Author : Boss Barture Category : Romantic Hausa Novels
zolaya.
Murmushi ya sakar mata, "wlh iya yine irin nawa, kinsan ance sabo turken wawa, ɗan hawan ta da nake yi yasa har na saba da ita.." ya faɗa yana ƙoƙarin mikewa, A hankali ya samu ya tsaya kan kafafunsa, murmushi ta yi mashi, "in shigar maka da kujerar ciki?"
"No, bana so Unaisah tasan na samu lafiya, tafi ji da ni Allah, duk in zata ganni ina gungura kujerar jikinta na 6ari take kamamin ta tura ni.."
Duk da halin damuwar da take aciki hakan bai hana tayi dariya ba, maganarsa ta bata nishadi ashe lambon ciwo yake ma Unaisah.
Bayan ya shiga sitting room din Chief, Jiki asanyaye ta wuce bedroom dinta, tana kallon Unaisah da Batool zaune kan rug, sun baza textbooks dinsu da alama karatu take koyawa Batool, bata bi takansu ba, cikin sanɗa ta wuce don kada su ganta saboda a halin yanzu tafi bukatar kadaici..
Luxury-incense By Sapnah Borno.
Ta kawo muku turarukan wutan su Na maiduguri dana chad, turarukanta masu masifar dadi da kama waje harma da daukar hankali, indai kikayi kabbasa da turaren ta har wajen da kika zauna indai kika tashi sai kin bar kamshin ki, sannan Tana saida mayukan gashi irin nasu na shuwa Arab masu tasirin gaske, wajen gyaran Amare kuwa babu magana dan tazo muku da Chadian and Sudanese dilka Wanda zaki gyara jikinki da kanki, oga ya kasa ganeki, haka zalika akwai wata humrar ta mai suna hana bacci da kuma sirrin shuwa Abun ba magana, yar uwata ki jarraba turaren yar mutan borno nasan zata zame miki best turaren wuta plug. Tanada turarukan da zaki turara gida, toilet, bedsheets, curtains, kabbasa and hair incense ku jarraba kada ku bari ayi babu ku.
Wardrobe balls
Kabbasa spray
Chadian khumra
Hawee
Halud
Gabgab
Sandal sukkariya
Kajinguru
Dilka soap
Ready to use dilka
Karkar oil
Turaren tsuguno
Habil
Dorut
Dorot after period
Brown khumra
Dufr khumra
Body milk
Sudanese kuleccam
Chadian dufr kuleccam
Musk khumrah.
Maganin matan mu sunada inganci Wanda muke kawo su daga sudan, sannan munada maganin karin girman nono, Wanda basuda effects, ga masu bukatar maganin Matsi ko maganin mata Masu aiki garanti munada su, sannan muna zuwa gyaran jikin amarya a duk garin da take
Our Chadian aphrodisiacs are.
Beejay fire
Sata jagab honey
Wetness and sweetness combo
Daka
Great A sabaya
Breast engagement powder
Ciccibi
Gumbar madara
Gumbar dabino
Bita Zaizai
08093772168
*Welcome, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan number din 08103884440*~_____💞______💗_____💘_____🌹______💋_____💫_____🫀___~
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin kaninfari 1k Tsimin dabino 1k Gumba 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 4k
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 maganin Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki
*Daga Alkalamin Boss Bature💋✍️*
Sallamar Taj ce ta katse tasbihin da ya ke yi, A hankali ya buɗe idanunsa da suka kaɗa sukai ja ya dube shi bayan ya amsa mashi sallamar..
Fuskar Taj da damuwa ya zauna kan sofa yana fuskantar sa..
"Haba Owais, har sai yaushe ne zaka fadamin abunda ke damunka? Ko kafi son in yi ta zama cikin damuwa ne? Unaisah ta ce min ka ce za ta ji a gurina kuma nima din ka ƙi sanar dani ba yadda banyi da kai ba..." ya faɗa yana mai nuna 6acin ransa .
Cikin sanyin murya Chief ya ce, "Am sorry, nasan ban kyauta ba, amma ka ƙara hakuri zuwa gobe idan muka shiga meeting zaka ji komai..."
Gyaɗa kan shi ya yi, "Allah ya kaimu da rai da lafiya" ya amsa da ameen
Shiru suka ɗanyi Jimm kowa da abun da yake saƙawa a ran shi..
"Please Owais, duk da bansan meya faru ba, amma tun ranar daka dawo daga yanayin ka na lura babu kwanciyar hankali atare dakai, da akwai wani mummunan abu daya faru, saboda ba karamin abune zaisa ka ki kulamu ba, kuma ka kulle kanka adaki, sannan baka son cin abinci, ka rame, even the chefs have complained about your lack of appetite, pls ka yi hakuri kada ka bari damuwa ta yi maka illa, nasan kai mutunne mai tawakkali, har burgeni ka ke yi saboda jarumtarka, da wuya mutun ya iya gane kana a halin damuwa, sai in tura ta kai bango ne ake iya gane me kake a ciki..."
Murmushi ya yi yana sauraron future in-in law ɗinsa, yana ƙara jin ƙaunar sa a zuciyarsa, da duk wani wanda suke rayuwa a gidan saboda yadda suke nuna damuwa akan shi, suna son shi suna son farin cikin shi, ranar da ya kulle kanshi a ɗaki abun da ya karya mashi zuciya yadda suka dinga zarya a ƙofar ɗakin suna masa magiya don ya buɗe masu, ta ya bazai gode da ni'imar da Allah yayi masa ba?
Sosai Taj yake lallashinsa tare da kwantar masa da hankali,
"Ni bansan da wasu kalmomi zan yi amfani gurin yi maka godiya ba, sai dai ince Allah ya faranta maka kamar yadda ka faranta mini, Allah ya ƙara dankon zumunci da kauna atsakaninmu.." Ya amsa masa da Ameen, fira Taj ya fara jan shi da ita duk dan ya kawar mashi da damuwa ya saka shi nishadi..
"Wa zaka fara aura a cikin su? Ina son in san matsayin ƴata," Ƴar dariya chief ya yi tare da kai hannu ya shafa sajen fuskarshi, cike da jin nauyin shi ya ce, "A rana ɗaya zan aure su." Taj ya ce, "Ban yarda ba, wayo zaka yi mini, kawai ka faɗamin wacece amarya wacece kuma uwargida."
Ƴar dariya Chief yayi, "Nazli ce uwargida saboda ta girmi Unaisah, ina so Unaisah ta ɗauke ta a matsayin yayarta, ta haka ne zasu mutunta juna.."
Murmushi Taj ya yi. "That's a good idea, amma yakamata ka sanar ma Unaisah ba ita kaɗai zaka aura ba."
"I couldn't tell her I left it until the time comes, In sha Allah..."
Kafin Taj ya ƙara magana wayar Chief ta fara ruri, idonsa ya kai kan screen din wayar tasa dake saman table, sunan sheikh Imam Malik ne ya bayyana, janyo wayar ya yi tare da yin picking ya kara a kunnansa...
Bayan sun gaisa Sheikh Imam ya ce mashi ya yi haƙuri ya ji shiru bai neme sa ba, yanzu yana son yin magana da shi in yana free,
Cike da ladabi ya ce toh a ina zai same shi? Bayan ya faɗa masa address din suka yi sallama ya mayar da duban sa kan Taj
"Sheikh Imam yana nema na." Taj ya ce, "Ok, ko zamu iya tafiya tare?" Ya amsa. "Eh."
Duk da baisan ko shi kaɗai sheikh Imam yake son gani ba amma yasan Taj bazai bada matsala ba..
A motar Taj suka tafi, bayan sun ƙaraso apartment building din da Imam Malik yake a parking space suka aje motar, lokacin da suka fito sai ga sheikh Imam ya fito sanye da Jallabiya, fuskarsa da fara'a ya nufe su, cikin girmamawa suka gaisa da shi. "Bismillah, mu shiga daga ciki..."
A apartment living room dinsa suka tsaya, bayan kowannansu ya zauna kan sofa ya miƙe ya nufi ciki, jim kaɗan ya dawo hannunshi ruƙe da ƙaramin tray mai dauke da drinks ya ajiye masu akan table da fara'arsa ya ce, "Sai fa kun yi hakuri, kun zo gidan gwauro, ni nake komai nawa, don ma bana jin dadi ai da har girki zan yi maku."
Murmushi suka saki gaba dayan su.
Chief ya ce, "Da nasan baka da iyali tuntuni dana sa an kawo maka house helpers wadanda za su taimaka maka da ayyukan gidan.."
Ƴar dariya ya yi. "Daka kyauta Owais, amma fa kada ku damu na saba, bana jin wahalar ayyukan gida, tun da safe nake tashi inyi share share da goge goge, idan na gama in kuma girka abun da zan ci.." Waro idanu suka yi Taj ya ce, "Gaskiya ba zamu bari ka ci gaba da zama babu iyali ba, waɗannan ayyukan bana maza bane, a shekarun nan naka hutu kake bukata..."
Murmushi sheikh ya yi, ya ji dadin yadda suka nuna damuwa akan shi.
"Bismillanku,"
Ya faɗa yana nuna masu drinks din, har zai zuba masu, chief ya yi saurin kai hannu ya ɗauki juice ɗin ya tsiyaya masu a cups, kowannan su ya ɗauka ya sha.
"Na ga ku biyu kuka zo, shima yasan komai ne"? A ruɗe Taj yake kallon sheikh da ya yi tambayar...
Chief ya ce, "A'a na bari sai mun haɗu gurin meeting zan sanar da su komai tun da atare muke gudanar da binciken case din, kuma Taj da iyalinsa sun bamu gudummuwa sosai..."
murmushi sheikh Imam ya yi. "Ma sha Allah.."
Shiru suka ɗan yi, da Taj ya lura kamar akwai abun da sheikh ke son ya tattauna da Chief a sirrance sai ya yi dubarar miƙewa tare da curo waya ya ce, "Ina so zan yi waya." amsa mashi suka yi da toh, Ya nufi ƙofa yana ɗangyasa kafa Sheikh ya yi mashi addu'ar ƙara samun lafiya, bayan ya fuce cikin mota ya koma, Benazir ya danna ma kira bayan ta ɗaga suka fara shan soyayya..
"Ya mutanan gidan naku Owais?"
"Suna nan lafiya, Alhamdulillah."
"Baban naku fa?"
"Har yanzu bai buɗe ɗakin ba, Kuma ya ce baya son mu buɗe shi, mu bar shi har zuwa lokacin da muka kama sauran Elders din zai fito da kan shi.."
"Kun yi magana da shi ne?"
Jinjina mashi kai ya yi, kafin ya labarta masa abun da suka tattauna da shi, ya ƙara da cewa, "Yana cin abinci idan muka kai ma shi..."
Shiru sheikh imam ya yi a can kasan zuciyarshi wani irin tausayin rayuwar ahalin Obie ne, dama saida ranshi ya bashi Obie bazai iya guduwa yabar ƴa'yanshi ba koda za'a kashe shi ne da azabtarwa, saboda yasan yadda yake tsananin son su, ta wani bangaren hankalinsa ya kwanta saboda baya son baba Obie ya gudu ya fi son ya tsaya ya kar6i hukuncin da za'a yi masa koya samu sassauci agurin hukuma.
"Owais, Ni ba mazaunin Abuja bane, Idan har ka ganni a abuja to gayyatata aka yi wani muhimmin taro ko wani aiki ya kawo ni, a ranar da abun ya faru na 6oye maku gaskiyar abun da yasa na shiga jikinku, saboda na ga hankalinku ba akwance yake ba, kuma nasan muddin na faɗa zaku ƙara shiga damuwa, shiyasa na ce zan neme ka a waya tun da kai ne jagoran binciken case din nasu.."
Ya ɗan dakata yana duban Owais da ya nutsu yana sauraron shi
"Ban ji daɗi da ya ƙi faɗa maka su wanene sauran ba, amma karka damu in sha Allah zamu dage da addu'a har sai asirinsu ya tonu...."
Numfasawa ya ɗan yi, kafin ya ɗaura da cewa, "Shekara kusan takwas da suka gabata, mun yi babban rashi na abokin mu ɗan kungiyarmu ta malaman ahlussuna, mai suna Malam Jazuli shi da ƴa'yanshi guda biyu. Ya ta6a kira na awaya kafin afkuwar lamarin a lokacin bana a ƙasar, ina a gidan Uncle dina dake a Sudan, a lokacin da ya kira muryarsa babu nutsuwa ya ce shiekh Imam Allah abun tsoro ɗan adam abun tsoro, na ce masa meya faru? Ya amsa min da cewa ya ga abun da ya ɗaga hankalinsa akan hanyar dawowar shi daga Kano, Uziri ya kama shi har ya yi parking motarsa a gefen titi, ya fito daga motar hannunsa ruke da robar ruwa ya ratsa cikin daji don yayi uzirinsa, bayan ya kammala yana kokarin miƙewa ya jiyo kukan jarirai can nesa da inda yake, lamarin ya ɗaure masa kai, ya yi ta mamakin meya kawo kukan jarirai a cikin dajin Allah?
Har zai tafi sai kuma ya ji bazai iya tafiya batare da ya ga a ina kukan nan ke fitowa ba, saboda zuciyarsa ta shiga raya mashi zai iya yiwuwa yada su aka yi ko kuma mace ce me ciki wata ƙaddarar ta afka mata da har ta haife su a cikin daji. Bai yi ƙasa a gwiwa ba, Ya ratsa cikin dajin yana ta mamakin yadda ya iya jiyo kukan tun daga inda yake bayan akwai tazara mai nisa tsakaninsa da inda yake jiyo kukan jariran, ba ƙaramar wahala ya sha ba har ya fara tunanin kodai kukan jariran bana mutane bane, saidai kuma ya kasa haƙura ya koma, yana cikin tafiyar kwatsam ya ƙaraso wani guri mai manya manyan bishiyoyi, duk da marece ya nutsa duhu ya fara bayyana hakan bai hana shi ganin meke wakana ba da taimakon hasken wutar dake ci jikin firewood...
La6ewa ya yi bayan bishiya yana leƙen su ganin manyan mutane zaune saman buzu, kwata kwata babu sutura a jikinsu sai jan ƙyallen da suka ɗaure ƙugunsu da shi, daga tsakiyar shimfiɗar ta su jarirai ne sabuwar haihuwa su biyu kwance saman jan ƙyalle sai tsanyara kuka suke yi kamar ran su zai fita.
Gaba ɗaya ya ruɗe ya rasa gane meke faruwa? Su wanene waɗannan mutanen masu kama da bokaye? Me zasu yi da jariran nan...
Bai ƙarasa zancen zucin nashi ba maganar wani daga cikinsu ta ratsa kunnanshi.
"Me kake nema? Daukaka ko arziƙi ko wani kake so a yi ma sihiri?
Muryar dattijo ya jiyo yana faɗin, "Arziƙi ranka shi daɗe, na gaji da talauci, shekara saba'in a duniya har yau ban mallaki gidan kaina ba, ba ci, ba sha, ba suturar sanyawa ta kirki, mutane har tsangwamarmu suke yi suna kiran iyalina da iyalan faƙiri, so nake ku azurtani ta yadda zan zama hamshaƙin mai kuɗi, shiyasa na kawo maku jariran nan ƴan biyu ne, Jikata ce ta haife su bata san na ɗauko su ba"
Mahaukaciyar dariya suka saka gaba dayansu kafin daga bisani suka ce ma shi ya tashi ya tafi daga rana irin ta yau ya gama talauci a rayuwarsa, duk wanda zai rabesa sai ya yi arziƙi, sannan in akwai wanda ke buƙatar taimakon su, ya haɗa shi da wanda ya yi masa hanya har ya samu ganawa da su." yana faman washe baki ya amsa da toh,
Wani daga cikin dattawan ya ce Sadaukarwar da ya yi ta mallaka ce, In har mutun ya mallaka masu ɗa, koda yana a cikin uwarsa ba a kai ga haihuwarsa ba zasu iya biya masa buƙatarsa, amma fa a bisa sharaɗin koda bayan wanda ya yi sadaukar ya mutu ne sai sun kar6i jinjirin in aka haife sa, kuma basu yarda da asara ba, in suka baka bashi sai ka biya su, dattijon ya amsa da toh..
Hankalin malam Jazuli ba ƙaramin tashi ya yi ba ganin abun yake kamar a mafarki, bayan tafiyar dattijon ya ci gaba da yi masu labe, anan ya ji suna maganar zasu kai yaran kurkukunsu don a raine su.
Ya ce min a lokacin bai ƙarasa jin maganganun nasu ba jikinsa na bari ya baro cikin dajin ya shige motarshi, ya bata wuta...
Abun ya tsaya mashi a rai, sai dai baisan su wanene suke aika aikar nan ba, amma ya ƙudiri aniyar sai ya gano su saboda bazai bari ana aikata fasadi a doron ƙasa ba.
Baisan ya zai yi ba, kullum da tunanin bayin Allahnnan yake kwana.
Bayan wata biyu da dawowarshi Jos, Kwatsam a wata ranar juma'a ya je masallaci yin salla, bayan an kammala yana akan hanyar dawowarsa gida yanata tunani har baisan ya hau titi ba, mota tayi masa horn a ɗan firgice ya ja baya,
Mai motar ya zuge glass ya fara zazzaga mashi masifa yana faɗin bai da hankali ne zai hau kan titi ko shi makaho ne?
A lokacin da ya dubi fuskar mutumin wani irin faɗuwar gaba ya ji ganin tsohon nan fakiri da ya ta6a gani a daji wanda yaje sadaukar da jikokinsa, lamarin ya daure masa kai har ya kasa tanka masa, mamakinsa yadda yayi arziƙi in a short time, saboda motar da yake a cikinta ta kai ta miliyan ɗaya da rabi lokacin.
Haƙuri ya bashi bayan ya tada motar ya tafi, ya ce na yi saurin tsayar da mai abun hawa na ce ya bi mani bayan motar, mai abun hawan ya kawoni unguwar da yake har layin gidan mutumin, nan fa na ga abun da ya kara daure mini kai ganin gidan da motar ta shiga ya haɗu.
Bayan na dawo gida na yi ta tunanin tayaya zan shiga jikin dattijon nan don in gano su wanene waɗannan mutanan?
Dubara ce ta faɗo min tunawa da maganganun da su ka yi da mutanen, nan na shirya kaina cikin yagaggun kaya da suka jikata, na sanya takalma ware daban daban, na yi shigar talaka futuk.
Na je har gidan dattijon nan faƙiri da ya dawo mai arziƙi, na yi masa sallama bayan ya fito na zuƙunna ƙasa na fashe da kuka na dinga rokonsa akan ya taimaka min da abun da zamu ci, Iyalina bata da lafiya ga ciki a jikinta, tun safe nake bin gidajen masu hali don su taimaka mini amma babu wanda ya kula ni don Allah ya taimake