KAMAR DA WASA HAUSA NOVELS COMPLETE PDF.doc

Author :  Nil Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   16 / 36

45K to 48K   out of 106.8K words

ga kayan dubiya amma bata san waye yakawo ba.

Satin fahad biyu a asibiti aka sallameshi domin jiki yayi kyau kuma babu laifi ya murmure sosai kamar ba majinyaci ba, tunda suka koma gida ya fuskanci akwai matsala domin bilkisu ta kafa ta tsare, duk da dai batace masa komai ba amma daure fuskar da take tayi ya isa yasanar dashi akwai matsala shi dai baice mata komai ba har dare, yana zaune gaban dressing mirror bayan yafito daga wanka da kayan bacci ajikinshi riga armless da wando iya cinya tashigo dakin, zama tayi gefen gado tana kallonshi so take tayi masa maganar amma bata san ta inda yadace tafara ba dole sai hakura tayi domin ta sake dan bashi lokaci. Bayan kwana biyu tadawo daga aiki yana kwance falo tawuce bedroom yau dai ta daura aniyar sanar dashi inyaso komai ta fanjama fanjam domin hamood ya matsa da son ganin fitowarta, fitowa tasake yi daga cikin bedroom tazo ta zauna tana fuskantarsa,

"Fahad.... Dan Allah inaso zamuyi magana..."

Kai yadaga mata bayan ya tattaro gaba daya hankalinsa gareta,

"So nake ka sawwake min..."

Kallonta yayi cikin rashin fahimta,

"Kamar ya fa...?"

"Ina nufin so nake ka sakeni...."

Tashi zaune yayi babu shiri yana kallonta,

"In sakeki? Laifin me kikayi min da zan sakeki? Anya kuwa kin san abinda kike fada?"

"Nasan abinda nake fada mana, auren ne bana bukatarsa yanzu shiyasa nace ka sawwake min"

Murmushi taga yayi sannan yamike yana mika,

"Allah ya kyauta, ni wallahi da zaki taimaka ma da kin hau kaina kinyi birgima sosai ko zan samu gajiyar dake jikin nan nawa marar dalili ta baje amma nasan bayi zakiyi ba, bari kawai natafi filin ball naje na basar acan...."

Daga haka yawuce bedroom yayi shirin ball yafito yana sanye da kayan ball ajikinsa jajaye na club din Barcelona harda safa hannunsa rikeda wayarshi da bakaken combos dinshi, wani kulli ne taji ya tokare makoshinta wato ma mahaukaciya ya dauketa ko yaya da har zai tashi yabarta without saying anything, babu bata lokaci ta mike taje gabanshi,

"Malam ji mana... Bakaji abinda nace maka bane?"

Juyowa yayi ya kafeta da ido bayan ya ajiye takalmanshi akasa,

"To mekikeso nace miki baby? Banida abinda zance shiyasa kikaji nayi shiru"

"Fahad wallahi tun muna shaida juna ka sakeni domin bazan iya zaman aure dakai ba, kalleka fa ka kalleni ai kaima kasan ni ba mate din aurenka bace dan haka kawai ka sakeni tun kafin duniya ta jimu..."

"To wai dan Allah laifin me kikayi min da zakice sai na sakeki, ko kuma ni laifin me nayi miki?"

"Babu abinda kayi min kawai bana bukatar auren ne ahalin yanzu"

"Hmmm bilkisu kenan karfa kiga kin girmeni kirinka yimin kallon sakarai ko marar wayo, ashe kecema mijin mutukar zan rinka aiki da umarninki...."

Sunkuyawa yayi zai dauki takalmanshi ta kamo rigarshi yadago yana kallonta,

"Wallahi fahad sai ka sakeni, akan me zaka dage sai kayi rayuwar aure dani..."

"A'a dan Allah basai kin yimin sharri ba,yaushe nataba nemanki? Na taba cewa sai na kusanceki?"

"Ni ba wannan maganar nake yimaka ba, maganar saki nake yimaka, ka sakeni kawai...."

Murmushi yayi sannan yadauki takalminsa yana kallonta,

"Zan tafi....me zan samu? Kiss ko hugging?"

Wani takaicine taji ya lullubeta ga bakin ciki da yake taso mata a makoshinta,

"Wai kai wasa ka dauki maganar nan ne?"

Wani sakaran kallo yayi mata sannan ya maida kallonsa ga wayarshi wadda ke vibrating alamar kira yashigo,

"To idan ba wasa ba menene? Ai wannan maganganun naki basuda maraba da wasan kwaikwayo hajjaju.... Ni natafi sai na dawo"

Tsabar bakin ciki rasa abinda zatai tayi,kasa koda kwakkwaran motsi tayi tana ji tana kallonsa yasaka kai yafice daga cikin falon yana amsa wayar da akayi masa,

"Hello anty fauziyya..."

"Auta yajikin naka?" Tafada daga daya bangaren,

"Anty nasamu sauki ni yanzu hakama filin ball zanje"

"Kai, kar kaje fa kajawa kanka matsala"

"Ahh babu komai Anty wallahi ras nake jina"

Kasa motsawa tayi daga wurin taci gaba da tsaiwa kamar wadda aka dasa har saida kafafuwanta suka fara nuna alamar gajiyawa da tsaiwar da take nan tazame ta zauna kamar abin shiri sai kuma kuka ya balle mata tashiga rusashi kamar wata yarinyar goye domin harta manta rabonta da kuka irin wannan.

Abangaren fahad kuwa sosai abinda yafaru tsakaninsa da bilkisu ya tsaya masa arai,ko kadan hakan baiyi masa dadiba amma haka dai yadaure ya yakice damuwar yashiga sha'aninsa duk da dai abun yana fado masa arai lokaci zuwa lokaci. Saida yabuga ball sosai sannan yafita yaje yanemi wuri ya zauna dan yahuta, shifa yanzu matsalar ma idan yakoma gida bai san ayanayin da zaije ya iske bilkisu ba wannan abu yanzu shine babbar damuwarsa.

Tunda bilkisu tayi wannan zaman yan borin tana rusa kuka bata dainaba saida kiran hamood yashigo cikin wayarta da rarrafe taje ta dauko wayar tadaga muryarta har ta dishe dan tsabar kuka,

"Sweetheart yasakeki...?"

Cikin dasasshiyar muryarta ta amsa amsa,

"Wallahi hamood yaki ya sakeni, nayi nayi amma abin ya faskara..."

"Don't tell me this sweetheart, you should insist akan dole sai ya sakeki, ki matsa masa sosai,bana son ki kara koda 1 week agidansa...."

Daga kai tayi tamkar yana kallonta,

"Yanzu baya nan yafita amma da zarar yadawo zan dora daga inda natsaya..."

"Yawwa one love..."

Kit takashe wayar tana jin sabon kuka yana taho mata,ahaka fahad yadawo ya isketa zaune dirsham kan rug tana hawaye,

"Hajjaju..... Wai dan Allah menene matsalar ne? Meke faruwa?"

Yace da ita yana kokarin tsugunnawa agabanta, jajayen idanuwanta wadanda suka kankance ta dago tana zabga masa harara,

"Fahad wallahi idan har baka rabu daniba sai kayi nadama tareda da nasani mai tarin yawa...."

"Ni wallahi bana son inji irin wadannan kalmomin suna fitowa daga bakinki"

Hayayyako masa tayi da masifa da tashin hankali tuni yatashi yawuce bedroom domin har anfara kiran sallar magrib, wanka yayi yafito yashirya yasaka jeans da jallabiya milk colour yafita bayan yasha turare tana zaune inda yabarta tana ta kuka,

"Ni narasa maganin abinda kukan nan zaiyi miki bilkisu.... Dan girman Allah ki barwa Allah lamarinsa ki sanyawa zuciyarki ruwan sanyi..."

Mikewa tayi tana hawaye tana tunkararsa,

"Wallahi fahad ko duniya zata tashi bazan cigaba da zama da kai ba domin ba kaine farin cikina ba, farin cikina yana wurin waninka dan haka yazama tilas ka sawwake min..."

Bai jira takaraso ba yafice da sauri yabar gidan, masallaci yatafi daga can yawuce wurinsu salim wato majalissarsu ta shan shayi, ita kuwa bilkisu tana nan zaune dakyar tatashi tayi salla bayan tayi salla hamood yasake kiranta yana kara jaddada mata maganar neman sakinta awurin fahad.

Gaba daya fahad bashida nutsuwa domin wasa wasa damuwar da bilkisu ke ciki tafara tasiri akansa saboda yau kimanin kwana biyar kenan suna cikin rashin kwanciyar hankali tun ranar da aka sallamoshi daga asibiti rabonshi da cikakkiyar nutsuwa domin bilkisu tasashi agaba da masifa da tijara tun abin baya damunsa har yafara damunsa,

Dama tunda haka tafara faruwa tadaina kwana acikin daki sai falo yanzu sai shine ke kwanciya aciki sannan tadaina girki kwata kwata sai dai tahada tea tasha shiyasa kwana biyar kacal duk tafita hayyacinta fahad yayi lallashin yayi ban bakin amma abin yaci tura. Yau ma kamar kullum yana daki yana shiryawa zai fita yajiyota tana yin waya afalo,saurarawa yayi dakyau nan yaji abinda take fada,

"Hamood ka kara hakuri wallahi ina iya bakin kokarina ganin ya sakeni but he refused... I don't even know what to do..."

Bai bari yakarasa jin wayar tasuba yaje yakarasa shiryawarshi yana niyyar fita tashigo ta watsar da wayoyin kan gado bayan ta watsa masa harara tawuce cikin bathroom, killer smile ya danyi aranshi yace,

"Daidai kenan"

Karamar wayarta yadauka yafita yabar babbar domin yasan tafi amfani da karamar, lifan dinshi yagoge da duster sannan yahau yafita.Saida yayi nisa da unguwar sannan yatsaya yayi packing agefen titi receiving calls dinta yafara bi yana dubawa har yagano abinda yake son yagano babu bata lokaci yayi dialing number hamood, a kasalance yaji yadauki wayar,

"Sweetheart ya sakeki ne?" Abinda kunnuwan fahad suka jiye masa kenan nan yayi kwafa yafara balbalawa hamood masifa kamar zai yashe hanjin cikinsa ya yar,

"Ban saketa ba kai meya hana ka saketan dakiki?, kai wanne irin garane marar tunani da nutsuwa? Dan tsabar jakanta shine zaka rinka kiran matata kana hure mata kunne wai sai takashe aurenta kunyi aure...... To wallahi bari kaji infada maka wani abu...."

Katseshi hamood yayi cikin bala'i,

"Shut up..... Karka kawo min raini anan domin ni ba sa'anka bane, bilkisu kuma dolenka ka rabu da ita na aureta saboda ita ba matar karamin yaro bace irinka....."

"To ai karamin yaron yayi abinda Kai babban banza ka kasa yi, kawai kazo kana yaudarar matar mutum dan tsabar jahilci da dakikanci,da kasan kana son nata meyasa baka tsaya ka aureta ba sai yanzu da tayi aure zaka dawo kana bibiyarta.... To wallahi am warning u daga yau karka kuskura ka kara kirar min matata idan kuma ka ki ji bazaka ki ganiba..."

"Uban me zakayi idan ansake kiran matar taka? Me kake dashi? Waya san dakai a kasar nan, matsiyaci kawai irinka malam...."

"Zaka san koni waye duk ranar da ka sake gangancin kiranta, banza dan akuya kawai...."

Katse wayar yayi sannan ya kasheta gaba daya ya jefa acikin aljihunsa yabuga Babur dinshi yayi gaba, gidansu yaje amma sam bai nunawa su ayiyah yana tareda matsala ba mamuh sai tsokanarsa takeyi wai yayan barunsa yau su zasu yanke suyi farfesu suci a matsayin abincin rana, shi dai sai dariya yake yajima agidan kafin yatafi da niyyar zuwa kasuwa wurin baba domin bai iskeshi agida ba yasamu yafita kasuwa acan ya shantake wurinsu baba wanda gaba daya shagunan dake layin duk na dattijai ne kamar baba shiyasa suke zamansu zama na mutunci ga yar majalissarsu nan gaban shagunansu karkashin wata bishiyar darbejiya, gefe fahad yakoma yayi zamansa yana sauraren hirar su baba irin tasu ta manya, rabonshi da yazo shagon baba yayi zama irin wannan har yamanta amma yau acan yayi sallar azahar ma nan aka kawowa su baba damammiyar fura cikin katuwar kwarya tasha sugar da gasasshen nama, cups aka fito dasu daga wani shago kowa yana diba sosai abin ya kayatar da fahad wato zama irin na iyayenmu da kakanni abin burgewa ne domin kowa yasan yanda zai zauna da kowa.

Abangaren bilkisu kuwa neman duniya tayiwa wayarta amma tarasa sai babbar amma sama ko kasa tarasa karamar, babu inda batayi checking ba agidan amma bata ganiba daga karshe dai tagane cewa fahad ne yadauka nan ta sake hawa ta cika tayi famm tana jiran dawowarsa amma shiru har hamood yakirata a daya layin nata dake kan babbar wayar yana fada mata irin zagin da fahad yayi masa hakan yasake tunzurata,shi kuwa fahad sai yamma yabar wurinsu baba yanufi shagonsu bayan magriba yakoma gida taso masa bilkisu tayi tamkar zata dokeshi,

"Bani wayata fahad, waye yace ka daukar min waya? Wai menene amfanin zama da mutumin da shi baya son zama dakai? Wacce riba zaka samu?"

Zama yayi saman kujera yana kallonta duk tabi ta hargitse,

"Bilkisu yakamata ki nutsu ki gane mai sonki da gaskiya, wallahi mutumin can yaudararki yakeyi, kiyi hakuri ki karbeni a matsayin miji nikuma nayi miki alkawari bazan baki kunya ba amma wallahi shi ba sonki yakeba dagaske nine nan masoyinki na gaskiya..."

"Ni ba dogon jawabi na tambayeka ba cewa nayi kawai ka sakeni babu ruwanka da rayuwar da zan shiga, babu ruwanka da yana sona ko sabanin haka sannan kabani wayata...."

"Anhanaki wayar kizo ki kwata ai kinada karfi......"

Yafada yana mikewa tsaye babu shiri taja da baya tana kallonsa, nunata yayi da dan yatsa,

"Bari infada miki fa kibar ganin ina kyaleki bafa tsoronki nakeyi ba kawai ina rabuwa dake ne saboda ina respecting dinki ko kina tunanin idan karamar yarinya nake aure age mate dina ko wadda na girma the same way zanyi treating dinta kamar yadda zanyi treating naki? amma wallahi idan kika kaini bango zaki fahimci bakida wayo zaki gane shayi ruwane, tunda kika zo gidan nan abinda kika gadama shi kikeyi ban taba takura miki ba to nima baki isa kin takura min ba, saki ne kuma baza ayiba idan kina iyawa ki saki kanki mana, haba kin takura min dayawa alhalin nikuma bahaka nake yimiki ba daidai da hakkina wannan ba taba bani akayi ba saboda Kin rainani amma ban taba takura miki akan hakanba bayan kuma inada karfin da zan kwata da karfin tsiya..."

Zaro idanuwa tayi tana hawaye cikeda masifa da jin haushinsa tace,

"Dama abinda ke ranka kenan so kake kayi min fyade to kazo kayi idan baka da imani..."

"Zaki gane banida imani sai ranar da na daureki nayi kaca kaca dake nayi round biyar akanki ranar ne zaki san banida imanin...."

Daga haka yawuce cikin bedroom yabarta anan tana sharbar kuka amma hankalinta yayi mugun tashi da jin kalamansa na karshe gaskiya idan fahad yayi mata haka ya cuceta idan ya rabata da martabarta bazata taba yafe masa ba kai wallahi muddin yanemi aikata mata abinda yafada saita raunata shi, zama tayi awurin taci gaba da risgar kuka har tsawon wani lokaci. Shikuwa fahad lokacin da yashiga daki dariya ma dramar su tabashi wato bilkisun nan shegen tsorone da ita sai son girman tsiya domin ya hango tsoronshi karara acikin idanuwanta da dukkan fuskarta gaba daya. Wanka yashiga yayi yafito yunwa na ciciyarshi domin bai wani ci isasshen abinci ba, daga shi sai gajeren wando da farar vest yafita yana janye singiletin zuwa saman kirjinsa sai shasshafa cikinsa yake yi,tana zaune inda yabarta bai ko kalleta ba yawuce dining kamar yadda ya tsammata batayi girki ba sai dafaffen shayin na'a na'a cikin tea flask wanda yanzu shi tamayar abincinta, babu yadda ya iya shi dinma tea din yasha ya dauki slice bread yashafa butter ajiki yaci yana tasowa ta mike tsaye duk da atsorace take dashi amma haka tayi karfin halin yimasa magana,

"Kabani wayata tun muna shaida juna...."

Banza yayi da ita yanufi bedroom,

"Wallahi ko kanaso ko baka so sai ka...."

Juyowa yayi yadawo da baya tana ganin haka ta dora hannu akai tafasa ihu saboda duk atunaninta abinda yafada dazu zai aikata, tsayawa yayi gabanta ya zuba mata ido,nan taja baya cikin sauri,

"Daina gudu karki damu yanzu babu abinda zanyi miki amma duk ranar da nahau kanki wallahi sai kin gane bakida wayo ai nafada miki sai nayi round 5, idan banda rashin tunani irin naki ya za ayi kinada aure ki zauna kina sauraron tatsoniyar wani jahili awaje? Me hakan yake nufi? To wallahi this is the last warning babu ke babu shi, ban son dakikanci da shashanci..."

Idonta fall hawaye muryarta adashe ta kalleshi,

"Fahad ni kake fadawa haka? Ni kake addressing da dakikiya jahila shashasha?"

Sauke idanuwansa kasa yayi sannan cikin sanyin murya yafurta,

"Am very sorry...."

Daga haka yajuya yashiga daki ya kwanta amma baya jin zai iya bacci adaren yau kamar yadda itama bilkisu baccin ya gagareta, inbanda sakawa da kwancewa babu abinda yakeyi har dare ya tsala. Kwana biyu haka nafaruwa har lokacin bai bata wayarta ba kuma bai sanarwa da kowa ba wani lokacin sai yaji kamar yafadawa koda wani daga cikin yayunshi ne amma sai wata zuciyar ta haneshi, gaba daya bilkisu ta hana kanta sukuni danma tana dan shakkarsa yanzu bata son yayi abinda yayita ikirarin zaiyi akanta, yau da safe yana daki kwance yamike yafito falo kwance ya sameta wayarta ya mika mata,

"Bilkisu ga wayarki.... Shi masoyi akoda yaushe yana kokarin ganin yayi abinda masoyinsa zai kasance cikin farin ciki koda kuwa shi din zai dawwama acikin bakin ciki, kamar yadda kika nema kije na sakeki saki daya...."

Cikeda farin ciki ta mike,batace komaiba tawuce bedroom taje tafara hada kayanta, duk abinda zata nema tazuba cikin babban akwati nan ta janyoshi tafito tana rikeda handbag dinta da akwatin,

"Ga akwatinan lefenka can harda sadakinka duk yana ciki..."

"Nabar miki saboda banyi miki dan nakwace ba..."

Bata sake cewa komai ba tasaka kai tafice daga cikin falon, wasu hawaye ne masu dumi suka zubo daga idanuwansa......


*Yar uwa littafinnan na siyarwa ne idan kina so ki biya saiki karanta*


*_Ummi Shatu_*

? *HASKE WRITERS ASSO.*


*KAMAR DA WASA....!*


_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*28*


***Runtse idanuwansa yayi yana jin wani irin kunci acikin zuciyarsa, hawaye yayita yi awurin har saida yaji kansa yasoma sara masa sannan yasamu yatashi yana share fuskarsa da handkerchief din dake cikin aljihunsa, wayarsa kawai ya dauka sai keys dinshi yafita daga gidan dan baya jin zai iya sake awa daya acikin gidan tunda wacce yake zaune saboda ita bata nan, Babur dinshi yabuga yabar gidan bayan ya rufe ko ina, kai tsaye gidansu salim ya wuce yabude dakin salim din yashiga ya kwanta yana jin kansa na cigaba da sassara masa saboda kukan da yayi domin rabon da yayi kuka irin wannan har ya manta. Yana kwance yarasa meke yimasa dadi har salim yashigo ganin idanuwansa arufe yasashi zaton fahad din kila bacci yakeyi wannan dalilinne yasashi ficewa batare da yayi masa magana ba.

Har wurin 12 na rana fahad na kwance dakin salim saida yaji dan dama dama sannan yatashi yatafi gidansu, bai shiga cikin gidanba yabude dakinsu nada shida Abba yashiga yasake kwanciya babu wanda yasan yashigo gidan domin ko babur dinshi bai ajiye wurinda za aganiba, sai lokacin yasamu damar yin kukan bakin ciki nan yarinka yi kamar karamin yaro babu jimawa yafara jin zazzabi zazzabi ajikinsa amma dai yadaure bai tashiba har azahar tayi, anan daki yayi sallah dama wayarshi akashe take saboda bama yason wani ya kirashi, salim ne yabiyoshi gidan bayan yakoma dakinsa yaga baya nan sannan har gidansa yaje amma gidan akulle ga kuma wayarshi akashe. Yana kwance duk jikinsa nayi masa ciwo salim yashigo ganinsa kwance alamun ba kalauba yasa salim fara tambayarsa amma fur fahad yaki magana sai ko ido da yake bin salim dashi,ganin yaki magana yasa salim shiga cikin gida wurinsu ayiyah domin karbo musu abinci, ayiyah na tsame alalan da ta dafa cikin cooler ita kuma mamuh na dama kunun gyada suna aikinsu suna hirarsu, koda salim yafada musu abinci yazo karbar musu shida fahad wanda ke dakin abba basu kawo komai ba suka zuba musu yakoma wurin fahad, dakyar da fada da komai fahad yatashi suka ci alalan domin kwaya daya ma yaci sai dan kunun da ya kurba yakoma ya kwanta,juyin duniya salim yayi akan fahad yasanar dashi abinda ke damunsa amma yaki daga karshe salim yatashi yafita. Tunda salim yatafi fahad ke kwance ya rufe kofar dakin shiyasa babu wanda zai tsammaci cewar da akwai

16 / 36