Author : Ummeey Muhammad Lawan Category : Romantic Books
farin cikin maran misaltuwa
Bude baki yayi zaiyin magana sai sukajin sallamar Mai gadin dauke da akwatuna a hanusa
Daga momy har Muhammad din babu Wanda ya Amsa sallama saima Bata fuska da sukayin
gaishesu baba Mai gaddi yayi ama ko kalonsa basuyiba bare har yasa ran xasu Amsa Masa.
dama in dasabo yariga da yasaba da halinsu haka yaita shugo da kayan Yana gamawa yayi ficewarsa
Abba ne yayi sallama yashigo dauke da far.a a fuskarsa muhammad ne Ya Amsa tare da fadin Abba sanu da hanya cikin jin dadi
Abba yace yauwa kamar ko kasan Ina bukatar ganinka gacan kayan lefe sun kamalla
Ina son a yaudina a kai kayanan anjima gwogwoka zatazo sukai kayan
kaikuma kaje kasamu kan,warka tafada maka Abubuwa da suke bukata Dan gane da bikin kaga lokaci ya ta karatowa
Jiyayi zuciyarsa namishi zafin tankar Ana soka mishi mashi
Da kar ya inya amsawa Abba da toh
Momy ce taya mutsa fuska tace amade baduka wanna kayan za.akai musu bako
Kallonta Abba yayi cikin baci Rai yace mekike nufi da Wana maganar
Cikin takaici momy tace gani nayin kayan suyin yawa saikace wata Yar hamshakin Mai kudin za a Auro alhalin Kuma Yar gidan matsiyatane
Cikin takaici Abba yace Yar Dan uwa nawa ne kike Kira da Yar matsiyata to wlh kishi ga hankalinki
Muhammadu Dan uwa nane na jini yafi karfin kikirashi da matsiyaci
Kuma inaso kisani da ummeey da muhammad duka sun Yan,yanane
Matsayinsu daya ne a guna
Mikewa momy tayin cikin masifa tace kada kasake hada wacer matsiyaciyar da Dan,na Dan wlh ko makaho ya laluba yajin yasan Akwai banbanci a tsakani ..
By YAR AUTAR DASHEN ALLAH......✍🏻🤵🏻♂ZABIN ABBANA🎅🏻
. NA
UMMEEY MUHAMMAD LAWAN
( UMMU AFNAN)
YAR AUTAR DASHEN ALLAH
For more inf...08140801885
Page 27 & 28
___________________"Abba Kam shigewa daki yayi ya kyaleta tanata bambaminta shima Muhammad din cikin bacin rai yayi ficewarsa daga gidan
Da misalin karfe 3 : 40 Gwogo Halima ce ita da sauran Yan,uwa suka nufi gidan yayanata
Momy dake fallo a zaune tazuba uban tagumi abun duniya duk yabi ya isheta
Tana cikin Wana yanayine tafara jiwo hayaniyar mutane
Da sallama suka shigo fallo Dakar Momy ta inya Amsa musu cikin daurewar fuska tace ohh Ashe kune
Shiyasa naita jin hayaniya sai kace wasu karnuka cikin bacin rai Gwogwo halima tace kada kikuskura kikara budan baki kikiramu da karnuka wlh kishiga hankaliki
Gwogwo Asabe ce tace Dan Allah Halima kubar maganar nan
Mufa Wana ranar Rana ce tafain ciki a garemu kiga baidace Ace mutsaya Munata sa isa da juna ba
Yakamata mu hanxarta mu dau kayanan mutafi kar dare tayimana
Gwogo Asabe ne Tak'arasa Ida kayan suke fara dauko kayan tayin suka fara budewa suna dubawa
Kowa nagurin Saida yayi santii kayan Dan bakaramin kudin Abba ya kashe ba
Akwatiina Sha biyu kowane a makare yake da kaya bude wata jaka sukayi sukaga daleliyar waya sai daukar ido takeyi
Cikin jin dadi Gwogo Halima tace la kuga harda waya cikin kayan lefen Suma karba waya sukayi suna xuxuta irin kyau ta
Rabi ce tace Kai gaskiya Ummeey tayin goshi Allah de yabada zaman lpy
Gwogwo Asabe ce tace ai dama can uwata Mai sa.ce da sa,arta take tafiya duk Wana da yarabeta saiya samu wanna sa,ar Kwoshewa sukayi da dariya
Momy de nazaune a gun gaba daya haushisu takeji jitake kamar taje tarufesu da duka
Haka suka tarkata gaba daya sukayi waje motocisu Mai gadi da direba ne suka debo kayan suka sa a mota
Kai tsaye gidasu Ummeey suka wuce dama mama tasan da zuwasu itama ta sanar da Yan,uwa da Abokan Arziki
Basu Bata lokaci ba suka inso gida cikin girmamawa Yan,uwan mama suka tarbesu dama Kuma suba baki bane a gida domi gaba dayasu Yan,wa junna ne
Bude akwaiina suka farayi kowa na kalon irin dukiyar da aka zuba a ciki
Haka mutane sukaita son barka kowa nayiwa ummeey fatan zaman lafiya
Hauwa ce tashigo dakin cikin sauri ta rugume Ummeey cikin farin cikin tace sister na kiyin goshi kiga iri dukiyar da muhammad ya kashe wajen gani yazuba mikin kayan lefe nagani nafada har da waya fa yasamiki a ciki Kai amafa kemai sa.ace a rayuwa
Tureta Ummeey tayi daga jikinta Ba,ta fuska tayi tace nikuma kiga Wana kaya basa gabana
Jikin Hauwa ne yayi sanyi tace kiyin hakuri Ummeey bawai nayi haka bane Dan nabata Miki Rai saide a rayuwata nakaji farin ciki Ida Naga Abu alkairi a tatare dake
Girgiza Kai ummeey tayin tace duk iri dukiyar da Yaya muhammadu zai kashe a kaina wlh bazasu taba sani farin ciki ba
Hauwa hijjabi ta tadauka tace kigani sai gobe Dan Naga zance naki ba Mai karewa bane ficewa Hauwa tayi tayiwa mama sai da safe
**********************
Kano
Tuda Haydar suka kama haryar Kano Adam yaketa fama Masa nasiha suna shigowa cikin Kano
Adam har gida yakai Hayda suna shiga suka Tara da dady da Ammy suna hira
Gaishesu sukayi ciki kullawa suka Amsa suka musu Yaya gajiyar hanya
Ammy ne ta dubesu ciki kullawa ta ce yanaganku haka jiki duk a mace kode Baku sameta bane
Shide Haydar kasa magana yayi gani suyi shuru babu wada yabata Amsa
Ammy tace wai meke faruwa ne kusanar da mumana
Adam ne yayi karfin halin yasanar dasu duk abuda ya faru ..
Ammy da dady Suma basuji dadin faruwa haka ba ama yayazasuyi Basu insa su sauya Masa kaddara Saba
Haka dady da Ammy sukaita rarashisa akan ya manta da komai kalamai iyayyenasa suyi tasiri a kansa domi ko ya rage yawan damuwa da tunnani
Gombe
*****************
Muhammad ne tsaye a kofar gidasu Ummeey fuskarna a murtuke babu a Lamar far,a atare dashi
yaro ya aika akan yakira Masa ita Bata wani Bata lokaci ba tafito insowa tayi inda yake tare da Masa sallama
Bai Amsaba saima binta yayi da wani wulakantece kallo kasa tayi da kanta Tana wasa da Yan,yatsu hanuta
Ciki gadara yace Mai kike bukartayi a bikinaki
Dago Kai tayi ta kalesa ciki sanyi murya tace a a bana bukatar komai
Bude motasa yayi ya ciro kudi masu yawa ya mika mata
Kin karba tayin tsawa ya daka mata har Saida ta razana batasan lokaci da Tamika hanu ta karbaba
Cikin sauri ta wuce gida
*****************
A YAUNE DUBA JAMA,A SUKA SHEDA DAURI AURE
Muhammad Abdallah Shu,Abu & Ummeey Muhammad Shu,Abu Abisa sadaki Naira dubu dari dauri Aure da yasamu halatar duban jama.a daga sasan jahohi daba daba
Gidasu Amarya yacika da jama,a sai hidima akeyi kowa kagani zakasan Yana cikin farin ciki
Ama bada Ummeey dataketa Aiki kuka hauwa sai rarashinta takeyi Ama Ina Taki tayin shuru
Abba ne yashigo yatura mama takira Masa ummeey
Shigowa daki mama tayi kama hanuta tayi tace tashi muje gacan Abbaki Yana kiranki
Bin mama tayi suka nufi dakin Abba Yana zaune a kan kujera durkusawa tayi a gabansa
Gyara murya Abba yayi yafara mata nasiha akan taji tsoro Allah tabi mijinta nasiha Abba yamata Mai ratsa zuciya
cikin kuka Ummeey tace Abba namaka Alkawari zan zamo Mai biyyayah ga mijina bazaka tabajin wani Abu Mara dadi daga gareni ba
Abba kayafemin duk wani abuda na aikata a gareka wada ranka bai soba
Cikin tsanyi jiki Abba yace babu abuda Kika taba min tsakanina dake sai Adu,a Allah yamiki albarka Allah ya Baku zuri.a danyiba
Kara fashewa tayi da kuka
Kama hanuta Mama tayi suka fita daga dakin mama tace da hauwa kuyi kushiya kuga gacan Yan dauka Amarya sufara zuwa
Mamaa ma hawayene keshiri zubowa daga idonta tayi sauri Mai dasu
Dakyar hauwa tasamu Ummeey tashiya haka Yan,dauka Amarya suka shigo
Dakar aka banbare Ummeey a jikin mama kuka Ummeey takeyi sosai mama ma kuka tafara
Haka ummeey tanaji Tana gani tabar mamanta acikin motar ma Ummeey Bata dena kuka ba suna insowa gida kowa yafito daga mota ama ita Taki fitowa
Gwogwo Halima ce tajawota daga cikin motar sukayi cikin gidan
Gidan ya tsaru sosai kowa sai Yaba kyawu gidan yakeyi
Domi Muhammad bakaramin kudin ya kashewa gida ba
Mutane suka wawatse gida yarage daga ita sai hauwa......
By YAR AUTAR DASHEN ALLAH....✍🏻 NA
UMMEEY MUHAMMAD LAWAN
( Ummu Afnan)
"YAR AUTAR DASHEN AoLLAH
For more inf... 08140801885
Page 29 & 30
___________________"mikewa Hauwa tayi tace Sister ya kamata nima yazukan natafi gida kiga dare yayi
'Rike gyaleta Ummeey tayin tace kema tafiya zakiyin kibarni a cikin wanna gida nikadai
Takarashe maganar kamar Mai Shirin yin kuku
Hauwa tace kiyi hakuri Sister ya zamo dole natafi babu yarda muka inya Aure ya riga da yarabamu
'kuka ne Mai karfi ya kufce mata ciki kuka tace kidena fadin haka yin Aurena bawai Yana nufin mu rabu da juna bane ai shin Aure ba mutuwa bane munana tare nidake insha Allah itama Hauwa fashewa tayin da kuka suka rugume juna
'A haka de Hauwa tawuce gida cikin Rashi jidadin rabuwa da Aminiyartata
**********************
Shiko Ango jin Wana ranar yake kamar ranar mutuwarsa Tsatsar baki ciki ne bayane a fuskarsa
Isma,il ne yace Abokina yakamata Ace yazuka kawuce gida Amaryarka tanacan Tana jiranka
'Wani mugun kallo ya watsa masa cike da jin hashisa yace in naje gidan uban mezamata Kai kasan yanda natsani yariyarnan kuwa
Isma,il yace nifa Muhammad banga ai bun yariyarnan ba Ummeey Tana da kyau Tana da ilimi Tana da tarbiya duk wani Abuda ake nema a gun mace to Ummeey tana dashi
"Muhammad Mai kake nema Agun Mace wada Ummeey bata dashi kada kamata ita dinfa jinikace kajin tsoro Allah karike yariyarnan tsakani da Allah idafa har kacutar da ita Allah bazai taba barinka ba
'cikin fushi yace takatta✋ Mallam wanan Yar guntuwar nasihar taka bazatayi tasiri a kainaba
Naga a lama Kai bakasan Mai akenufi da Aure dolle ba bakasan radadin dake tatare dashiba
Cikin fushi yatashi ya shinu mota keey yayiwa mota yafigeta da karfi har Yana tada kura
Isma,il bisa yayi da kallo yace Allah ya shiryeka Abokina bazaka taba gane irin gatan da Abba yayi makaba sai nagaba
'yana insowa gida hon yafarayin Mai gadine yazo cikin sauri ya wangale geet din
Shigowa yayi ya kashe motar yafito Mai gadi ya gaisheshi daga Masa hanu yayin
yayi shigewarsa ciki
kaitsaye dakinsa yanufa dakin bakaramin haduwa yayiba komai na dakikin farine kal sai daukar ido yakeyi
Cire kayan dake jikinsa yayi ya wuce tolet wanka yayi yafito ya wuce gaban Miro goge jikinsa yayi da tawul
Mai ya shafa sana yafeshe jikinsa da turare masu kamshi kaya barci yasa ya haye kan gado wayasa dake ta fama Kara ya dauka karawa yayi a kunesa
Yace hello baby y kk ?
Cikin shagwaba meenat tace tooo gani na de kwance cikin tunanika zuciyata takasa samu nutsuwa
idan natuna cewa yau zaka hada jiki dawata Yan mace baniba sainaji zuciyata tankar zata tarwatse nakasa yarda da Alkawari daka daukamin
"Kwantar da hankaliki baby ai babu wata Yan,mace dazan inya hada jiki da ita "Idan bakeba
"Kikara hakuri baby nan dawasu Yan,kwanaki zanje nasamu Abba nasanar dashi kece zabina yaje yasamu dadynki a yin maganar Aure mu
Wani sanyi dadi taji naratsata cikin fari ciki tace too baby kamar nan da wane lokaci kena Dani gaskiya namatsu Naga anyi bikinan kowama yahuta..
Muhammad yace aini nafiki burin gani Wana Rana ama karki damu kamar yau ne ranar zatazo kiji baby na yaxu Dee barci nakeji zan inya cemiki good night
Cikin shagwaba Meenat tace ko nazo natayakane nasa sai kafijin dadin baci musamama idaka daura kanka a saman kirjina
Murmushi Muhammad yayi yace sauri mekikeyi baby lokaci hakan yanana zuwa kamar yaune
Uhmm ida nabiyeki sai mukwana a haka byeee kikulamin da kanki ilove you so much kashe waya yayi wani fari ciki ne ke shigarsa murmushi yayi yace
Meenat kekadance kike sani fari ciki Koda Ina cikin damuwa Ina sonki Meenat
*********************
'Hauwa natafiya Ummeey waka tayi tadauro alwala tayi sallah tadade a kan salayan Tana rokon Allah da yabata ikon yiwa mijinata biyayyyah baci ne Mai nauyi yayi awun gaba da ita
Bata farkaba sai da Asuba tashi tayin tannufi bayin dauro Alwala tayi tatada Sallah
Tana indarwa Alqu,an tadauka tafara karata Suratul Maryam
Agogo taduba taga karfe 6:30 rufe Alqur,ani tayi tatashi tanufi kichin domin tamusu Abun karyawa
dubawa tayi taga duk wani Abuda Ake bukata nakayan Abinci akwaishi a kichin din
Dankalin tasoya da kwai sai farfesu kifin da ruwa tea Tana gamawa tashige daki
wanka tayi tafito tazauna a gaban Miro kwaliya tayi wada hakan yakara fito mata da kyauwu fuskarta
Bude Akwatin kayan lefenta tayi taciro wata doguwar riga baka Tasha adon siton
rigar tasaka tayafa dankwalin rigar a kanta
bakaramin kyau tayiba kichin Takoma tadebi Abinci inya wada zata iyaci
Jerawa kuloni tayi akan wanni hadadden tire
dauka tayi tanufi dakisa gabanta nafaduwa A hankali tamurda kofar tashiga bakinta dauke da sallama
Zaune yake a kan kujera ya daura kafa daya kan daya
Karasawa tayi Ida yake durkusawa tayi a gabansa ta ajiye tiredi dake dauke da Abinci cikin girmamawa tace Ina kwanna Yaya.
Dago Kai yayi ya sauke idanusa Akanta take yaji wani sabo tsanarta yakara shiga zuciyarsa.
ciki bancin Rai yace keeeeee.. ubawa yace kishigomin daki
Kasa tayi da kanta tace Abincika nakawo maka Naga baka fito bane duban tiredin dake gabansa yayi hanu yasa ya dau kofin dake dauke da TeA a cikin dagowa yayi yawatsa mata a fuska
Wani iri Kara Ummeey tasaka sakamoko zafin dataji Akan fuskarta
Mikewa yayi yamatso daf da ita cikin kakausar murya yace a gidan uwarki nake cin Abinci dazakiyi tunani tuda nabar gida ba Mai bani Abici
konayi Miki kama dawanda zaki kawowa Abu yaci to wlh duk ranar da kikasake shigomin daki saina ballaki
Zaki Fitamin daga daki Kosaina ballaki wawiya kazama
Hawayene ke zirya a fuskarta maganganusa sumata ciwo musamama zaginta dayayi a duniya babu Abuda tatsana irin a zagin iyayenta
Fita tayi daga danki a fallo ta zauna kifa kanta tayi a kan kujera tafara raira kuka Mai tsuma zuciya.....
BY YAR AUTAR DASHEN ALLAH.....https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share
_*FACEBOOK LINK*_
https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link
_*WHATSAPP LINK*_
https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA
_*DASHEN🌲 ALLAH*_
_*WRITER'S ASSOCIATION📚📚*_
_*ALLAH SHINE GATAN MU*_
_{ƙungiyar dashen allah ƙungiya ce ta jajurtattun marubuta kuma tsayayyu masu aiki da ilimi wajen rubutunsu dan ganin sun kawo muku labari wanda zai wa'azantar daku ilimantar daku, faɗakar daku.}_
*Alƙalami✍🏽 yafi takofi🗡️*
_*ZAƁIN🤵🏻♂ABBANA👳🏼♂*_
_*NA*_
_*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_
_*(UMMUH AFNAN)*_
_*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_
For more inf...08140801885
Page 31 & 32
___________________Bugu kofar da Akeyine yasata daga kanta share Hawayen da suka Bata mata fuska tayi
tashi tayi tanufi bakin kofar hannu tasa tabude Gwogwo Halima ne ita da Hauwa
Murmushi jin dadi tayi tace sanu da zuwa Gwogwo Sister kekuma sai yazu kikaga dama zuwa ko Aini fushi nakeyi dake
Kallonta Gwogwo Halima tayi tace yau Naga ikon Allah yaushe ma garin ya waye to da Asuba kikeso tazomiki gida
Hauwa tace kyaleta Gwogwo so takeyi nazo da sasafe ya muhammad ya korani dariya Gwogwo tayi
Ummeey Kalon Hauwa tayi ta wuga mata harara Kara Kwashewa da dariya Hauwa tayi tace Gwogwo kiga Tana harata ko saboda nazo gidanta
Dariya Gwogwo tasa tace Ai kunfi kusa babu ruwa na
Gwogwo tace kehaka ake tarbar baki bazaki bamu gurin zama ba
Ummeey Tace lla Gwogwo kiyi hakuri duk gawace tabi ta insheni da surutu tanuna Hauwa Hauwa tace nikan karkimin Shari kede dama haka kike.
Zama sukayi a kujera Ummeey takawo musu lemo da ruwa sai a lokaci tatuno bata karya ba
Tashi tayi nufi kinchi tadauko kullolin data zuba nata Abinci ta ajiye a gabasu
Suna cin Abinci suna hira Gwogwo nabasu labarai sukuma sai dariya sukeyi dama Kuma Gwogwo takware wajjan barkonci da bada dari
Muhammad dake zaune a dakinsa ya soma jiyo hayaniyar tasu tsaki yaja a ransa yace wato yariyarnan hartafara jidomin tarkace mutane a gidana
To wlh gaba daya sainayi maganisu mikewa yayi ya fito daga dakin kaitsaye falon nata yanufa
Gwogwo ko suna gama cin Abinci tace zata zaga bandaki Ummeey tanuna mata inda bayin yake
Ta dawo tafara gyara gurin dasuka cin Abinci
Yana insowa inda take tsaye hanu yasa ya sharara mata wasu lafiyayu maruka Wanda Saida shatin yatsutsa yafito a kan fuskarta
tangaltagal tayi zata Fadi Hauwa tayi sauri tatareta kuka tasaka Mai