Author : Ummeey Muhammad Lawan Category : Romantic Books
Kai kadaine wada idan nakala nakaji sanyi a ciki Raina nakan daga hanuwana sama in godewa mahalincina daya hadani da Wana santalellan saurayi kalarka kalar burgewa murmushinka shiyake sake narkar da zuciyata ciki kaunarka
kallon kallo mukewa juna nida ita wada haka yayi sanadiyar shigarmu cikin wani yanayi Mara fasaruwa
Gawani sanyi ni,ima nakadawa a ciki lambu wada hakan yayi sanadiyar shigewar Ummeey jikina Kam, kame,ta nayi da karfi tankar wani zaizo ya kwacemin ita
Kiraye kirayen sallah Asuba ne ya sauka a kan kuneena tashi nayi nazauna Ina tuno Abubuwa da suka faru a ciki mafarkina murmushi nayi gami da fadin ya Allah katabatarmin da Wana mafarki
Tashi nayi nanufi Toilet na dauro Alwala nawuce masalaci ban dawo gidaba Saida gari yayi Haske
Shiri tafiya office nayi nafito nataran da Ammy da Dady sai Kuma Fatima kanwata suna karyawa zama nayi kusa da Fatima
Na gaishe da Ammy da Dady mikewa Fatima tayi tahadami. Tea sana tazubamin ferfesu kifin
fuskarta dauke da murmushi tace ya Haydar ango Anty Ummeey dafatan katashi lafiya
Ga Abinci ka ciye duka kaga Anty ummeey zataji dadi ganika haka
Dariya sukayi gaba dayansu Haydar yace Ammy kiga yariyar nako tsabar tamai Dani Mai cikin rada Wai naciye Wana abinci duka
Murmushi Ammy tayi tace kufi kusa Dan Naga duk wada ya shiga tsakaniku Kai da Fatima to shi zaiji kuya
Shuru yayi ya fara cin abincisa Yana gamawa ya Mike yace Dady Ammy nawuce office
Dady da Ammy suka yimasa a dawo lpy fatima tace Allah yatsare ango Antyna murmushi yayi Hadi da girgiza Kai yace keba nasan maganiki yayi ficewarsa daga gida Kai tsaye office yanufa......
Yar Autar dashen Allah......__________________ "Ummeey namin wani irin son wada baki bazai inya furtawaba hakama Kuma ido bazai inya kwatatawaba"
Domin tayi nisa a ciki kaunarta
Dami salin karfe 4:30 nayi shirina cikin kanana kaya nikaina nasan bakaramin kyau nayiba
"Kai tsaye gidasu Ummeey nanufa yaro na aika yamin sallama da ita fitowa yayi yace Dani Tana zuwa
"Niko Ina tsaye a jikin mottata fitowa tayi cikin takunta Mai daukar hankali ta karaso Ida nake bakinta dauke da sallama.
Sanye take da hijabi har kasa duk da hijabi da tasaka haka bai hana fito mata da kyauwu da Allah ya mataba
Cikin muryarta Mai dadin sauraro tace barka da zuwa angona dafatan ka Inson lafiya yasu Ammy
Tsitar kaina nayi ciki wani irin yanayi kaallonta nake Ina murmushi gashi na gagara Amsa mata gaisuwanta
Son Ummeey Yana Neman zautar dani
Murmushi tayi tace diya Wana kallon haka ai saika hadiyeni
Murmushi nayi gami da sake kureta da kallon sayayya Mai ratsa zuciya masoya nace waneni ai Haydar bai insa ya hadiye Ummeey saba
Idan na hadiyeki to wazan kallan anjima kisan nifa idanuwana basa gajiya da kallon wanna kyakyawar fuskarna taki
Sa anan kunuwana basa gajiya dajin sauti muryarki Mai dadin sauraro
Ummeey tace Haydar zuciyata takamu da kaunarka a lokaci da banyi zatoba sonka yariga da ya daskare a cikin zuciyata babu tayarda za ayin yafita saide idan an tsaga zuciyata
kaga tsaga zuciyata Kuma shine zai zamo sanadiyar rasa Raina.
Rayuwa zata min dadine idan har kakasace a tare Dani ina son kayimin alkawari cewa bazaka taba barinaba duk wuya duk ritsi Muna tare da Kai
Zamu rayu a karkashin inu daya Zan zama matarka Kuma uwar Yan,yanka kada mubawa shaidan dama da zai farakamu
Haydar ina son kayimini Alkawari cewa Kai nawa ne babu Abuda zai rabamu idan ba mutuwaba
Mutuwa ma Dan tazamo dolene zan son ace tafara daukana Kaikuma tabarka a Raye Dani bazan taba jure rashin kaba
Wlh rayuwata Bata da wani anfani idan yau akace babu Kai a tare Dani ka tausayawa zuciyar data cika da kaunarka kazauna a cikinta kabata kulawa tamusama kada daga baya kace zaka fita daga cikinta Hawayene ke zuba daga idanuta
hannu nasa natari hawayeta hankalina bakaramin tashi yayiba gani Hawaye nazuba a idanu Ummeeyna zuciyata namin zafi jinake tankar ana zubami ruwa dalma
Ciro Hamkicif nayi daga aljihuna mika mata nayi. hanu tasa takarba
kishare hawayenki Ummeeyna mudin Ina Raye bazan taba bari kizubar da hawayeba Ummeey idan da Alkawari Haydar Bazai taba juya Miki bayaba
Mudin Haydar Yana Raye bazai taba barin Ummeeyn saba nayi Miki Alkawari zamuyi Aure nidake zamu haifi yara kyawawa
Hanu nazira ciki Motata naciro leda namika mata.
Matsawa tafarayi da baya tace Mai zangani Haydar Ina sonka ne Dan Allah badan kudin kaba idan har kanaso kamin wata kyauta to kabari sai ranar da nazama malakinka
Mamakine ya kamani gani yada naga tarude akan namata wata kyauta wada batasa menene a cikiba lallen Ummeey tadabace a cikin mata
Babu yarda bayi da Ummeey ba akan takarba ama Taki
waya dake ciki ledar naciro mika mata nayi gashi ai waya kan Zaki karba kodan muke gaisawa ko
Girgiza Kai tayi tace kayi hakuri Haydar wlh banso nayi jayaya da kaiba Abbana ya hanani rike waya
Nikuma bana son nayi Abuda zai batawa Abbana Rai kayi hakuri akwai ranar da zan kasance karkashi ikonka a ranar kana da damar min duk wata kyauta da kaga tadace dani
Jinayi Ummeey takara samu wani matsayi namusama a ciki zuciyata sallama mukayi tawuce gida
***************************
Musamu kimani shekara daya nida Ummeeyna munshaku sosai har nazamo gareta tankar Yaya mutsarawa yarda zamu gudanar da rayuwarmu da zaran muyi Aure...
By YAR AUTAR DASHEN ALLAH......https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share
_*FACEBOOK LINK*_
https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link
_*WHATSAPP LINK*_
https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA
_*DASHEN🌲 ALLAH*_
_*WRITER'S ASSOCIATION📚📚*_
_*ALLAH SHINE GATAN MU*_
_{ƙungiyar dashen allah ƙungiya ce ta jajurtattun marubuta kuma tsayayyu masu aiki da ilimi wajen rubutunsu dan ganin sun kawo muku labari wanda zai wa'azantar daku ilimantar daku, faɗakar daku.}_
*Alƙalami✍🏽 yafi takofi🗡️*
_*ZAƁIN🤵🏻♂ABBANA👳🏼♂*_
_*NA*_
_*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_
_*(UMMUH AFNAN)*_
_*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_
for more inf...08140801885
Page 47&48
_________________"Haka rayuwarmu takasace kullun ciki fari ciki da anashu wani irin sabo mukayi wada har,takai ga bama boyewa junamu komai
Ummeey bata da wani buri da ya wuce kullu taga tasani ciki fari ciki
Haka mukaci gaba da gudanar da soyayyarmu bamu taba kawowa a ramu akwai wata kaddara da zatazo tarushemuba
Kullu nasara muke hangowa da buri malakar juna Soyayya muke zubawa Mai cike da kauna
Shikasa Adam soyayyata da Ummeey bakarami burgeshi tayiba harta kaiga yamin lakabi da Haydar na Ummeey
Ita kuma Ummeey Haydar Wana suna da Adam yasa Mana yabimu domi ko harta Abokanayemu haka suke kirana da Haydar na Ummeey
Itama anata bangare haka kawayeta suke kiranta Ummeey Haydar
"Bana mantawa Akwai watarana da nazo kofar gidasu ummeey zance tafito ita da kawarta Maryam suna karosowa Ida nake
Maryam tace Haydar na Ummeey sunaka yazagaye ciki kawayemu domin duk wada yasa suna Ummeey to yasa na Haydar
yaude Allah yanuna min Haydar din Ummeey
Murmushi nayi nace sai Kuma kikaga Haydar din Ummeey jinsa yafi ganishi ko
Zare idon tayi tace rufami asiri kada kasa yazu Amaryarka tabuge anan
Kallonta Ummeey tayi dauke da murmushi akan fuskarta tace kwantar da hankalinki bazan bugekiba aini banason kowa ta yabamin mijina Nafison ace nikadai ce zanga kyauwusa
Itama Maryam murmushi tayi tace Haydar Ina tayaka murna kayi dace samu mata Tagari gashi kudace da juna Allah yabarku tare har Abada
Amsawa mukayi da Amin wani dadi naji Yana shiga ciki Raina nace kawarmu dolene nabaki tukunci hanu nasa cikin aljihuna naciro kudin wada bansa yawasu ba namika mata Hanu tasa takarba hadi damin godiya
*********************
Anyi bikin kanwata Fatima da angon ta Sadiq wada nikaina naso ace an hada da namu biki ama Allah bai nufaba. Fatima tayi kuka rabuwa damu wada nikaina basan Hawaye nazubo daga idanunaba saboda duk duniya bani da kamarta ita kadaice Yar uwata abokiyar shawarata ida bada Aure babu Mai rabani da Fatima .
*************************
WASHE GARI
"Da yama nida Adam mukaje gidasu Ummeey. Muka gaishe da mahaifiyarta tayi farin ciki sosai daga nimu
Tatarbemu cikin girmamawa da karanci
***********************
Baya mun dawo daga gidasu Ummeey Kai tsaye daki Dady nanufa
Sallama nayi nakarasa Ida yake gaisheshi nayi ya Amsa cike da kullawa
"Kallona Dady yayi cike da kulawa yace Haydar kamar a kwai maga a bakinka ko Sukuyar da Kai nayi kasa nace dama Dady inaso aje a nemamin Aure Ummeey ne muriga da mudedeta kamu
Dady yace Alhamdulillah dama nima akwai maganar da nakeso nayi dakai nasa kasan Wana Company da nake ginawa a Kaduna Alhaji Yahaya shine Mai lura da gun
To yau yake sanar Dani bashi lpy shine nake son kaje kalura da guri kamin Allah yabashi lafiya
Daka dawo zanje na nema maka Aure Ummeey a gun Mahaifinta
Jinayi tankar natsala ihu take zufa yafara ketowa a jikina
yazayi da wanan lamari Dadyna Yana da muhimaci a gareni bazan inya salake Umarnisaba
Take nadaure nakwon da duk wata damuwa datake damuna nace Dady babu komai Allah ubangiji yakamu gobe ama Dady zanyi kamar kwana nawane a can Kaduna
Dady yace karka damu Haydar da zaran yasamu lafiya zaka dawo ama inaga bazaka wuce sati biyu ba
Dago Kai nayi da sauri take gabana yafadi ayyah zan inya jurewa nayi har sati biyu batare da nasaka Ummeey a idonaba
Jikina a sanyaye nace to Dady Allah ya kaimu gobe ya Amsa da amiin mikewa nayi gami da fadin Dady a huta lafiya sai da safe fita nayi daga dakin Dady nanufi dakina
Inajin wani iri a ciki zuciyata wayata naciro nakira Adam nake shaida Masa yarda mukayi da Dadyna shikasa Adam yaji babu dadi
Ama sai ya karamin karfin gunwa gamin da cewa Haydar sati biyu kamar yaune a gurin ubangiji
kada kadamu kanka kaide kayi fatan Allah ya Kaika lafiya ya dawo da kai lafiya Dan Allah Haydar kada kabari Dady ya fahici halin dakake ciki
Nasamu kafin gwuwa daga guri Adam domin Adam Abokine nagari Mai son gani cigana a rayuwa take naji duk wata damuwana tayaye
Godiya nayi mishi sosai sana mukayi sallama
By YAR AUTAR DASHEN ALLAH.......https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share
_*FACEBOOK LINK*_
https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link
_*WHATSAPP LINK*_
https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA
_*DASHEN🌲 ALLAH*_
_*WRITER'S ASSOCIATION📚📚*_
_*ALLAH SHINE GATAN MU*_
_{ƙungiyar dashen allah ƙungiya ce ta jajurtattun marubuta kuma tsayayyu masu aiki da ilimi wajen rubutunsu dan ganin sun kawo muku labari wanda zai wa'azantar daku ilimantar daku, faɗakar daku.}_
*Alƙalami✍🏽 yafi takofi🗡️*
_*ZAƁIN🤵🏻♂ABBANA👳🏼♂*_
_*NA*_
_*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_
_*(UMMUH AFNAN)*_
_*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_
for more inf...08140801885
Page 49 50
_________________"Washe gari da safe nafito ciki shirina sallama nayiwa Ammy da Dady sukayi min fatan alkairi da fatan dawowa gida lafiya
Adam naki a waya mukayi bakwana yamin Allah ya kiyaye hanya Muna gama waya dashi
Gidasu Ummeey nanufa Dan aike natura yamin sallama da ita
Ita kanta Ummeey Saida tayi mamaki zuwana a Wana lokacin Dan tida nake da ita bantaba zuwa gidasu a iri Wana lokaciba
Hijjabinta tasaka tace Mama banaje nagani ko lafiya Haydar yazo a Wana lokaci Mama tace to sai kin dawo Allah de yasa lafiya
Tana fitowa daga gidansu kallo daya Ummeey tayimin tagane cewa akwai damuwa a tatare Dani
Kallona tayi dauke da damuwa a kan fuskarta tace Diya lafiya kuwa naganka ciki iri Wana yanayi
Wani kallo nake mata wada ita kanta sai da tatsorata
Ummeey tafiyace takamani zuwa Kaduna Dady ya turani domin nalura Masa da wani Company sa
Ama kiyi hakuri bazan wuce sati biyu ba zan dawo
Kallona Ummeey tayi fuskarta dauke da damuwa tace Haydar yazu tafiya zakayi kabarni kasafa zuciyata dakai tasaba idanuwana sunsaba da ganika kunuwana sunsaba da saurara sautin muryarka
Bazan inya hakuri Rashi ganikaba har na tsawo sati biyu zuciyata bazata inya jurewaba
Ama yazanyi kajeka Haydar tuda Umarnin Dady ne bamu insa mutsalake Umarnisaba
Ama nasani zuciyata zata kasace cikin radadin Rashi ganika takarasa magana ciki kuka
Gani Tana kuka yasa Kwata Kwata naji tafiyar tafita a kaina
Rarashita nafarayi kiyi hakuri Ummeey kidena zubar da hawayenki babu Ida zani nafasa zuwa zaje nabawa Dady hakuri tuda bakya so bazan inya tafiya nabarki ciki wana yanayiba
Girgiza Kai tafarayi idonta cike da kwalla tace Ah Ah Haydar kada kafifita farin cikimu fiye dana Dady zamu inya jure duk wani kunci domin gani Iyayyemu susamu fari ciki .
Na amince katafi fatanade karikemin alkawarina kakulamin da kanka a duk Ida zaka shiga banyarda kakula wata Yan,mace ba
Ina son kasani Koda gangar jikimu suyi nesa da juna to zuciyoyimu sunanan mane kamar hanta da jini suke bazasu taba rabuwaba
Fatana Allah ya Kaika lafiya ya Kuma dawo min dakai lafiya!!
Kura mata idon nayi cike da Son da kauna nace ai kiriga da kin gama mamaye zuciyar Haydar da kaunarki babu wani matsuguni da wata zatasamu a ciki domi ko Haydar na Ummeey ne
Nadade da kulle zuciyata da Dan makulin nayar dashi a ciki teku
Baby zantafi Ina son kikulamin da kaki Dady yace dazaran na dawo za a kawo kudin Auremu kiga shikena nakusa zamowa Ango kekuma Amarya ko
Murmushi tayi hadi da rufe fuskarta da tafukan hanuta
Dariya nayi nace zan tafi Amaryar Haydar sauri tayi tacire tafin hanuta daga kan fuskata ciki wani irin yanayi tace Allah ya Kaika lafiya ya dawo da kai lafiya
Kukane ya kufce mata da sauri tayi gida
Tsayawa nayi a gun jikina a sanyaye narasa Mai yakemin dadi
Da kar na inya Jan Motata nabar kofar gidan zuciyata cike da damuwa nadau hanyar Kaduna...✍🏻https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share
_*FACEBOOK LINK*_
https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link
_*WHATSAPP LINK*_
https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA
_*DASHEN🌲 ALLAH*_
_*WRITER'S ASSOCIATION📚📚*_
_*ALLAH SHINE GATAN MU*_
_{ƙungiyar dashen allah ƙungiya ce ta jajurtattun marubuta kuma tsayayyu masu aiki da ilimi wajen rubutunsu dan ganin sun kawo muku labari wanda zai wa'azantar daku ilimantar daku, faɗakar daku.}_
*Alƙalami✍🏽 yafi takofi🗡️*
_*ZAƁIN🤵🏻♂ABBANA👳🏼♂*_
_*NA*_
_*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_
_*(UMMUH AFNAN)*_
_*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_
For more inf...08140801885
Page 51_52
________________"Dami salin karfe 1:30 nashigo ciki gari Kaduna nasauka a gida Abokin Dady dake G.R.A
Nasamu tarba Mai kyau daga guri Alhaji Buhari da Dan,sa Kamal domi bakaramin fari ciki sukayiba da zuwana gidasu
Dama Kuma Susan da zuwana domi Dady yasanar dasu
Kamal ne yadubeni yace Haydar mushiga ciki ko kasamu kawatsa ruwa kayi Sallah gana Abinci Yana zama jiranka
Murmushi karfi hali nayi nace ok muje dauka jakar kayana yayi muka wuce dakinsa Dakin ya hadu babu laifi
Niko Toilet nashiga watsa ruwa nayi nadauro Alwala nafito nayi shirina ciki kananan kaya
Sallah a zahar nayi sana nayi Addu,oi na Kamal ne ya shigo hanusa dauke da kulolin Abinci karasowa yayi Ida nake yace Haydar ga Abinci!!!
"Murmushi nayi gami da fadi ai dabaka wahala da kanka wajan kawomiba zafito da kaina nadeba naci nifaba bako bane a gidana koka mantane
Kamal yace eh nasan da haka ama ya zama Dole mutu ya karama duk wada yazo gunsa Koda ko bai sansaba
Nace eh kumafa hakane nagode da kullawarku gareni dakaina nazuba Abinci nafaracin baci wani da yawaba naji Abinci yabar kaina
Sakamako wani irin faduwar gaba da nakeji Adu,a nafarayi a zuciyata
Kamal ya lura da yanayina ya canja kallona yayi dauke da damuwa a kan fuskarsa yace Haydar meke damuka ?
Naga yanayika gaba daya ya canja kode mumaka laifine bamu saniba ?
Kamal babu Abuda kuka min tsakanina daku saide San barka
Natsici kainane cikin yanayi nafaduwar gaba jinake Kamar Akwai wani Abu Mara kyau da yake Shirin faruwa Dani
Dafa kafadata Kamal yayi yace Ayyah kayi hakuri Haydar insha Allah babu Abuda zai faru da Kai da yardar Allah kaide kariga Fadi innallillahi wa,inna ilaihir raju,u
Zaka samu sauki a ciki zuciyarka fatamu Allah yasa muji alkairi Amsawa nayi da Amiiin
***********************
Musaba sosai da Kamal kullu ciki kwatarmi da hankali yake
Hakama. Mahaifiyarsa Umma tadaukeni tankar dan,ta da taga na zauna nayi shuru haka zataita tanbayar Mai yake damuna ?
gani yanda shuru nawa yake daga musu hankali sai nake Dane duk wata damuwata domi gani hankalisu ya kwanta
Kullu Ina zuwa lura da Company wani lokaci Kamal yaka rakani nasamu kimani kwana goma a Kaduna ama har yazu Alhaji Yahaya bai samu lafiya ba Wana lamari bakarami daga min hankali yayiba damuwa takara bayana karara akan fuskarta Dan ankai mataki da bazan inya danewaba
Kullu Kamal ciki kwatar min da hankali yake tare da tanbayar maike