KAMAR DA WASA HAUSA NOVELS COMPLETE PDF.doc

Author :  Nil Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   13 / 36

36K to 39K   out of 106.8K words

tunda kince inshiga to zan shiga din"

Bata kara cewa komai ba shima haka har yagama yatashi yafita.

Haka zaman nasu yaci gaba da kasancewa,watansu daya da aure taje gida tawuni cur har dare lokacin ana sa ran ganin watan Ramadan nanda kwanaki uku zuwa hudu ammah kuwa mahaifiyarta har yau bata taka taje gidan ba, duk wata siyayya da suke bukata fahad ya kokarta ya iyota dama ba wasu kaya masu yawa bane domin sunada kayan abinci enough kawai dai sai dan abinda ba arasa ba, ranar da aka tashi da azumi ranar bilkisu tatashi da period asanyaye take komai sakamakon ciwon da mararta ke danyi mata kadan, ruwan zafi ta dafa tasha lipton ko zataji dan dama dama shi dai gogan yana kwance abinsa yanata bacci shiyasa bata yarda ta dafa komai ba tabari har saida yatashi yayi wanka yafita duk yayi wani kalar tausayi kamar yauce ranar farko da yafara azumin, saida ta tabbatar yafita sannan tatashi ta dora indomie, ta juye indomie din tana soya kwai sai gashi yadawo yamanta key din drewar shagonsu wadda suke ajiye kayan mutane aciki idan ankawo musu dinki,

Jin kamshi ya cika gidan yasashi binta kitchen din bayan ya dauki key din,

"Ranki yadade ke bakya azuminne ko kema yar ganin watance?"

Banza tayi dashi taci gaba da abinda takeyi amma harga Allah bataso yasan bata azumi ba,

"Ko dai.....!"

Juyowa tayi ta antaya masa harara hakan tasa yayi shiru,

"Allah yabaki hakuri mantawa nayi ashe suhur zakiyi, ayi suhur lafiya"

Bai jira tajiyo ba yagudu yabar gidan yana dariya, shi dai yasha jin malamai suna cewa mata masu al'ada basa azumi wato itama hajjaju yau hakan take kenan, tunda yabar gidan bai dawoba sai da aka kusa shan ruwa, a kitchen ya jiyota tana aiki shikam yau duk yayi laushi ga uban dinkunan da ya yanyanka shiyasa can ma yabarosu sai bayan ansha ruwa zai koma yafara hadawa. Yajima akwance ga kayan da yazo dasu amma yakasa tashi yakai mata ita kuma bata san yadawo ba, saida ta dora kosai kafin man yayi zafi tafito daukar wayarta zata kirashi tace yataho mata da mayonnaise taganshi kwance, yau kam an zuba rana ga zafi shiyasa azumin ke wahalar da mutane, kamar zatayi dariya amma ta danne ta wuce tana yimasa sannu, bayan tadawo ta dauki ledar da yashigo da ita tawuce kitchen wanda fruits ne aciki yasiyo, dakyar ya iya tashi yayi wanka lokacin yaji karfin jikinsa, yana gaban mirror zaune yaji wayarshi na kara, ganin salim ne yasashi dauka bayan yayi tagumin dole,

"Abokina gani nan zanzo asha ruwa dani fa..."

"Sai kazo to"

Daga haka yakatse wayar duk atunaninshi da wasa salim yake bayan yagama shiryawa yasa three quarter da t shirt yafito falo yasake kwanciya babu jimawa yaji ana knocking akasalance yaje yabude salim din kuwa yagani dagaske, cikin murmushi ya mika masa hannu sukayi musabaha yashigo dashi har falo,bedroom yashiga yadauko hijab din bilkisu yabita kitchen, ya dora mata saman kafadarta, juyowa tayi ta kalleshi yau baya magana saboda azumi na dukanshi,

"Salim ne yazo" abinda ya iya fada kenan yajuya yafita, saida tagama komai sannan aka kira salla, fruit salad ne bata jima da gamawa ba lokacin kayan ta tattaro gaba daya ta kawo musu falo har lokacin gogan akwance yake yakasa tashi shiyasa salim ya kalleta yana dariya bayan sun gaisa yace,

"Hajjaju wannan fa yau sai kinzo kin dagashi dan yakasa tashi"

Dariya tayi takoma kitchen takawo sauran kayan ta ajiye musu sannan ta kalli fahad wanda ke kwance rub da ciki,

"Tashi kasha ruwan mana...."

Hannu yamika mata saboda ganin idon salim bata kiba takama nashi yatashi zaune azuciyarsa yana cewa,

"Wannan badan ansha ruwaba ai sunan azumina karyayye irin wannan laushi haka"

Kunu ta zuba masa ta mika masa sannan tace,

"Karka sha abu mai sanyi yanzu sai an dan jima, kafara shan mai zafi tukunna"

Kai yadaga mata shi dai salim tuni yahada tea dinsa yana sha da kosai, juyawa tayi tawuce daki tabasu wuri tana zuwa tashiga wanka. Su fahad kuwa bayan ciki ya dan dauka fanfon waje sukaje sukayi alwala sannan sukazo sukayi salla bayan sun idar suka dora da ciye ciyensu sai lokacin bakin fahad yabude sunata hira da salim, bilkisu na fitowa sanye da hijab har kasa tanata zuba kamshi fahad ya kalleta ya dage girarshi guda daya cikeda tsokana yace,

"Hajjaju sannu da shan ruwa, ansha ruwa lafiya?"

Ita dashi sun san meyake nufi amma shi salim bai saniba shiyasa shima yayi mata sannu da shan ruwan, iya na salim din kawai ta amsa tawuce kitchen tazubo dankali da kosai tafito,

"Ranki yadade sannu da shan ruwa fa naketa yimiki amma kin shareni laifin me nayi?"

"Yawwa sannu"

Murmushi yayi ya saci kallonta ta zabga masa harara, tana jinsu sai surutu sukeyi kasancewar sun koshi, suna gamawa suka mike zasu fita, kaya fahad yaje yasauya sannan suka fice yana sake tsokanarta,

"Hajjaju yau mun kai daya ko?"

"Goma aka kai" Tafada cikin gatse,

Dariya yayi yaja hannun salim suka fita, itama wurinda suka ci abincin ta zauna ta kintsa sannan ta kwashe kayan takai kitchen tawuce daki,takardar hutunta take son turawa ta mail domin daga gobe ko jibi take son farawa.....


*Dan Allah idan har baki biya kudin littafin nanba karki karanta hakkin wasu domin na siyarwa ne.*



*_Ummi Shatu_*

? *HASKE WRITERS ASSO*


*KAMAR DA WASA....!*


*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*



*23*



***Bai samu yadawo gidanba sai wurin karfe 10 bilkisu duk tsoro ya isheta domin bata taba zama agidan ita kadai da daddare ba,tana daki tarufe da key yashigo kwankwasa mata kofa yayi dakyar ta tashi ta bude dan tsoro tana ganin shine ta harareshi,cikin alamun atsorace take tafurta,

"Ina kaje kakai dare haka?"

"Ranki yadade daga shago nake wallahi, bayan mun fita daga nan salla mukaje mukayi daga can kuma shine naje gida nayiwa su ayiyah barka da shan ruwa shine nawuce shago"

Bashi hanya tayi yawuce ciki tana cewa

"To gaskiya kar ka kara kaiwa haka awaje"

"To ranki yadade"

Falo yasake fitowa yawuce kitchen yazubo abinci yaci sannan yayi shirin bacci, da asuba itace ta tasheshi ya tashi yayi suhur, kallonta yayi tana kwance kan gado tana shirin yin wani baccin bayan yayi brush yafito,

"Nima anya gobe zanyi azumin nan kuwa? To naga wadanda suka fini ma basayi"

Tana jinsa tayi biris dashi daga karshe yafice yaje yayi suhur din saida yayi sallar asubah sannan ya kwanta. Washe gari tafara hutunta kamar yadda ta nema, kullum tare suke shan ruwa da salim ranar da akayi azumi na biyar sukaje gidansu fahad suka yimusu sannu da shan ruwa bayan Bilkisu ta siya musu kayan tea, shi kuwa fahad kayan marmari yasiya musu suka kai musu washe gari kuma suka je gidansu Bilkisu can dinma kayan marmarin fahad yasiya cikin manyan ledoji suka kai ita surukuntar fahad da ammah dariya take bata domin basa sakewa da juna, har karfe 9 nadare suna gidan wurin goma suka dawo gida. Bilkisu sai da tasha azumi bakwai ana takwas ta dauka danma ranar ansamu ni'ima agari dan har ruwa aka sheka shiyasa bata wani jishi ba sosai, bayan ansha ruwa fahad ya fara halin nasa na tsokana, har bedroom yabita yabar salim afalo,

"Hajjaju yau wasu takwas suka kaifa wasu kuma bakwai wasu shida ke kuma first ramadan yau"

Harararshi tayi ta gyara zamanta,

"Kafita daga idona..."

Ficewa yayi daga dakin gaba daya yana dariya, akwana atashi haka azumin yafara tafiya domin har anfara lissafin salla, duk kannenta babu wadda batazo ba ita da mijinta sunyi mata barka da shan ruwa ba, azumi yaraba tsakiya abba ya aiko musu da kaya kaca kaca kayan tea ne, kayan abinci da sauransu ba ita kadaiba harsu mamaa kowa ya aika masa dashi. Tunda salla ta taho fahad yazama busy domin aiki yayi musu yawa dama duk karshen azumi ashago suke kwana su kwana suna aiki amma wannan karon saboda bilkisu yahakura sai dai yataho da kayan gida yayita yankawa da safe idan yafita sai ya dinka, ana saura kwana biyar salla yake tambayarta wai ita bazata yi dinkin salla ba ehh tace masa kawai, har ana igobe salla bai samu kansa ba cefane ma sai yaro yatura yace yaje tafada masa duk abinda take bukata sai yazo yabashi kudin yaje yasiyo yakai mata, zamansa agidan yanzu kalilan ne, dawowarta daga kunshi kenan itada khulsum dan aiken yazo list tayi tabashi na abubuwan da take bukata domin shinkafa ma ita zata dafa ranar sallar ba tuwoba. Fahad bai dawo gidanba sai 11 nadare domin acanma yasha ruwa yau, ido biyu yasamu bilkisu batayi bacciba domin itama duk vegetables din da zata bukata ta zauna ta gyara gamawarta kenan yashigo amutukar gajiye,atamfa yar ubansu ya dinko mata dark pink mai zanen agogo ajiki, karba tayi tana kallon dinkin da yayi mata riga da skirt fitted, daga atamfar har dinkin sunyi mata kyau,

"Thank you..." Tafada cikin nuna alamun jin dadi, bai amsaba ya kalleta,

"Duk wannan kwalliyar ni aka yiwa?"

Yafada cikeda tsokana,

"Kai kasani..."

Dariya yayi yawuce bathroom domin watsa ruwa. Bayan yafito ya dauki shirgin shimfidarsa yafita,

"Ni wai ko tausayina ma ba ayi kullum akoroni falo hmmm"

Washe gari akayi salla, tun da aka sauko taketa samun baki,fahad ya hade cikin dark blue din shadda harda hula yayi kyau sosai, saida yaci abincin sallar da tayi sannan yafita, su mariyane sukayi mata rabon abinci, aranar da yamma sukaje gidansu fahad din ita dashi barka da salla da gidan yayyenshi washe gari kuma sukaje gidansu Bilkisu, bayan salla da kwana biyu kuma suka tafi garko gaida hajiya iyallo.

Bayan salla da kwana biyar saiga fahad da sabon roba roba dama tun safe taga yafice ranar bai zauna yayi baccin safen nanba,tana tsakar gida tana karatun littafin hausa yashig??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????o gidan da babur din,dakatawa tayi da abinda takeyi ta tsaya tana kallonsa daga shi sai three quarter da bakar t shirt,sam bata san cewar ahaka yafita ba sai yanzu,

"Wannan roba robar fa...?"

"Ranki yadade nawane,dan kudina da na samu da sallar nan ne duk na tattare naje nasiyo machine dinnan"

"Allah yasanya alkhairi, kuma shine kafita har wata uwar duniya ahaka?"

Kallon jikinsa yayi bayan yakafe Babur din,

"Meya faru da bazan fita ahaka ba?"

Girgiza kai tayi taci gaba da abinda takeyi,

"Yadai kamata idan angirma asan angirma..."

Murmushi yayi yana shafa sumar kanshi,

"Hakane, bari nayi wanka naje nayi aski sumata tafara yawa..."

Bata tanka masaba yawuce ciki, saida tagama abinda takeyi sannan tatashi tana kallon babur din nashi, farine tass sabo fill sai kyalli yake yi abayan machine din wurin daura lamba andaura wani kyakkyawan abu mai kamada madubi wanda ajiki aka rubuta _prince_ adan karkace, girgiza kai tayi azuciyarta tana cewa,

"Wannan yaron kana fama da kuruciya.."

Falo tashiga baya ciki da alama yashiga wankan da yace zaiyi, bedroom tawuce domin ajiye nail cutter din da tagama amfani da ita, maganarshi tajiyo daga cikin bathroom,

"Hajjaju dan Allah kifita zan fito.... Wallahi babu kaya ajikina"

"Ni nasa kashiga wankan ahaka?"

Bakin kofar ya matso sosai,

"Gaskiya kifita, kemafa boye min kikeyi ba dole nima inboye jikina ba"

Bata kara bi takansa ba ta ficewarta dama ba zama tazo yiba saida ya tabbatar tafita sannan yafito daga shi sai towel, agurguje yashirya wai dan kar tashigo ta sameshi ahaka, kananan kaya yasaka sannan yafita falo, abincin shi da yafita baici ba ya dauko yaci sannan yafice, su ayiyah yaje yakaiwa Babur din suka gani da sauran yan uwa dake kusa ranar ko filin ball baijeba dan bashi yadawo gidanba sai bayan sallar ishah kasancewar babu wuta agari yasa bilkisu bata samu zarafin ganin askin kanshi ba da yayi, yana dining yana cin tuwon da tayi na semo miyar busasshiyar kubewa wacce taji busasshen kifi tashiga daki abinta tayi shirin bacci. Kudurtawa yayi aransa cewa nan bada jimawa ba zai kawo canji awannan zaman nasu, gaskiya yazama dole suyi rayuwa irin wacce kowanne miji da matarsa keyi, kamar kullum shimfidarsa yayi afalo ya kwanta bacci, washe gari tatashi da farin ciki domin su maama sunce mata zasu zo su wunar mata duk da itama ayau bata tashi da wuriba makara tayi, saida tafara yin wanka sannan ta fito domin shiga kitchen, yana kwance saman doguwar kujera husnah nata damunshi da kira ganin tayi masa miss called har guda uku yasashi dagawa a na hudun hakan yayi daidai da fitowar bilkisu bata ko kalleshi ba tawuce kitchen abinta, saida yagama wayar da yakeyi sannan yashiga wanka batare da ya debe shimfidarshi ba, yana gaban mirror yana taje sumarshi bilkisu tashigo binshi tayi da kallo musamman ma sumar kanshi domin wani irin aski ne akayi masa duk an saisaye gefe da gefe amma tsakiyar ba ako taba ba,

"Hajjaju na ina kwana?"

Saida tasake kallon kanshi sannan ta amsa da,

"Lafiya lau, yanzu dama wannan shine askin da kake cewa zakayi? Gaskiya yakamata kasan kagirma wallahi"

Wani dan malalacin murmushi yayi ya kalleta ta cikin mirror din yana cigaba da taje kanshi,

"Wai hajjaju sai kiyita cewa nagirma bayan har yanzu ban girmaba tunda babu wani abu da ya canja.... Ina dai saka ran zan girman very soon wallahi kuma no marcy"

"Ni ba dogon bayani na tambayeka ba, waccan shimfidar da ka kwana akai wa kabarwa ya dauke maka?"

"Matata mana..."

Kallonshi tayi sosai sannan tajuya tafita batace dashi komai ba, koda yagama yafito yanata tutturo baki ya harhada kayan ya kwashe yakai ciki sannan yasake fitowa lokacin tagama hada komai na karyawa saida yayi breakfast sannan yamike yana kallonta,

"Ranki yadade mu mun tafi shago zamu karasa dinka kayan da basu samu shiga da salla ba"

"Allah yabada sa'a"

"Amin godiya nake"

Gidan tagyara bayan fitarsa tana gamawa takoma kitchen tahada wanke wanke tafara bayan tagama tashiga bedroom tana gyarawa taji sallamar su maama nan gida ya rude da farin cikin ganin junansu da sukayi su ukune sukazo har huda ta hudu bajewa sukayi afalo suna shagali.

A lissafin bilkisu yau zata koma aiki shiyasa tatashi da wuri tayi komai nata na aikin gida sannan tayi shirin fita nan fahad yace zai kaita a machine dinsa dama bata taba hawaba ba wai dan tasoba tayarda, tana gama shiryawa shima yafito da three quarter da body hug,

"Kasan me? Nifa bazaka kaini ahaka ba gaskiya, meyasa kake hakane?"

"Gaskiya hajjaju kina yawa..."

Ciki yasake komawa yasako jallabiya ruwan kasa yadawo yadauketa suka tafi yau kam jinsa yake acikin wani yanayi wanda bai taba tsintar kansa ba, kusancinsu da bilkisu ya haifar mata da wani lamari mai girman gaske kun san yanda lifan yake wurin zaman baida wani girma, abakin gate din office dinsu ya ajiyeta bai bari taga idonshi ba yayi wani kasa da ido, saida yaga shigarta ciki sannan yajuya yatafi. Da tatashi ma shi yaje ya daukota yasamu khulsum nata yimata tsiya itama tana ramawa, koda ya kawota gida baiko shigaba yakoma shago. Da daddare kuwa har tafara bacci taji shigowarsa dakin yana kokarin yin shimfida agaban gadonta, kallonshi tayi bayan tasa hijab tatashi zaune,

"Ji mana malam, me zakayi?"

"Bacci, yau anan zan kwana"

"Saboda wanne dalili?"

"Wallahi yau tsoron kwana ni daya nakeyi, dan Allah karki koreni"

Komawa tayi takwanta tana cewa,

"Tun da lokacin da kake kwana afalon bakaji tsoronba sai yanzu?"

"To ai ban taba tsorata ba sai yau shiyasa"

Juya masa baya tayi taja bargo tarufe gaba daya jikinta tana cewa,

"Nidai idan kagama ka kashe min wuta pls"

Duk da baya son duhu amma babu yadda ya iya haka yakashe wutar tunda yanaso ya kwana adakin atunaninsa tahakanne kadai zai sa yakara samun kusanci da ita. Washe gari tana son taje kitso ta can kuma zata biya ta gidansu khulsum domin ta dubata saboda taga text dinta cewar bata da lafiya yau, shine yakaita duk inda zataje bayan tagama yakoma daukota, kallonshi tayi sama da kasa yana sanye da koriyar t shirt mai gajeren hannu da hoton tsintsaye ajiki anrubuta angry birds, sai bakin wando mai kyau amma dan tsiya an yanke gwiwar an wani tsagashi shiyasa ga gwiwarsa nan awaje ga wani dan banzan askin da ya sarkaba yanzu irin wadanda yan kwallo keyi ko musicians awani saisaye gefe da gefe amma kuma tsakiyar atara uban suma, ita duk ma ashigar tasa wannan askinne yafi yimata takaici,shi dai kallon tsaf yake yimata ta cikin bakin glass din dake fuskarsa kasancewarshi mai hasken fata glass din ba karamin kyau yayi masa ba dama yanzu baya raboda saka glass tunda yasai babur saboda iska da kwarukan dake fadawa mutum ido idan yana tuki,

Yanda take kare masa kallo haka shima yake kare mata kallon batare da ta saniba,

"Wai kai dan Allah sai yaushe zaka girma ne? Kullum kai kenan cikin shiga marar kan gado"

"To hajjaju wai yau kuma meye laifin shigar tawa?"

"Oho..."

Daga haka ta tattare skirt dinta ta hau machine din, juyawa yayi ya kalli kafarta duk kwaurinta awaje yau bata saka safa ba,

"Ranki yadade ki sake jan skirt din naki kirufe kafarki"

"Muje kawai ko naja ba rufewa zaiyi ba tunda ba zani bane"

Saida ya tura baki sannan yafigi machine din yaringa bin lungu wai dan kar yabi ta cikin gari mutane su ganta.

***
Ahalin yanzu basuda wani matsala a zamansu sai dai fa har gobe zamane suke yinsa irin na yaya da kani bawai mata da miji ba domin har yau dagashi har ita basu san menene aurenba suna dai zaune ne kawai tsawon watanni biyar da aurensu, tun ranar da yace mata yana jin tsoron kwana shi kadai yadawo kwana cikin dakin amma yana kasa ita kuma hakimar na kan gado,yau tunda asuba taga kiran maama tana dagawa taji tace mata ankai meenah asibiti ana zaton ko haihuwace, nan tayi maza tashiga kitchen domin hada abincin da zata tafi musu dashi asibiti dama shiyasa yanzu bata kashe wayarta da daddare saboda tana tunanin za anemeta saboda daga meenah har Hindu cikinsu yatsufa, fahad yana kwance yanata baccinsa bai san meyake gudana ba saida tagama komai tayi wanka sannan ta tasheshi lokacin karfe 6 nasafe, da kayan dake jikinsa ya dauki key zai fita ta dakatar dashi,

"Ba dai ahaka zaka fita ba ko?"

Fasa fitar yayi yaje yacire armless din rigar dake jikinsa yasaka jallabiya harda hula sannan yafita, suna tafe yana ta kunkuni,

"Wai sai anyi abu ace wani kagirma bayan har yanzu ayaronka kake tunda babu abinda ya canja... Hmmmm zan girman dai akwai lokaci"

Ita dai da yake hankalinta ma baya wurin bata san meyake yiba, wani private hospital ne mai suna al shaddad hospital aka kai meenah acan suka iske maama da mahaifiyar mijin

13 / 36