KAMAR DA WASA HAUSA NOVELS COMPLETE PDF.doc

Author :  Nil Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   23 / 36

66K to 69K   out of 106.8K words

yasamu dukka turarukan da yake amfani dasu wadanda suka kasance ba masu matsanancin karfiba saboda shi yanzu al'amuransa sai ahankali,suma su ayiyah saida yadauka musu sabulun wanka sinki biyu domin duk wanda zai siya musu abu agidan to guda biyu yake siya, daga karshe yadaukawa su Maryam gidan chocolate yanufi wurinda ake biyan kudi, yana shawo kwana yayi kicibus da maama rikeda jaririn yaronta ahannunta, sam ita bata ganeshi ba domin fuskarshi arufe take,

"Hajiya maama...."

Taso ta dauki muryar amma saita kasa gane ko tawaye, ganin bata ganeshi ba yasashi cire glass din fuskarshi da mask din da yarufe hancinsa, cikeda mamaki maama taware idanuwanta tace,

"Ya fahad idonka kenan.... Yaushe akasa?"

Dariya yayi yamika hannu yakarbi awwab dake hannunta wanda tuni har yafara wayo,

"Wallahi hajiya maama ina nan, ina babynki hudah yanzu tagirma ko?"

Dariya maama tayi,

"Tagirma tana can gida wurin adda labour..."

Jin ta ambaci labour yasashi dan runtse idonshi,

"Allah sarki... Tana lafiya ko? Yanzu nasan ta haihu ma may be...koda yake bari nayi shiru kar mijinta yasa akamani"

"A'a wai baku taba haduwa ba? Ai tana gida, yanzu batada aure..."

"Ya salam.... Sun rabu da mijinne ko kuma rasuwa yayi?"

"Wallahi rabuwa sukayi, ai kwata kwata aurenta bai wuce 3 months ba suka rabu...."

"Ikon Allah... Allah yarufa asiri,wallahi ban saniba nima da yake yanzu nakoma Kaduna da zama can nake karatu, practical yanzuma nazo yi wallahi..."

"To Allah yataimaka amma dai yakamata kaida adda labour ku tuna baya, yanada kyau akoma gidan jiya"

Dariya fahad yayi ya rausayar da kai yana kallon fuskar awwab ganinshi yake kamar bilkisu ce ta haifeshi dan tsananin kamarsu kasancewar kamarta daya da maama,

"Ai yayar takice miskila ce maama... Tanada wuyar sha'ani...."

Dariya itama mamaa din tayi sannan tace,

"To ai zaku daidaita tunda kai kanada saurin fahimta da saukin kai..."

"Haka dai kikace, Allah yazabi abinda yafi alkhairi..."

Bata kai ga amsawa ba abban hudah yakaraso domin har yagaji da jiranta acikin mota,

"Haba nidai nasan tsayawa gaisawa da wata ko wani kikayi saboda naji shirun yayi yawa..." Yafada yana mikawa fahad hannu domin yin musabaha,

"Ehh wallahi mijin adda labour nagani shine natsaya muke gaisawa..." Tafada tana dariya, murmushi fahad yayi,

"Ahh kice yayanmu ne, babban yaya yakake?"

Dariya abin yabawa fahad jin mijin mamaa na kiransa da wai Yaya bayan kuma yagirme masa ahaife sosai, karbar pampers din dake hannunta fahad yayi bayan yamikawa abban huda awwab, dama pampers kadai tazo siyawa awwab irin babban nan, wurin biyan kudi fahad yaje yahada yabiya har da nasu duk da sunata cewa yabarshi, har zai tafi maama ta dakatar dashi ta karbi number dinshi domin ita dai haka kawai take kaunar fahad shiyasa ba ason ranta aurensu ya mutuba dan dai kawai kaddara tashiga cikine.Lokacin da yakoma gida magrib tayi shiyasa saida yatsaya yayi salla sannan yashiga cikin gida yakaiwa su ayiyah abunda yasiyo musu, sunata saka masa albarka yadauko abincinsa shida Abba yafito domin abban ma yana gari tun watanni biyu da suka wuce yagama service yanzu haka yana zuwa bureau of statistics acan yake dan taba kwadago,

Yana zama gefen katifa kamar da tunanin bilkisu yazauna domin gaba daya hirar da sukayi da maama ce tafara dawowa cikin tunaninsa, sama sama yaci abincin yana daf da kammalawa yaji anfara kiran sallar isha kasancewar yanayi yasauya yanzu da wuri ake yinta, tashi yayi yafita masallaci bayan yadawo ya cire rigar sanyin dake jikinsa ya kwanta da sauran rigunan ajikinsa da safa akafarsa bargo yaja ya lulluba sannan yajawo laptop dinshi yakunna, gaba daya tunanin bilkisu ne ke neman addabar ruhinsa duk da yanata kokarin ganin hakan bai kasanceba. Duk abinda yasan idan yayi zai dauke masa hankali kar yakai ga tuna bilkisu yayi amma abin yafaskara, laptop din ya ajiye agefensa ya kunna wa'azin marigayi sheikh Albani Zaria yana saurara wanda yarage volume din sosai, daga kanshi yayi ya kalli sama kawai yana dulmiya cikin kogin tunani, ji yake kamar zai sake fadawa tafkin kaunarta akaro na biyu duk da bazai so hakanba, yasan kawai yana yaudarar kansa ne wurin kokarin hana zuciyarsa tunaninta domin abinda zuciyar take so ne, kamanninta bazasu taba gushewa daga cikin zuciyarshi ba, to tayaya ma zuciyarshi zata manta da ita alhalin silar sonta ne ya illatata har tasamu rauni daga wani bangare na jikinta, jin anturo kofa za ashigo yasashi maida hankalinsa ga kofar, yaya abba ne yashigo yana rataye da jakar laptop dinshi yana sanye cikin farin yadi,

"Amma gaskiya yau kayi over time... Duk cikin aikinne haka?" Yafada cikin sanyin murya sannan kuma ayanda yayi maganar ahankali yayita irin yadda yakeyi duk lokacin da ciwonshi yatashi hakan yasa Abba karasowa cikin faduwar gaba,

"Na dan biya ta gidan Anty asabe ne wai zan yimata register din wani abu nasu na malaman makaranta.... Wai amma lafiya kuwa?"

Murmushi fahad yayi yana gyara kwanciyarshi zuwa barin dama tayadda zai fuskanci Abba dakyau,

"Lafiya lau nake meka gani?"

"Naji maganarka ne ahankali... Amma kasha maganinka kuwa?"

"Nasha dazun nan, ka kwantar da hankalinka fa lafiya lau nake Allah"

Sai lokacin Abba yajishi yadan samu sukuni, ajiye jakarshi yayi yakalli fahad,

"Wannan sandararren abincin fa...?"

"Nakane mana..."

"Tab, ni ai yanzu ruwan zafi zansha, bari nashiga cikin gida nasa su Mariya su dafa min..."

"Su Maryam na aikatuwa hannun samarin gidannan... Idan kowa yayi aure dai sa huta suma" inji fahad,

Daukar flask din abincin abba yayi yanufi hanyar fita yana cewa,

"Ni ai ko nayi aure da daya acikinsu zan tafi..."

"Katafi da ita tazama yar aikinku ko? Ai ayiyah bazata baka ba dama dai nine..."

Baiji abinda Abba yake fada ba sakamakon karar da wayarshi tasoma yi, ganin husnah yasashi jin gabanshi yayi faduwar da har saida yasa hannu ya dafe kirjinsa,cikin sanyin murya yadauki wayar itama najin muryarshi haka yasata jin hankalinta yatashi nan tashiga tambayar ko ciwonshi ke neman tashi amma yace mata a'a saida taji sunjima suna hira baiyi wani abuba sannan hankalinta ya kwanta. Tunda suka gama waya da husnah yake cikin duniyar tunani, idanuwanshi alumshe ga wa'azi nayi cikin system dinshi amma azahirin gaskiya ba wa'azin ma yake saurara ba ahaka abba yadawo dakin yayi shirin bacci yadauki laptop din yakashe masa sannan ya kwanta saboda duk azatonshi bacci fahad din keyi bai san tunani yake tayiba tunanin bilkisu wadda yasan har gaban abada bazai taba iya raba zuciyarshi da sonta ba duk da har gobe yana jin zafin abinda tayi masa amma baya danganta hakan da laifinta ko laifinshi yabarshi amatsayin rubutacciyar kaddara wacce shida ita basu isa guje mata ba.


*_Ummi Shatu_*

BAZATA


*Littafinnan na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*


40***Sam daren ranar fahad bai samu runtsawa ba ko kadan yana ta sake sake cikin zuciyarsa ya kwance ya saka har dare yayi nisa duk da gargadin likita yana yawan fado masa zuciyarsa inda likitan ke cewa yaguji yawaita tunani haka kuma ya rinka samun isasshen bacci arana fiyeda na awa shida. Ganin dai bashida mafita sannan kuma baida guntuwar dabara yasashi fawwalawa Allah dukkan lamuransa dakyar yasamu bacci ya daukeshi wanda sanadiyyar hakan saida ya makara wurin tashi sallar asubah, sau uku Yaya Abba na tashinsa amma yana sake jan bargo balle ga uban sanyin da ake zurarawa sai bayan da aka fito daga masallaci Abba yasake tashinsa, tashi yayi yana babbata fuska kamar zaiyi kuka yanufi toilet saboda kwata kwata baya son taba ruwan sanyi a wannan lokacin sai dai hakan yazama dole. Har gari yawaye rana tafito bai tashi daga baccin da ya koma ba sama sama yake jin sallamar da Abba keyi masa bayan yashirya tsaf domin tafiya aiki, shikam sake gyara kwanciyarshi yayi yaja bargo ya lulluba amma ko minti biyu baiyi ba karar wayarshi ya tasheshi, dan guntun tsaki yaja sannan ya lalubo wayar wadda ke can karkashin pillown Abba,

"Abokina ya akayi?" Shine abinda yace bayan ya daga wayar,

"Kafita ne?" Salim yafada daga daya bangaren,

"A'a ina gida akwance...."

"To bari nazo nakarbi key din babur dinka dan Allah..."

"Sai kazo, idan kashigo ka dubashi can gaban katifa dan Allah basai ka tasheni ba...."

Daga haka yakashe wayar yasake gyara kwanciyarsa cikin sa'a bacci yafara fisgarsa amma lokacin da salim yashigo dakin saida yatashi duk da salim din bai tasheshi ba, bude kansa yayi ya leko yana lumshe idanuwa,

"A'a kaida kace kar atasheka kuma menene haka?"

Maida kansa yayi ya kwantar yana cewa,

"Dallah malam ni ka rabu dani bayan kaine ka tadani..."

Dariya salim yayi yafice daga dakin yana cemasa,

"Ka jirani inje indawo inyaso sai mu hau saman dakyau"

Koda salim yafita kasa komawa baccin yayi ganin lokaci na tafiya yasashi tashi yajanyo babbar rigar sanyinshi yasaka yafita dukkan hannayensa suna cikin rigar, cikin gida yashiga yadebo ruwan zafi yazo yayi wanka, yafito kenan yana shiryawa salim yadawo, kananan kaya yasaka yadora rigar sanyi yar madaidaiciya mai dogon hannu, zama yayi gefen katifa yana shafa mai, ahankali yace da salim,

"Abokina jiya nasamu labarin matata...."

"Wacce mata? Husnah?"

Harararshi fahad yayi sannan yayi murmushi duk a lokaci guda,

"Yaushe husnah tazama matata? Ai ba adaura mana aureba tukunna, maganar hajjaju Bilkisu nake yimaka.."

Tsaki salim yaja cikin jin haushi yace,

"Wai dan Allah meyasa kai baka da zuciya ne? Yanzu kai ko Bilkisu da kanta tadawo gareka taroki alfarmar ka mayar da ita gidanka yadace ka yarda da hakan? Bare kuma ba itace ta nemi hakanba, wai ana so dole ne? Tunda bata sonka kayi hakuri ka rungumi mai sonka amma bawai wadda bai damu dakai ba.... Harga Allah nidai am not happy da wannan madness din naka...."

Daga ido fahad yayi yana kallonsa saboda har lokacin salim din yana tsaye,

"Shikenan....." Fahad yafada yana cigaba da shafa mai akafarshi yana gamawa yajanyo safa yasaka yasan duk yadda zai kai ga yiwa salim bayani bazai taba ganewa ba saboda shi kadai yasan abinda yakeji, tabbas yasan Bilkisu bata sonshi to amma ai shi yana sonta kuma bashi ya dorawa kansa ba da shi yadorawa kansa da tuni yajima da cire sonta daga zuciyarshi ko dan yahuta.

"Ka zauna mana, bari nakarbo mana abinci muyi breakfast sai mufita gaba daya...."

Zama salim yayi yana harararshi har lokacin haushin kalaman fahad din yakeji, babu jimawa fahad yakawo musu gurasa da miya da dafaffen shayi mai kayan kamshi, ganin har suna kokarin gama cin abincin amma salim bai saki fuska ba yasa fahad langabar da kai,

"Haba abokina kayi hakuri mana ai na hakura kamar yadda kace inyi..."

"Yadai fi maka, amma matar da taso kasheka shine yanzu kake son sake tarayya da ita"

"To ai magana tawuce, nace maka na hakura"

Lab coat dinshi ya dauka da sauran abubuwan da yake bukata suka fita tareda salim, saida yafara zuwa jami'ar bayero yaga husnah sannan yawuce asibiti domin yanzu acan take karatu tana karantar Bsc nursing, shi kansa yasan abinda ya fadawa salim ba gaskiya bane domin bazai taba iya daina son Bilkisu ba shi yanzu fargabarsa ma guda daya ce kar wani yasake zuwa ya rabashi da ita ta hanyar aureta, gaba daya yinin ranar nan haka yayishi sukuku su kansu sauran daliban wadanda aka turosu tare saida suka fuskanci akwai matsala domin kamar marar lafiya haka yazama, su bash ma da suka kirashi video call saida sukayi korafin rashin kuzarinsa domin su ba kano aka turosu ba suna can Zaria, har yagama abinda zaiyi yatafi gida bashida wadataccen kuzari tun daga wannan lokaci yake jin ciwon kai sama sama. Kwana uku da haduwarshi da maama a super market takirashi suka gaisa duk da yaso share maganar Bilkisu amma yakasa saida ya tambayeta nan suka dan taba hira sukayi sallama, saving din number yayi ya ajiye wayar, yasan zaiyi wahala salim ya fahimceshi amma zaiyi iya iyawarsa wajen ganin ya fahimtar dashi, tashi yayi ya shirya yafita bai zame ko inaba sai shagonsu salim lokacin salim din na kofar shagon shida wani mai gyaran generator ganin fahad yasashi yin murmushi, ciki fahad yashiga yana dudduba turarukan dake jere reras,

"Malam me kake nema? Kasan dai babu irin turarenka anan domin kai babbar harka kakeyi mukuma na yaku bayi muke saidawa..."

Dariya fahad yayi yazauna kan kujera yana bashi hannu, musabaha sukayi fahad na cewa,

"Zaka fara sharrin nakane da ka saba? Nifa magana nazo muyi akan Bilkisu..."

Tsaki salim yaja sannan cikin fada yace,

"Wai dan Allah kai maye ne?"

Lips fahad yalashe yana murmushi,

"Mayen sonta ba, pls salim be serious... Wallahi Bilkisu bata taba yimin wani abu na cutarwa ba aduk tsawon zamanmu kawai abu daya tayi min wanda wannan ma kaddara ce da sharrin shaidan amma kai kanka shaidane munyi zaman lafiya da ita tunda kaima kana zuwa gidan kuma idanuwanka suna gane maka..... Wallahi salim ina sonta narasa ya zanyi...."

Ajiyar zuciya salim ya sauke sannan ya kalleshi,

"Nifa har yanzu banji kafadi abinda yarabaku ba nikuma shi nake son sani...."

"Salim wannan kuma ai sirrine, amma karka dora laifin akanta ka dorashi akaina... Sannan mubarshi azuwan kaddara"

"Shikenan Allah ya zabi abinda yafi alkhairi"

"Yawwa abokina, amin, dan Allah kazama cikin shiri domin wannan karon dakai za ayi yakin sannan katayani da addu'a.... Bari nahaura sama"

"Ashirye nake ai" salim yafada yana dariya, fita fahad yayi yahaura sama yana murmushi,

"Salim kenan...." Yafada acikin zuciyarshi lokacin da yake kokarin shiga cikin shagonsu. Tsawon sati biyu yadauka yana ririta maganar aranshi amma yarasa ta yadda zai iya fadawa su ayiyah ko baba, shidai yasan yayi addu'a a tsawon sati biyun nan sosai kuma har yau baiji canjiba gameda soyayyar Bilkisu sai dai abinda ke yawan fadar masa da gaba shine watanni biyu kenan da su baba suka kai musu kudin aure shida ya Abba, shi fahad gidan kanin Baban husnah dake Kaduna aka kai masa shikuma ya Abba Nusaiba kanwar salim, duk da haka baya jin zai iya hakura da auren Bilkisu koda kuwa mata uku yakaiwa kudin aure mutukar yanada gurbin da zai sakata, kullum da maganar yake kwana yana tashi amma idan yaje cikin gida sai yakasa sanar dasu amma yau ya kuduri aniyar fada ko yasamu yaji sauki acikin ranshi, mamuh yasamu tsakar gida tana daka fura ita kuma ayiya na dafa kindirmo, zama yayi kan kujerar mamuh yar tsugunno,

"Ayiyah dan Allah wani taimako nake son kuyi min.."

Dukkaninsu dakatawa sukayi daga abinda sukeyi suna sauraronsa, dakyar yasamu karfin yin magana,

"So nake ku sanarwa da baba yaje gidansu Bilkisu tsohuwar matata ta ya tambayar min izinin aurenta... Wai tunda jimawa suka rabu da tsohon mijinta nikuma wallahi har yanzu.... Ina.... Sonta..." Kai idan kaji yadda yakarasa maganar sai yabaka dariya amma su ayiyah basuyiba domin sun dake, nan kowa taci gaba da abinda takeyi babu wacce ta tanka masa har yakaraci zamansa yatashi yafita bai kara yimusu maganar ba suma basuce masa komai ba haka shima baba baice masa uffan ba shiyasa yafara tunanin kila su ayiyah basu sanar masa ba, tun yana daurewa har yasamu baba dakansa yayi kokarin yimasa maganar amma sai baba ya katseshi ta hanyar cemasa iyayensa mata sun yimasa maganar, nan mamaki ya ishi fahad, jin wai ashe baba yasani amma yayi shiru, shi dinma shirun yaci gaba dayi yana addu'a.

Bayan sati daya da faruwar lamarin ranar asabar yana kwance dasafe yana bacci kasancewar babu aiki Abba yashigo yana tashinsa, yana bude ido abba yace masa,

"Baba yace katashi kashirya zamu rakashi anguwa anjima..."

Duk haushi yaji ya kamashi haka kawai yana baccinsa mai dadi Abba yakatse masa saida yagama nuku nuku da kunbiya kunbiyarshi sannan yatashi yayi wanka ganin irin shigar da Abba yayi harda babbar riga yasashi shima kwaikwayon shigar abban ko ba komai babbar rigar zatayi masa maganin sanyi, kasancewar sanyine basubar gidaba sai bayan azahar su shidane acikin motar da baban salim da baba sai salim din da fahad gaban motar kuma ya baffane ke driving ya abba na zaune gefenshi,shi dai fahad nata son ya tambayi inda zasuje amma babu dama domin da ya tambayi salim cikin rada ma cewa yayi shima wallahi bai saniba, tafiya sukayi mai nisa shidai sai yaga kamar yasan garin amma kuma gaskiya yakasa tunowa sosai yadda yakamata. Karfe uku da wani abu suka karasa babbar fada wacce ke girke tsakiyar garin sai lokacin fahad yatuna garin ashe garko ne garinsu Bilkisu domin aurensu nafarko anan aka daurashi,

"To amma me mukazo yi nan kuma? Ko rasuwa akayi musu?"

Wannan tambayar ita yake ta yiwa kansa har suka shiga ciki inda jama'a ta dan taru amma kuma mutanen basuda wani yawa sosai, daga can baya suka zauna shida salim sukuma su baba suka wuce can gaba, tsawon mintuna goma aka dauka ana gaishe gaishe kafin daga bisani aka fara daurin aure, sudai su fahad basa jiyo abinda ake fada bayan kamar mintuna biyar aka gama daura aurenshi da Bilkisu batareda yasaniba akan sadaki naira dubu talatin aka daura auren wanda baba shine yabada sadakin, kiransu ya Abba yazo yayi nan suka karasa gaban manya shidai yaga anata nunashi amma bai san daliliba saida suka fito bayan sun gama gaishe da manyan sannan yake tambayar Abba dalilin nunashin da aka yitayi aciki,

"Ango ake tambaya shine aka nunaka saboda wasu sun zaci wai nine..."

"Ango kuma? Wai auren wa mukazo ne?"

"Aurenka da Bilkisu mana...,congratulations lil bro...."

Jin abinda yace yana dafa kafadarsa yadaure masa kai shida salim, saida sukayi sallar la'asar aka fito musu da abinci sannan sukayi haramar tafiya, goro da alawa da dabino aka kawo musu fal aka saka abayan mota,suna kokarin shiga cikin mota su baba suka karaso fuskarsu dauke da fara'a hannunsa cikin na abbansu Bilkisu suna sake yin doguwar musabaha......


*_Ummi Shatu_*

*FARIN GANI*

*Wannan littafin na siyarwane me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



41***Shi dai fahad har suka bar cikin garin garko sukayi tafiya mai nisa bai bar mamakin abinda ke faruwa ba jinsa yake kamar acikin mafarki gaba daya lamarin yadaure masa kai, yana so yayi tambaya amma yana jin kunyar kar su baba suga rashin kunyarsa, shiru yayi kawai ya lumshe idanuwansa yana sauraron hirar su baba wadda mafi yawanta akan irin halin dattako da karamcin abbansu Bilkisu ne, godewa Allah yake tayi acikin zuciyarsa domin yasan shine yayi masa wannan gatan yasake aura masa Bilkisu akaro na biyu. Daf da lokacin sallar magriba suka shiga cikin garin kano, murnarsa bazata taba kwatantuwa ba a wannan lokaci, ko cikin gida bai shiga ba yawuce dakinsu yabar ya Abba da salim da aikin shigar da kayan daurin aure cikin gida, wanka yafara yi da ruwan sanyi domin yanzu ko sanyinma sai yaji yadaina ji shifa yanzu jinsa yakeyi tamkar anzare masa

23 / 36