KAMAR DA WASA HAUSA NOVELS COMPLETE PDF.doc

Author :  Nil Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   15 / 36

42K to 45K   out of 106.8K words

musamman ma daga mararsa zuwa babban yatsunshi na kafa,

Jin kowa nayi masa sallama suna tafiya yayi saurin yiwa salim alama da ya kira bilkisu,

"Hajjaju oga fa yana magana"

Murmushi tayi ta koma da baya tana cewa,

"Lallai salim kaima din hajjajun zakace"

Tana zuwa yayi mata alama da ta sunkuyo taji, duk atunaninta magana zaiyi mata akunne amma tana mika fuskarta saitin tashi taji yabata hot kiss a kumatunta mikewa tayi tana harararsa shima harararta yayi murmushi ne ya subuce mata batare da ta shirya ba, hannunta ya riko yana yimata alama da wai shima tayi kissing din kumatunshi,

"Dan Allah kaga ni sakar min hannu gasu can ni kadai suke jira kar kasa azargi ko wani abu mukey...."

Murmushin karfin hali taga yayi kafin yagirgiza Mata kai alamun bazai sakar mata hannun ba, hannunshi tayiwa kiss tana kokarin fita abba yashigo ganinsu ahaka yasashi saurin komawa da baya, hararar fahad tayi,

"Kagani ko...."

Bata saurareshi ba tafice daga dakin, binta da kallo yayi yana yimata dariya acikin zuciyarshi, dama ita kadai ake jira tana zuwa suka tafi,itada maryam da mariya aka sauke agidanta tana shiga wanka tafara yi sannan tayi sallar ishah domin batayi ba a asibitin acikin wannan daren takira maama da ammah duk ta sanar dasu rashin lafiyar fahad da asibitin dayake kwance ahalin yanzu sannan takira khulsum wacce har tafara bacci itama tasanar da ita, dayake jiya batayi isasshen bacciba shiyasa yau tunda ta kwanta bata tashiba sai da asubah duk da hakama ta makara sallah domin har masallatai sun jima da idarwa......


*Littafin kamar da wasa na siyarwa ne yar uwa idan har kinada bukata ki siya ki karanta domin yana dauke da dunbin darrusa na rayuwar da muke ciki yau, ka karanta halak dinka yafiye maka alkhairi akan karanta hakkin wani.*



*_Ummi Shatu_*


? *HASKE WRITERS ASSO.*


*KAMAR DA WASA...!*



_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*25*


***Kitchen tashiga bayan ta idar da salla sukuma su mariya suna kokarin gyara mata gidan, saida ta shirya lafiyayyen abincinta tazuba a flask wanda zata kai asibiti sannan ta zubawa su mariya suka ci daga nan tabasu kudin napep saboda sai sun koma gida sannan zasu shirya su tafi makaranta danma dai sunyi wanka agidanta da sunje gida uniform kawai zasu saka, bedroom tashiga bayan ta sallami su maryam sun tafi, tana kokarin daura towel idonta yakai kan wayar fahad dake ajiye saman bedside drewar tana karar neman agaji, koda taje gaban wayar sunan husnah tagani ajiki nan wayar takatse wani kiran yasake shigowa, ko kadan bataji tana sha'awar daga wayarba har tayi tagama sai lokacin ta dauka ta jona masa a charge kasancewar akwai wuta. Wanka tashiga tayi tafito ta kintsa adan hanzarce sannan tayi breakfast kafin ta hada komai wanda zata tafi dashi tarufe gidan tatafi, shatar napep ta dauka yakaita har asibitin lokacin karfe bakwai da wurin rabi,iya ya abba ne kadai awurin da alama babu wanda yazo tunda yanzu garin yawaye, saida suka gaisa ta tambayi yamai jiki sannan tashiga ciki, idonshi akan kofa shiyasa tana shigowa idanuwansu sukayi arangama da juna, murmushi taga ya sakar mata kasalalle yana kwance rigingine kanshi tallafe bisa hannunshi na dama,

Har gaban gadon takarasa zata zauna, hannu yamika mata yakamo nata, zama tayi tana kokarin ajiye handbag dinta bayan ta dire kayan da tazo dashi. Kallonta yake tamkar yau yafara ganinta domin ba karamin haduwa yau dinnan tayiba, leshi ne ajikinta dark pink anyi mata gown tasha lafaya itama pink duk ta lullube jikinta, juyawa tayi ta kalleshi,

"Sannu yajikin?"

Daga mata kai yayi yana matsa mata yatsunta bata kai ga sake yin wata maganar ba Abba yashigo dauke da brush da toothpaste,

"Gaskiya mijinki jinyarsa akwai takurawa.... Ni yanzu ma gida zanje anjima zan dawo"

Murmushi bilkisu tayi ta dan karkatar da kai tana kallon fahad wanda idanuwanshi ke lumshe,

"Meya faru yayanmu?"

"Shifa idan yana ciwo nafarko bazaiyi bacciba sannan na biyu bazai ci abincin ba na uku bazai sha magani ba sannan komai sai anyi masa kamar wani jariri, yanzu gashi yanace sai ankawo masa brush kuma bari kigani ko yayi brush din bafa cin komai zaiyi ba kuma Dr yace zai dan iya cin abinci kadan kadan bawai dayawa ba"

"Sannu da kokari, Allah yabada lada....,ayi mana afuwa amma"

Bude idanuwa fahad yayi ya kalleta yana jin wani irin sabon sonta yana shigarshi,

"Yanzu dai gashi sai kusan yanda zakuyi kiyi masa brush din"

"A'a babban yaya ai sai ka taimaka min"

Da taimakonshi suka samu yayi brush din sannan ta zubawa abba abinci yafita waje yaci, Dr ne yashigo shida wasu nurse maza guda biyu yaduba jikin fahad sannan yafita yabar nurse din domin su gogewa fahad wurin da aka yankashi, ai ana saka audugar da aka tsoma cikin ruwan spirit ya runtse idanuwansa tareda sake damke hannun bilkisu tun nurse din Suna tsokanarsa sun zaci shagwaba ce har kowa ya fahimci dagaske yake domin kuka yasaka musu saida aka gama suka fita Abba yashigo tsayawa yayi yana kallon fahad wanda har lokacin bai daina kukanba,

"Kai wai menene amfanin kukan ne? Dallah malam tashi kaci abinci saboda ni tafiya zanyi"

Ko motsi baiyi ba bare asaka ran zai yarda yaci abincin, shi dama idan lafiyarsa kalau yana son abinci sosai amma idan bashida lafiya to shida abinci sai ahankali, gyara zama bilkisu tayi tafara lallashinshi,

Gefen lifayarta tasaka tafara goge masa fuskarshi, kanshi tashiga shafawa sannan ahankali ta sunkuya daidai kunnenshi tafara yimasa rada,

"Kaifa yanzu ba yaro bane kagirma, kayi hakuri.... Yi shiru katashi kaci abinci, dan kadan zan baka dama kai na dafowa..."

Ahankali ahankali yasoma rage kukan nashi har yadaina gaba daya sai ajiyar zuciya da yake ajiyewa, mikewa tayi da niyyar yiwa ya abba magana amma sai taga wayam wato yafice yabasu wuri kenan, tea ta hada masa mai kauri bai kai rabin cup ba ta taimaka masa ya dan tashi yanata cije lips, yana hawaye yana shan tea din wai ahakanma dan itace amma da wanine da sai ansha fama dashi kafin yasha, wainar kwai guda daya da dankali guda biyar ta sake bashi yana ci yana yamutsa fuska yana gamawa ta mayar dashi ya kwanta, wayarshi ta ciro ajakarta tabashi yakarba ya ajiye agefen pillow din da yake kai, su ayiyah ne suka shigo harda baba lifayarta taja tarufe fuskarta kadan tasauka kasa ta gaidasu bayan sun gaisa tafice waje ta zauna bisa bencin dake kofar dakin anan ammah ta sameta itada Rabi mai aikinta, tare suka???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? shiga ammah ta dubashi sannan tafito itada rabi suka bar ammah acan wurunsu ayiyah. Sunata hirarsu da Rabi har khulsum tazo itama tashiga ta dubashi tafito tatafi saboda wurin aiki zata tafi. Wurin misalin karfe 10 saiga maama dasu meenah abban hudah yakawo su anan suka shantake kamar ba dubiya suka zo ba domin anan ammah tatafi tabarsu,kowaccensu rikeda yarta har su anty fauziyya sukazo suma dauke da girke girken da suka iyo, shikuwa marar lafiyar yana daki kwance shida salim suna hira amma dayake jiya baiyi baccin kirki ba da daddare yanzun sai hamma yake danyi.

Bayan anyi sallar azahar suna gama cin abinci salim yaleko yakira bilkisu tashi tayi batare da ta bude warmer din da rabi takawo ba yanzu, dakin tashiga fahad na baje sai faman lumshe idanuwa yake, hannu yamika mata yajata gefenshi,

"Zo ki tayani baccin rana luv"

Ita abinma maimakon yabata haushi kunya yabata saboda ga abokinshi zaune kan gadon marassa lafiyar dake makotaka da na fahad amma babu patient akai, maganarsa tasake juyowa ahankali domin tunda aka kawoshi asibitin ma sai yanzu ne sukaji yayi magana amma da ko me yarike maganar oho,

"Zo muyi baccin rana hajjaju"

Dan satar kallon wurinda salim yake tayi amma sai taga shi hankalinsa ma ba awurinsu yakeba domin yana ga kan wayar fahad dake hannunsa, jin kunyar gwasaleshi tayi agaban abokinshi domin tasan babu wanda yasan irin zaman da sukeyi kusan kowa yazaci zaman aure sukeyi na hakika, tana can duniyar tunani ya hardota da hannunshi zuwa kan kafadarshi bai tsaya ananba yashiga shafar bayanta kamar wata jaririya, lumshe idanuwa tayi tai shiru kamar mai yin baccin da gaske shi dai mutumin abu biyune suka taru suka hadar masa lokaci guda ga ciwo ga kuma wani abu dake sauka asassan jikinsa gaba daya wanda yafi kamada kasala kasala, gajiya gajiya, ji yayi bazai iya jure wannan kamshin nata dake barazanar tarwatsa tunaninsa ba, bakinshi yakai kan goshinta yabata kiss mai sanyi sannan ya soma kokarin lulluba da lifayar jikinta anan ne kuma taso bashi matsala amma sai ya shagwabe fuska,

"Allah sanyi nakeji fa..."

"To akawo maka bargo?"

Girgiza kai yayi harda makale kafada,

"Ni naki nakeso, dan wannan mayafin naki zai isheni.."

Yar kokawa sukayi kafin ta farga yashige cikin lifayar tata ya kwakuma akirjinta amma fa duk abinnan dake faruwa bai motsa kafafunsa ba iyakacin hannayensa da kanshi ne yake motsawa, salim dake zaune yana jin duk abinda ke faruwa tunda ya kallesu sau daya bai sake iya kallonsu ba sai bayama yajuya musu domin sunyi mutukar bashi kunya. Mintuna kadan taji jikinsa ya dan saki alamar yayi bacci da dabara da komai tasamu ta zare jikinta ta tashi tafita bayan ta gyara masa kwanciyarshi yadda bazai takuraba, tana komawa wurinsu maama sai kuma duk ta tsargu da kus kus din da sukeyi musamman ma da ta kama Hindu na gulmarta da ido itada meenah,

"Adda labour ya mai jiki?" Inji maama, banza tayi da ita ta karbi Minal dake hannun hindu ta rike tana lakutar kumatun yarinyar,

Duk dan bikin da suke tayi tana jinsu bata tanka ba daga karshe ta jawo warmer din da ammah ta aiko musu da ita tabude domin bata san ko wanne irin kalar abinci bane, farfesun koda ne cikin warmer din sai tashin kamshi yake wannan dalilin ne yasata niyyar baiwa fahad yaci domin naman ya dahu ligif zai iya ci,

"Maman hudah zuba muku kuci ni ba ci zanyiba sai dai shi ku bar masa"

Jin irin dariyar da sukayi yasata tashi gaba daya tabar musu wurin kafadarta dauke da Minal, kamar da wasa take bin hanyar da tagani wacce zata kaika sassa daban daban dake cikin asibitin, aranta sai yaba tsari da haduwar asibitin take yi wani daki tawuce wanda shine na karshe ajerin dakunan dake bangaren, ahankali yamaida kofar yarufe yafito yana rikeda mukullin motarsa yana dan sosa kunnenshi na dama dashi, wani kamshine ya mamaye wurin, daf da zata sha wata kwana wacce zata kaika pharmacy wayarta ta subuce ta fadi kasan tiles din dake shimfide awurin kadan yarage yataka wayar tata saboda irin garawar da wayar tayi ita kadai amma sai Allah ya takaita, sunkuyawa yayi yadauko wayar yamika mata daidai lokacin da ta jiyo hannunta daya ta mika masa domin dayan tarike Minal dashi, tun daga kafarshi tasoma kallonshi, farin takalmine akafar tashi yana sanye da shadda ruwan kasa da hula sai farin glass dake idonshi, kamar hadin baki idanuwansu suka sarke cikin na juna, wata faduwar gabace mai girma ta saukar mata wacce tayi sanadiyyar sakin Minal dake hannunta sai shine yayi azamar tare minal din ya rungume yana yiwa bilkisu wani irin kallo mai dauke da alamomin tambayoyi daban daban, cikin rawar jiki da rawar baki ta furta,

"Hamood...."

Shi dinma cikeda rawar baki yace,

"Bilkisu.... Kece ko kuwa mafarki nake?


*Book dinnan na kudine idan kina bukata kibiya saiki karanta.*



*_Ummi Shatu_*

? *HASKE WRITERS ASSO.*



*KAMAR DA WASA.....!*


*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*



*26&27*


***Daga ita harshi kasa sake furta koda kalma daya sukayi sai kallon juna da suketa faman yi kamar yaune suka soma ganin juna,

"Bilkisu kin sakani acikin mutukar damuwa, Allah yasa ba aure kikayi har kika haihu ba..."

"Haba hamood har yaushe zanyi aure inhaihu batare da saninka ba, najiraka najiraka har nagaji, na nemeka duk inda nasan zan iya samunka amma nagaza daga karshe dole tasa na fidda wani mijin nayi au..."

Arazane ya kalleta har yana cin tuntuben matsawa kusa da ita,

"Wai kina nufin kinyi aure? Wannan shine abinda bazan taba iya jurewa ba bilkisu, rashinki agareni babbar matsala ce wadda bata da magani... Bazan taba iya jurewa ba"

"Hamood nikaina wannan auren nayi shine kawai arashinka amma tunda...."

"Bilkisu karki cemin komai, yazama dole ki dawo gareni muje mu shimfida daddadar rayuwar da muka jima muna tsarawa kanmu, yazama dole mu cika burinmu da alkawarin da muka jima muna yiwa juna..... Dole ki kashe aurenki kidawo gareni domin kece farin cikina..."

Duk da ba acikin nutsuwarta takeba domin jikinta inbanda rawa babu abinda yakeyi amma hakan bai hanata murmusawa ba,

"Hamood wallahi kaine burina, kaine mijin da nadade ina yiwa kaina mafarkin samu dan haka yanzu lokaci yayi, kai dai kawai kabani dan lokaci kankani zanyi handling komai...."

"Bilkisu sai nake ganin kamar idan kika tafi yanzu bazan sake ganinki ba..."

"Karka damu hamood ka kwantar da hankalinka ni takace kai nawane kamar yadda muka dade muna yiwa juna fata, bani Minal intafi saboda kar wani acikin sisters dina yazo yaganmu"

"To ai sai kibani number dinki saboda ta wannan hanyar ne kadai zan rinka sanin halin da kike ciki..."

Batayi musuba ta rubuta masa awayarshi tabashi takarbi Minal, yana tafe yana waiwayenta itama haka har suka bacewa juna tana shawo kwana sukayi kicibus da meenah wacce tataho nemanta domin zasu tafi gida abban minal yazo daukarsu,

"Adda maigado ina kika shigane mukayita dubaki shiru gashi wayarki taki shiga?"

Murmushin dole ta kakalo takalli meenah,

"Wayarce tafadi wlhi inajin sim din yagoce..."

Jerawa sukayi suka tafi meenah sai hira take yimata amma ina hankalinta ita gaba daya ba awurin yakeba, sam yanzu bata cikin nutsuwarta, ganin hamood yatada mata tsohuwar soyayyar da ta jima tanayi masa domin yanzu ji take zata iya yin komai dan ta kashe kaddararren auren nan na fahad taje ta auri hamood dinta,

Sama sama suka gaisa da baban minal sukayi sallama da kannen nata suka tafi suna tafiya tanemi wuri ita kadai ta zauna tana tunanin menene abinyi? Anty fauzy ce tataho wurinta tana murmushi,

"Hajjaju to ga mijinki can yatashi yana ta yiwa mutane daru akan shan magani sai kije kibashi..."

Mikewa tayi zuciyarta tana suya domin sam fahad bai dace da itaba hamood shine wanda yadace yazama mijinta domin irin mai shekarunsa takeso 35 a matsayinta na yar shekara 30 ba wai fahad ba dan 25,zuciyarta babu dadi tashiga dakin da yake duk yabi ya ruda mutane, ganinta yasa su ayiyah fita aka barsu su biyu sai salim na cikon uku, zama tayi gefen gadon ta dauki maganin ta mika masa baiyi musuba yakarba yana babbata fuska.

Tamkar zaiyi kuka haka yake taune maganin yana korawa da ruwa har ya shanye su tass komawa yayi yamaida kansa bisa pillow ya kwantar yana hararar salim wanda ke zaune yana kallonsu,

"Baby zansha sweet bakina daci...."

Batace masa komai ba amma yaga amsar maganarshi acikin idanuwanta,sake bata rai tayi tajanyo handbag dinta ta bude ta ciro yar karamar milk chocolate tabashi. Tunda magrib takawo jiki tace zata tafi gida babbata rai fahad yashiga yi domin shi idan ta son ranshi za abi abar bilkisu ta kwana dashi ba ya Abba ba,yauma kamar jiya dasu mariya aka hadata dan su bita su tayata kwana duk da ita bata so hakanba domin tana son sakewa tayi waya da hamood sosai adaren yau,

Sam yau batayi garajen hada daki dasu maryam ba domin a falo tayi shimfidarta sukuma tabarsu acikin bedroom, zama tayi ta harde kafafuwanta kan katifar da fahad yake kwana, tana sanye da rigar bacci fara tas mai santsi iya gwiwa sai bakar hula akanta, daman jiran kiranshi takeyi shiyasa kiran na shigowa tayi murmushi ta dauka tana kwantar da murya saboda dare ne,

"My sweetheart yakike? Yanzu dan Allah menene abinyi? Ni nafi son kiyi gaggawar dawowa gareni"

Murmushin jin dadi tayi,

"Karka damu hamood ka kwantar da hankalinka very soon zan zama mallakinka"

"Are u sure?"

"Am 100% sure hamood...."

Dariya sukayi atare lokaci guda, sun jima sun bata lokaci sosai suna shan hira domin har wurin karfe 1 nadare suka kai yana sanar da ita abubuwan da suka faffaru saida bacci ya takurawa bilkisu sannan sukayi sallama.

Washe gari da safe bayan ta sallami su mariya sun tafi sake kwanciyarta tayi har saida hamood yakirata sannan tatashi, bayan sun gama waya tashiga wanka tashirya sannan tatafi asibiti amma yau bataje da wuriba kamar jiya shi dai fahad yana kwance ya kosa yaga zuwanta, dauke da basket din abinci ta shiga dakin tasha yaluwar Arabian gown mai manyan stones ajiki tayane kanta da wani mayafi mai kauri milk colour, tunda suka gaisa da ya Abba bata sake furta komai ba, fahad sai kallonta yake taki kulashi wannan dalilinne yasashi niyyar jan magana, shagwabe fuska yayi,

"Baby inata kiranki ban sameki ba, dama zan fada mikine ki taho min da kayana gashi yanzu sai na ya abba nasa saboda dazu ya gyara min jikina..."

Jijjiga kai tayi tana kallon wayarta,

"May be network problem ne"

"To kibani abinci inci saboda zan sha magani"

Dariya Abba yayi yana tattara kayansa zai fita,

"Yaro yasamu sauyin yanayi wato yanzu da kanka ma kake cewa abaka magani kasha ah lallai angaida bilkisu..."

Murmushin yake tayi tatashi ta zuba masa potatoes plan din da ta iyo sannan ta hada masa tea dan kadan, yauma kamar jiya da taimakonta yaci abincin sannan yasha magani, haka tawuni acikin wani hali, hali na rashin walwala domin ita bata ki a sallami fahad ayauba su koma gida inyaso ayita takare, yauma magrib nayi ta tafi gida itada su maryam, lokacin bacci nayi suka sha hirarsu da hamood.

Gaba daya fahad yakasa gane kanta a yan kwanakin nan ada tana sakar masa fuska suyi wasa da dariya wani lokacin har tsokanarta yakeyi amma yanzu tadaina sai shan kunu da daure fuska, ita kuma anata bangaren kawai so take yawarke a sallameshi suje gida ayi wacce za ayi domin hamood yace baya son bikinsu ya dauki dogon lokaci yafiso ayishi kwana kusa, kullum sai sunyi waya dashi fiyeda sau uku wani lokacin ne ma idan tana cikin mutane bata yarda ta dauka. Yau kam tun kafin taje asibitin husna taje duba fahad itada kawayenta domin kullum idan taje shagonsu bata samunshi sai ace baizo ba daga karshe dai su hamza suka fada mata fahad baida lafiya, wahala sosai tayi masa kamar ba student ba domin harda girki da fruits ta siya ta kai masa, suna tafiya bilkisu na zuwa shiyasa basu haduba tadai

15 / 36