KAMAR DA WASA HAUSA NOVELS COMPLETE PDF.doc

Author :  Nil Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   25 / 36

72K to 75K   out of 106.8K words

ajiki ta dauki hand bag milk ta dauki wayarta sannan tanufi wurin shoe rack tadauko flat din takalminta tasaka tayi hanyar kofa, sai da takusa zuwa kofar cikin isa da kasaita taji yace,

"Ina zakije?...."

Bata ko kulashiba tayi niyyar fita nan taji yasake maimaita ina zakije?

Kanta tsaye tabude kofar zata fita amma kawai sai ji tayi ya danko waist dinta yadawo da ita baya, sam bataji lokacin da yataso ba bare taji tafiyarsa, mayar da kofar yayi ya rufe, yanda ta sha kunu haka shima yasha kunu, kawar da kanta tayi gefe daya tana huci yayinda shikuma yake kallonta ko kiftawa baya yi,

"Wai meye haka? Wannan wanne irin wulakanci n...."

Bata kai ga karasawa ba taji ya fincikota wanda har saida kirjinsu suka manne wuri daya, numfashinsu ke haduwa kowa yana shakar na kowa, ido ta daga dakyar ta kalleshi shima yana kallonta,

"Wa kika tambaya da zaki fita?....... Ehye?.... Tambayarki nake.... Nace wa kika tambaya?" Yakarasa magana cikin tsawa,

Yana kallon yadda idanuwanta ke kadawa tamkar zata fashe da kuka, cikin bakin ciki da rawar murya tace,

"Ba asaniba..... Dallah ni ka sakeni...."

Sake matseta yayi har lokacin yana rikeda damtsenta daya tana manne kirjinshi,

"Ni kike cewa baki saniba?.... Idan kikayi wasa wallahi daga yau bazaki sake ko taka daidai da kofar gidaba.... Zakiyita zama cikin gidan nan babu fita har sai ranar da na gadamar daukarki na kaiki duk inda nakeso...."

Sake matsota yayi cikin huci yace,

"Sannan kisan irin maganar da zaki rinka fada min idan bahaka ba sai kinyi nadama...."


Fincikarta yayi wanda har kayan hannunta suna zubewa yaje ya jefata kan gado nan ta zabura ta mike wanda hakan yaso bashi dariya amma yadake,

Tsayawa tayi ta rike kugu tana haki tamkar dambe zasuyi,

Matsawo yafara yi ahankali yana cewa,

"Ko dambe zakiyi dani ne? Nace dambe kika tashi yi dani....?"

Kafin tabashi amsa wakar ali jita tafara tashi daga cikin wayarshi, _"Rana da wata suna da haske gimbiyata sai ke soyayyarmu har abada...ko rana da wata sun daina haske gimbiyata sai ke soyayyarmu har abada..... I love u baby.....Sarauniya baby...."_

Komawa yayi da baya yadauki wayar domin yasan husnah ce saboda ita kadai yasawa wannan tune din,

Zama yayi kan bedside drewar dinta yadauki wayar,

"Sweet ma'u ya akayi.... Ko har yanzu fushin akeyi dani?" Yafada yana murmushi kasancewar tun lokacin da yafada mata anmayar da aurensu da Bilkisu bata daukar wayarshi sai yau da ta kirashi,

"Ya fahad Allah kai dinne kana bani headache dayawa...."

Hands free yasaka wayar tayadda Bilkisu zataji komai wacce har lokacin ke tsaye tana rikeda waist dinta,

"Am very sorry one love... Ki yafewa Prince dinki idan bahaka ba ciwon zuciyata yatashi dama kuma kin san ata sanadiyar sonki ya kamani...."

Ajiyar zuciya husnah ta sauke sannan cikin sanyin murya tafurta,

"No ya fahad dan Allah kabari bana son inrasaka.... Na hakura, bazan sake bata maka rai ba.... Ranar ma ban san meya sameni ba har nayi fushi dakai... Am so sorry..."

"Kishi...." Yafada yana murmushi yana satar kallon Bilkisu wacce tacika tayi famm sai huci takeyi kamar bijimin sa,

"U are right.... Ni nasan inada kishi akanka bana son nayi shearing dinka da kowa amma babu yadda zanyi i will accept koma meye...."

"That's why am loving u.... I love u yanmatanah..."

Ai Bilkisu bata jira tagama jin wadannan mugayen kalmomin nashiba ta shige cikin bathroom ta bugo kofar da karfi garammm wadda hatta husnah dake kan waya saida taji, har suka gama waya da husnah Bilkisu bata fitoba, hularshi yadauka yasaka yasan acike take dashi na ya hanata fita unguwa gashi kuma yazo yana waya da wata agabanta duk da baida tabbacin ko tana kishi ko sabanin haka amma yadauki alwashin gano hakan, itace bata saniba duk maganganun da yake fadawa husnah ita yake fadawa indirectly amma yasan bazata ganeba, gaban bathroom din yaje yatsaya yakara kunnensa amma baiji motsin komai ba yasan ba komai takeyi ba,

"Kin dai ji abinda nafada miki ko? Karki sake inji labarin kin fita... Sannan ki kira ita kawar taki kifada mata nahana wannan fitar..."

Cikin jin haushi da masifa yaji tace,

"Sai anfitan... Kayi abinda zakayi... Kuma baza akiratan afada mata dinba kai ka kirata mana da kanka... Aikin ban..."

"Idan kika kuskura kika karasa ko...idan ba tsoro ba kibude kofar mana....", kwafa yayi da karfi sannan yace,

"Ni ai bana kiran matan mutane iya inda Allah ya tsayar dani na tsaya... Gobe aiki kadai nayarda kifita baya ga nan duk inda kikaje keda Allah..."

Bai jira abinda zatace ba yawuce yafita yana jin wayarta nata ringing duk da bai dubaba yasan abokiyar tafiyar tatace taji shiru shine kila take kira, duk da bai fada directly ba tagane da hamood yake da yace wai shi baya kiran matan mutane, jin yafita yasa wasu hawayen bakin ciki zubo mata, wai ita fahad kanin kanin bayanta ke yiwa haka wannan wacce irin kaddara ce? Wai meyasa zaman nan yasake kulluwa?....




*Littafin nan na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



*_Ummi Shatu_*

JIYA IYAU...


*Wannan littafin na kudine me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



43***Tafi mintuna goma cikin bathroom din bata ko motsa ba kawai hawayen bakin ciki da takaicine ke fita daga idanuwanta ba abinda yafi tsaya mata arai irin iko da isar da yake neman fara nuna mata, danme zai sakata agaba yana yi mata tsawa? Bude kofar bathroom din tayi tafito ko zama bata yiba ta nufi falon ammah wacce ke zaune suna gaisawa da Abba amma kafin Bilkisu takarasa har sunyi sallama kasancewar su lokacin salla yayi acan,

Zama tayi idanuwanta duk sun sauya cikin bacin rai tafara magana,

"Ammah gaskiya yakamata kijawa fahad kunne..... Naga abin nasa yana nema yayi yawa, ni bana son nuna isa da gadara...."

"Wani abu yayi miki?" Ammah ta bukata bayan ta zuba mata ido tana sauraronta,

"Ammah waifa har nagama shiryawa zamu fita nida khulsum dubiyar abokiyar aikinmu shine zai wani ce wai baza niba...."

Murmushi ammah tayi kafin tace,

"To ni mai gado menene nawa? Shine dama yakeda ikon yabarki ko ya hanaki kuma tunda ya hana ba shikenan ba?"

Wasu zafafan hawaye taji sun zubo mata sakamakon abinda taji ammah tafada, wato shikenan haka za abarshi azuba masa ido yayita yin abinda ya gadama?

"Amma ammah haka za abarshi....?"

"Mai gado to me kikeso nayi akai? Shine yakeda iko dake bani ba... Akan ya hanaki fita unguwar shine zaki zauna kina kuka? Allah ya kyauta to"

Tashi ammah tayi tafita zuwa kitchen domin ganin wacce wainar Rabi mai aikinta take toyawa ganin haka yasa Bilkisu tashi tafita zuwa dakinta. Tana shiga taji wani abu yatsaya mata arai musamman da ta shaki kamshin turarenshi wanda yatafi yabar mata adakin, karar wayarta ne ya katse mata tunani nan ta daga cikin sanyin murya,

"Haba labour irin wannan jira haka? Kin barni tsaye fiyeda 30 minutes.... Nidai tuni nakoma cikin gida gashi inata kiranki baki daga ba hope u are doing good?"

Ajiyar zuciya Bilkisu tasauke cikin sanyin murya mai kunshe da zafin rai tace,

"Am very sorry kawata,kin san me? Hanani zuwa yayi dan rainin wayon nan har saida yabari nagama shiryawa ina kokarin fitowa yace bazan jeba...."

"Wai wa kike magana ne?" Khulsum ta bukata,

"Fahad fa...."

Dariya khulsum tayi sannan cikin kara tace,

"What? Wowwww.....fahad again? Wonderful... Tofah, kice love kuka zauna yi shiyasa nayita kira kika ki dagawa..."

Cikin fushi Bilkisu tace,

"Malama bana son wulakanci... Abinda yafi love a'a kin manta sex...."

Dariya khulsum tayi cikin tsokana tace,

"Ai shi dinma bazance a'a ba may be kunyi tunda mata da mijinta ai komai na iya faruwa...."

"God forbid...." Daga haka takatse wayar cike da takaicin khulsum, yanzu tasan ba khulsum kadai ba kusan kowa haka zai rinka kallonta fanko ana yimata kallon tayi tarayya da kanin kaninta, kwanciya tayi cikeda bacin rai sai kuma wayar da yakeyi yi tafado mata,

"To wai aure yayi ko kuma budurwarsa ce?" Shine tambayar da tayiwa kanta bata samu amsarta ba tasoma kukan bakin cikin da ya kunsa mata, saida tasha kukanta ta more sannan taji zuciyarta tayi sanyi kadan kawai sai taji bata son sake ganin koda mai kamarsa ne, gaba daya wani irin haushinsa takeji, da haushinsa ta kwana ranar washe gari kuwa bayan tadawo daga aiki harda kulle kofarta gudun kar yashigo mata kamar jiya amma kuma sai taji shiru baima zo ba.

FAHAD

Tunda yabar gidansu Bilkisu yake jin nishadi atare da shi bawai bata mata ran da yayine yafi burgeshi ba a'a yadda yafara sata tayi laushi tun ba aje ko inaba shi yafi bashi dariya, sannan bawai yahanata fita bane dan ya kuntata mata sai dai kawai yana son ya nuna mata tsakaninsu shine jagora kuma shine shugaba koda kuwa shekarunta sun ninka nashi sau dari, dole awannan zaman nasu sai ya gyara mata zama kuma ya nuna mata karfin power din da yake da ita.

Da niyyarshi yaje gidansu husnah amma sam taki yarda yasan kunyarshi takeji sakamakon abinda yafaru tsakaninsu rannan shima kansa kunyar yakeji but babu yanda ya iya saboda mai faruwa ta rigada tafaru. Daren ranar yana kwance kan katifarsu ya tasa kanshi da pillow yadora laptop dinshi kan cikinshi yana kallon wani Nigerian film kawai sai yaga film din yayi kama da irin rayuwarsu shida Bilkisu saboda shima guy din cikin film din matar ta girmeshi amma yadda take tarairayarshi abin gwanin burgewa, lumshe ido yayi yana tunanin to ko sai yaushe shi zai samu irin wannan tarairayar wurin hajjajun tashi, murmushi yayi kafin yace,

"Mai gado rigima..."

"Kai kuma kaida waye kake magana?" Abba yace dashi wanda shigowarshi kenan cikin dakin,

"Ya Abba kallo nake yi, kasan wani lokacin idan mutum yana kallo ko yana karanta novel kamar me aljanu yake zama saboda zakaji yana magana shi kadai...."

"Gaskiya kam... Allah yabada sa'a"

Har yagama kallon baibar tuna bilkisu ba hakama lokacin da yazo yin bacci murmushi yarinka yi shi daya. Washe gari bai samu zuwa gidansu ba saboda sunsha aiki sosai a lab shi kansa bai samu tasowa ba sai 6 shiyasa kawai yayi zamansa agida yahuta dan ko salim basu haduba ranar,yana so yakira Bilkisu amma bayason tasamu dama dayawa akanshi shiyasa ya shareta yakira husnah suka raba dare suna hira, washe gari kam da wuri yadawo gida domin lokacin da yadawo ma 3 batayiba, shago yawuce bayan yayi wanka domin akwai wasu dinkuna da aka aiko masa daga abuja tun shekaran jiya wata yar makarantarsu shiyasa can yaje yafara yankawa saboda cikin week dinnan takeso, karfe biyar daidai yabar dinkunan yafita yauma yana son yaje yaga dramar da zasuyi shida mutuniyar tasa, duk da kananun kayane ajikinsa haka yatafi gidan surukai, yana zuwa su ammah na fita itada driver da Rabi mai aikinta shi da yazaci ma Bilkisu ce sai yaga ba ita bace,

Dama yana jin kunyar zuwa ahaka ammah taganshi da kananun kaya maroon din riga mai rubutun yes ajiki har sau uku sai bakin wando da p cap, koda wasa Bilkisu bata zaci zaizo ba da bazatayi saken barin kofarta bude ba, yauma baccin takeyi kamar mai shan wani abu domin sun daura itada baccin yamma yanzu tunda ba nadare takeyi sosaiba zama yayi gefen gadon dan mugunta maimakon ya kyaleta amma sai yafara neman hanyar da zai tadata. Tv yakalla da alama da kallo takeyi before baccin ya dauketa volume yakara Wanda tajishi har tsakar kanta babu shiri ta bude idanuwa tana laluben remote,

Ganinshi zaune yasata hade rai sosai kamar yadda shima yayi,

Hijabi ta yayima ta saka tana harare harare, baki yatabe cikin ranshi yace,

"Nadai gani..."

Daga shi har ita babu wadda yayi magana suna zaune shiru shidai hankalinsa nakan tv ita kuma ta dauke kai gefe daya cikeda jin haushinsa,diff nepa suka dauke wuta zamansa yagyara akan gadon sosai ya jingina bayan yadauki kafafuwansa gaba daya ya azasu bisa gadon, wayarshi yaciro yakira mukhtar saboda dazu lokacin da yafito daga shago yaga miss called dinshi yasan lokacin da yabar wayar a charge ne yakirashi,

"Ango howfar?" Mukhtar yafada yana dariya, dariya shima fahad yayi sannan yace,

"Kajika wannan ai tsohon zance ne abinda ba yau aka daura auren ba bakuma jiyaba..."

Bilkisu na jin yafadi haka tamike daga kan gadon ta sauka saboda tasan duk yadda akayi maganarta akeyi matsalar auren yaro kenan komai zai iya kwashewa wanda yashafi sirrinsa da iyalinsa yafadawa friends dinshi ta ayyana hakan cikin ranta, bathroom tashiga babu jimawa tafito fuskarta jike da ruwa alamun wanketa tayi lokacin yagama wayar yana dai cigaba da latse latse awayar,

"Karka kara shigo min daki ahaka, sannan karka kuma gigin tashina idan ina yin bacci...." Tafada cikin muryar dake nuna fushi karara bai tanka mata ba taji yana kiran waya domin a speaker yasaka, laptop dinta ta dauka ta matsa can kan prayer rug dinta ta zauna,

"Yanmatanah ya azumin?" Taji yafada cikin karya harshe,

"Babu wahala ya fahad... Ankusa ansha ruwa ma ai"

"To me zan kawo miki?"

"Kanka...." Tafada muryarta ahankali,

"Ko baki fada ba ai dama ni nakine ke kadai...."

"A'a ya fahad badai ni kadai ba bayan kayi min kishiya da tsohuwar matarka bayan kuma...." Saurin cire wayar daga hands free yayi sakamakon jin husnah na neman yimishi baran barama, duk abinda yakeyi Bilkisu najinsu shiyasa bata san lokacin da ta mike afusace ba taje gabansa ta tsaya tana huci,

"Tashi kafice min daga daki....I said get out from my room...." Katse wayar yayi sannan ya kalleta fuskarshi atamke,

"Daina yimin tsawa aka.... Ban son hayaniya"

"Anyi din... Katashi kafitar min adaki kuma karka sake dawowa..."

Yi yayi kamar baijita ba, hakan yasake kular da ita,

"Fahad katashi kabar cikin dakin nan nace..., akanme zakazo kana kawo min nonsense anan...."

Tun kafin takarasa yatashi yahadata da bango ya matse,

"Wa kike yiwa shouting aka? Ni sa'anki ne?"

Wata uwar harara ta dalla masa kafin ta tureshi tana cewa,

"Kai waye da baza ayi maka shouting akai ba? Ubana ne kai? Zaka wani zo min har cikin daki ina baccina katada ni sannan kazauna kana damuna, bazanyi tolerating wannan ba...."

Tsayawa yayi yana kallonta har saida tagama sannan yace,

"Ki gama fadin duk abinda ke ranki amma idan kika bari na kamaki ko...."

"Idan katashi dukana bayan ka kamanin ka dakeni da ice ko da dorina mai baki dubu..."

"Ni ai ba mahaukaci bane ko jahili da zan zauna ina dukan mata... Koda yake su wasu shashashan matan ai sunfi son mijin da zai dakesu...."

Haushin da ya rufeta yafi na dazu shiyasa tasake tunzura ta hayayyako masa cikin zafin rai da kunar zuciya tace,

"Ai maganar ciki ba magana bace idan har ba tsoro akejiba afito fili afada amma bawai ayita magana atukunkune ba... Idan anso masu dukan ai sun cancanta asosu dinne..."

Baki yatabe sannan yace,

"To ai dadin abin dai su babu wata soyayya da za anuna musu sai ta duka, akamasu a lakada musu duka idan dare yayi kuma arabesu amma da rana babu marabarsu da jakuna while wasu matan suna can ana riritasu ba ason ko kuda yasauka akansu...."

"Kafita min adaki nagaji da wannan hayaniyar taka..."

"Baza afita dinba..."

"Saboda kai...."

Bata karasa ba taji ya shako ta, idanuwansa cikin nata yake kusanta fuskarshi kan tata tayadda kusancin nasu har yai yawa, lumshe idanuwa tayi tana jiran jin bakinsa kan nata dan taga kamar hakance manufarshi amma sai taji sabanin haka dal taji ya dalle mata baki yana cewa,

"Wannan bakin naki na rashin kunya nakusa nayi maganinsa....sai na kasheshi murus tayadda bazai kara fada min bakar magana ba...." Ita kanta saida taji tsikar jikinta tana tashi saboda yadda yayi maganar, su da suke fada amma voice dinshi tayi sanyi takoma cool sosai sannan tasauya tana fita a rarrabe sabanin dazu kodan kusancin dake tsakaninsu ne oho,kasa bude idanuwanta tayi sai dai tana ta kokarin kwace kanta daga rikon da yayi mata saboda hatta bugun da zuciyarshi keyi tana jinshi kamar yadda shima yake jin nata kasancewar manne suke da chest din juna wani karin takaicin ma shine babu fa komai ajikinta sai iya yar doguwar rigar da ta zira sai hijabi....



*_Ummi Shatu_*

*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



44****Dariya ma shi taso bashi saboda yadda ta runtse idanuwa tana jiran taji abinda zai biyo baya, afirgice ta bude idanuwanta tana kallonshi saboda jin yadda ya take mata babban dan yatsan kafarta, muryarta na sarkewa tana rawa tafara hankadeshi tana cewa,

"Meye haka... ? Dallah ni sakeni..."

Sake damketa yayi yana kokarin saita kanshi, rikon da yayi mata ba karamin riko bane domin da irinta guda biyar zasu hadu ba lallai su iya kwatarta ba,

"Kin san me? Ina raga miki nefa saboda wani dalili wanda nabarwa kaina sani amma wallahi idan kikayi wasa...."

"Kadaina raga min din, kayi duk abinda zakayi....."

Tafada cikin jin haushin abinda yayi mata, juyi daya yayi ya canja musu position ita takoma jikin bango,

"Karki damu kiyi tayi min rashin kunya akwai ranar fanshewa, duk ranar da natashi hukuntaki kisa aranki ranar sai kinyi kuka da idanuwanki...."

"Dan Allah idan katashi yin hukuncin ka kasheni har lahira...."

Murmushin mugunta yayi wanda itama dakanta saida ta fahimci hakan domin da alama bai kai har zuci ba duba da yadda ya cure baki,

"Bazan kasheki ba amma zaki wahala over..... Sai kin gane ke karamar yarinyace ranar..."

"Kaine karamin yaro bani ba....."

Wata matsa yasake yimata hakan yasata kokarin tureshi tana ta huci saboda bacin rai,

Saida yabari tayi nisa wurin kokarin tureshi ta gama sakar jiki ya murde hijabin ya yar, nan sabon fada yatashi domin da iya karfinta take kokarin dauko hijabin daga kasa shikuma yasa kafa ya take, durkushewa tayi awurin tahada kai da gwiwa bayan tasaka kukan zuci,

"Matsoraciya kawai..... " yafada yana murmushi, daga haka yafice yabarta sai faman kuka take kukan bakin cikin rainatan da fahad yayi domin yanzu tagane yagama rainata tsaf sam baya ganin girmanta gashi duk maganar da tazo bakinshi sai yafada mata sai kace wata mate dinshi,

"Ni Bilkisu naga takaina.... Wannan wacce irin rayuwa ce..."

Haka taketa fada cikin kuka har tsawon wani lokaci, saida tagama kukanta ta share sannan tashiga wanka tafito duk sai faman kumbure kumbure takeyi ita kadai ahaka su ammah suka dawo suka sameta duk bata da cikakkiyar walwala sai cika take tana batsewa ita dai ammah idone nata batace uffan ba.

Washe gari awurin aiki khulsum tabi ta dameta akan takira fahad ta tambayeshi idan yabarta sai su wuce duba Christy basai sun koma gidaba saboda idan suka bari aka sallameta har tadawo aiki ba karamar kunya zasu jiba, agaba khulsum tasata da naci dole ta tashi tafita waje itafa bama ta da no dinshi dan rainin hankali, maama takira tana dagawa

25 / 36