? Ni nataba yimata haka? Yarinyar nan yau harda suce waini juyace,kuma wai....." Wani kukan tasake fashewa dashi cikin sauri yazauna kusa da ita ya kwantar da ita kan kirjinsa akaro nafarko,

"Am sorry.... Stop shading your tears... Fada min abinda yafaru wai me?"

Kasa magana tayi sai sautin kukanta dake tashi cikin dakin har lokacin tana rungume ajikinsa yana shafar gadon bayanta, saida yabatar tagama kukan ta dan tsagaita sannan yayi magana,

"Me tace miki bayan haka?"

"Cewa fa sukayi wai saida nagama yawon iskancina nasha pills da abortion sannan na aureka shiyasa wai har yanzu ban haihuba..."

Ji yayi ranshi yabaci sosai kwata kwata bai taba zaton husnah zatayi masa hakaba, sakinta taji yayi ahankali sannan yamike yafita......



Yau banyi editing ba kuyi hakuri da spelling mistakes

*_Ummi Shatu_*


*Littafina na kudine me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



51***Amutukar fusace yashiga dakin husnah, ransa idan yayi dubu to ya baci yau, tana kwance rub da ciki da waya a hannunta tana rubuta assignment, figota yayi ya finciko ta, atsorace tabishi yana rike da ita yana janta har dakin Bilkisu wacce ke zaune har lokacin bata daina kukaba, jin tahowarsu tareda husnah yasata saurin hadiye kukanta ta goge fuskarta, banko kofar fahad yayi yatura husnah yana huci,

"Husnah.... Maimaita abinda kuka fada mata keda kawayenki...."

Zaro ido husnah tayi kafin ta dora hannu aka,

"Nashiga uku ni asma'u...
Anty me mukace miki? Nida wa? Ni yau ma da babu inda naje shine zakiyi min karya ki hada min sharri....." Tun kafin ta rufe bakinta taji wani wawan mari wanda ko tantama batayi fahad ne ya dauketa dashi dan ransa yakai makura wurin baci gaba daya idanuwansa sun juye daga farare zuwa jajaye,

"Waye yake yimiki karyar? Sa'arkice ita? Kifada min abinda yafaru ko inyi ball dake....."

"Ni wallahi karya take yimin... Karya ne.... Bance mata komai ba amma dan tsabar munafurci shine zata hadani dakai saboda tana bakin cikin muna zama lafiya... Wallahi karya tak...."

"Idan kika kara cewa karya take yimiki wallahi sai na fasa miki baki... Dama bakida mutunci ban saniba? Matar tawa zaki saka agaba kirinka zagi? Sa'arki ce? Ni kin taba ganin na zageta? Zaki fada min abinda yafaru ko sai nayi wasan kura dake?...... Ki fada min inda kika ganta tana zubar da ciki ko tana shan pills kamar yadda kuka ce....."

Ganin yayi kan husnah gadan gadan yasa Bilkisu saurin mikewa ta tashi tasha gabanshi, kokarin tureta yayi yana cewa,

"Asma'u baza kiyi min bayanin abinda kukayi ba sai na hau ruwan cikinki?.... Bari na kamaki"

Rikeshi gamm Bilkisu tayi ta kalleshi da idanuwanta wadanda ke jajur, sannan ta kalli husnah,

"Zo ki fice.... Fitar min adaki..."

Sim sim husnah tawuce tana harare harare, duk fahad yana kallonta lallai yarinyar nan munafuka ce wato saima ta nuna ita sam batayi hakaba sharri akayi mata shifa yatsani zama da mutum munafiki wanda baya kaunar zaman lafiya, har husnah tafice Bilkisu na rike dashi, hannuwanshi duka biyu ta kama tasaka cikin nata,

"Kai kuma ai bahaka akeyi ba.... Meyasa zaka kawota gabana har karinka marinta kana neman dukanta akaina....., bazata ji dadiba, gara ka tambayeta kaida ita idanma fadan ne sai kayi mata daga kai sai ita amma idan ka kawota gabana kayi mata fada ai tamkar kayi mata cin fuska ne......"

Kallonta yayi da idanuwanshi wadanda ke cikeda bacin rai shi yasan ba abanza yake kaunar Bilkisu ba, tanada sanyin hali da farar zuciya sam bata da mummunan nufi akan kowa,

"Kiyi hakuri kinji....insha Allah zanyi maganin abun..."

"Na hakura amma gaskiya gida zan tafi.... Gidannan yayi mana kadan mu biyu, matarka bata san ganina haushina takeji, nima kuma haushinta nakeji kaga zama wuri daya bazai yuyu ba... Ni kawai duk ranar da kasamu damar canja min gida sai indawo amma yanzu gida zan tafi...."

Murmushi yayi yajata bakin gado ta zauna shikuma ya tsugunna agabanta yana kallonta,

"Kawai sai kitafi gida kije kice musu kin kasa kishi da yar karamar kanwarki akanta kika dawo gida?"

"Ni ba akanta bane, fitinace bana so.... Kana jin fa abinda suka fada min wai ni yar iskace...."

"Kibar maganar nan pls.... Nidai ai nine na aureki ko? To ban zargeki da hakaba dan haka duk wanda ma zaice kinyi haka kar abin ya dameki tunda ni mijinki ban zargi haka daga gareki ba.......ni nasan atsaftace kike soo don't worry about that...."

Shiru tayi batace komai ba har lokacin idonta bai bar fitar da kwalla ba saboda ba ataba jifanta da wata muguwar magana makamanciyar wannan ba,

"Ina zuwa...." Ganin yamike yasata rikoshi,

"Fahad karfa kace zaka daki yar mutane.... Babu kyau duka...."

"Ni ba dukanta zanyi ba, ina zuwa..."

Dakin husnah yakoma wacce itama sai yanzun takoma bayan tagama jin duk abubuwan da suka fada shida Bilkisu, zama yayi agefen gadonta ita kuma tana tsaye atakure duk atsorace take dashi dan bata taba sanin cewa yanada zuciya har hakaba,

"Husnah abinda kikayi kin kyauta kenan? Meyasa zaki fada mata haka? Kin san zunubin dake cikin wannan maganar kuwa? Ko court fa takaiki za a iya yimiki bulala saboda kazafi kika yimata......."

"Dama ai ita kafi so shiyasa kullum abayanta kake, baka son laifinta...."

"Husnah ba maganar ita nafi so bane... Maganace ta gaskiya.... Bilkisu ba sa'arki bace bai kamata kizo ki rinka fada mata magana irin hakaba..."

"Gaskiya ya fahad wallahi kaima tagama dakai inbanda haka ya daga fada maka magana zaka hau kai ka zauna batare da kayi bincike ba? Ni kasan abinda ta fada min?"

Mikewa yayi cikin fushi,

"Karya kikeyi babu abinda ta fada miki.... Kin san wani abu husnah? Wallahi zan yi mugun bata miki rai akan wannan maganar, matsawar kina son mu shirya to yazama wajibi ki iya bakinki bana son rashin kunya kuma bazan taba lamunta ki raina min mataba saboda ai ko bata girmeki ahaifeba ta rigaki zuwa gidan nan anan kika tarar da ita, ita bata takura miki ta hanaki kwanciyar hankali ba sai kece zaki takura mata? Da lokacin da zan auroki ta tada fitina tanuna bata yarda ba kina tunanin zan aureki ne?, wallahi tun wuri ki shiga hankalinki......"

"Amma dai ya fahad ai....."

"Will you shut up ko sai na bigeki.... Ban san bakida kunyaba ai sai yau... Mun kusa fara fada dake asma'u"

Mikewa yayi cikeda fushi sai kuma taga yakoma ya zauna hannunshi kan kirjinshi, babu shiri yazame ya kwanta kan gadon kafafuwanshi akasa hannunshi dafe da chest dinshi, lumshe idanuwa yayi yana jin bugun zuciyarshi yana fita ahankali ba normal ba, tsugunnawa husna tayi gabanshi ta dafa shi,

"Sannu ya fahad.... Dan Allah kayi hakuri.... Yau kasha maganinka?"

Kai ya daga mata hakan yasata sake matsawa kusa dashi,

"Ka kara wani pls..."

"Nabarshi a kaduna..."

"A'a akwai wani anan... In dauko maka?"

"Kar yazama over dose husnah kinga dazu nasha wani..."

"No bazai zamaba, dan Allah kasha magani"

Tashi tayi ta dauko masa harda ruwa yasha yasake kwanciya babu jimawa bacci yayi gaba dashi, ita wallahi tana son fahad har cikin ranta amma ta tsani bilkisun nan bata kaunarta ko kadan gashi shikuma taga kamar yafi sonta. Bilkisu na dakinta bata sanma abinda ke faruwa ba tadai ga shiru bai dawoba, tunani tayi abinda fahad fa yafada gaskiyane idan taje gida me zata cewa su ammah? Tunda ita dai bada fahad sukayi fada ba tasan su abba bazasu barta ta zauna ba ai jarabar iyallo ma kadai ta isheta tunda kullum tana hanyar zuwa gidan dan bata cikakken sati biyu bata zoba, tashi tayi ta maida kayanta ta ajiye ta hada tea din da tun rana tayi niyyar sha amma yaran nan suka bata mata budget, yau kwata kwata babu abinda tasaka acikinta tun safe, zama tayi tasha tea din sannan tashiga wanka. Abangaren fahad kam yana can yanata bacci dan ko sallar ishah baiyiba har yanzu yanata bacci har 11 sannan yatashi husnah na zaune kasa ta kifa kanta saman gado itama anan baccin yayi gaba da ita, tashi yayi duk jikinsa babu kwari,tashin husnah yayi tana tashi ta tsaya tana kallonsa,

"Tashi ki hau kan gado ki kwanta..."

Tashi tayi tahau kan gadon shikuma yamike saboda baiyi sallar ishah ba gashi ma yunwa yakeji,

"Kinyi sallah?"

Daga masa kai tayi hakan yasashi fita daga cikin dakin yana zaro wayarshi daga aljihunsa, dakin Bilkisu yashiga ga mamakinsa idonta biyu tadai yi shirin bacci da laptop kusa da ita tana rikeda cup din tea,kunnenta ta makala earpiece tana sauraron kundin tarihi na Malam Aminu Ibrahim daurawa, daga kai tayi ta kalleshi dama dogoyen

31 / 36