Chapter 70 Reading KURKUKUN KADDARA FINAL STEP BY HAFSAT BATURE BOSS.txt Arewa Novels

KURKUKUN KADDARA FINAL STEP BY HAFSAT BATURE BOSS.txt

Author :  Boss Barture Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   70 / 107

207K to 210K   out of 319.4K words

agidan ta. Natasha ta yi kukan baƙin cikin da bazan iya misalta shi ba, a lokacin da Ummi ke bata labarin yadda Unaizah ta ƙare a gidan kurkukun ƙaddara, ta yi danasanin ƙulla alaƙa da Musa, ta tsane mashi sau ba adadi, gaba ɗaya ta ji rayuwar duniya ta sire mata, musamman da ta karanta wasiƙar Unaizah da Ummi ta bata, baƙin cikinta Unaizah ta mutu da tunanin harda ita Musa ya ci amanarta, bayan ita batasan komai ba. A ranar saida Ummi ta yi tunanin Natasha bazata rayu ba, saboda yadda ta dinga fasa ƙara tana fitar da gumi akan fuskarta, ta dinga lallashinta tana roƙonta akan ta yi haƙuri abun da ya faru ya riga da ya faru, yanzu haka Musa yana a hannun hukumar Isod zasu kai shi kotu, amma ina Natasha ba ta fahimtar komai...


~___________________________________🔥💫~


*ISOD HEADQUARTER*


*DG OWAIS💪🔥*


Yana a tsaye gaban ƙofar shiga Cell, a hankali yake danna code ɗin ƙofar, bayan da ta buɗe ya shiga daga ciki,


Wa zan gani idan ba Ɗan iya ba,


Yana a kwance kan floor kamar mushen jaki, warinsa ya cika cell din, 6arin mazaunansa ya ƙone fatar duk ta sa6ule jawur ba ƙyan gani, sakamakon ƙonewar da ya yi, badan ana yi mashi treatment ba da tuni naman wurin ya ru6e, amma da yake basu son su mutu sun fi so su fara girbar abun da suka shuka tun a gidan duniya shiyasa suke duba lafiyar shi, kwata kwata babu gashin gemunsa ya ƙone ƙurmus, yatsunsa duk sun lankwashe sun ƙone, ko sutura babu a jikin shi sai ɗan pant ƙarami irin na mata, sai nishin azaba ya ke saki, daga gani yana jin raɗaɗi ba kaɗan ba, cikin fitar hayyaci ya ke yin sambatu yana fadin, "Wayyyo Allah na, Wayyo na shiga uku na baniiiii, na baniiii, na baniiiiii na lalace, jikina zafi, ku sosa min bayana, ku sosa min ɗuwawuna ƙaiƙayi nake ji, ku cire min ciwon jikina, zan mutu..."


Girgiza kai Owais ya yi ko kaɗan bai ji tausayin shi ba. A hankali ya zauna kan kujera tare da ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya yana kallon shi.


"Baka ga komai ba Dan Iya, wannan somun ta6i ne na daga azabar dake tunkaro ka, ko ka manta rayukan da kuke ƙonawa da fetur? Ya ka ji raɗaɗin na raunin jikin ka?"

Da ƙyar ya iya juyo da kansa ya dubi Owais da idanunsa da suka kaɗa jawur kamar jan gauta, hancinsa sai tsiyayar da tsinkakkar majina yake yi gwanin ban ƙyama.


Ƙaton le6en nan nasa ya ƙonu da wuta ya yi sumtum kamar ganda.


Daga gani yana jin azabar radadi ta ko'ina a jikin shi.


Muryarsa ma bata fita, guragura ya ke magana..


"Ba dati, na tuba, ku min rai, na gane kushkurena, Ku kai ni asibiti su cire min ciwon jikina, su canza min wata fatar, don Allah..."


Ƙyalƙyacewa da dariya Owais ya yi, duk da ƙyanƙyaminsa da yake ji, maganarsa ta bashi dariya.


"Sai da Lokaci ya ƙure maka, ka ga asirinka ya tonu baka da mafita tukunna zaka tuba? La'anannen Allah, azzalumi mai safarar ƴa'ƴan mutane ya kai su inda za'a azabtar da rayuwarsu, tayaya kake tunanin mu zamu yafe maka? In banda ma kai ɗin wawa ne jaki, kamar yadda baku da imani baku da tausayi, kuma baku iya yafiya ba, muma haka jami'ai muke akan mugaye irin ku, bamu da tausayi, idan muka fara azabtar da su sai sun ɗanɗani kuɗar su.."


ya ƙarashe maganar cikin fushi tare da bugun gaban table ɗinsa.

Fashewa da kuka Ɗan iya ya yi, nan take ya fara 6urkuta tusa da fitsari daga kwance, DG ya yi saurin zaro hanky daga aljihunsa ya toshe hancin shi, cike da jin ƙyanƙyami ya furta, "Abun ƙyama, yanzu ina tsafin nan naka? Da bakin ka? Suna ina? Ko zasu iya taimakon ka?" Ya faɗa yana ɗage masa gira.


Fashewa ya kuma yi da wani kukan, bakinsa har ya fara fitar da jini,


"Ka daina bana son ji, ka rabu da ni inji da abun da ke damuna, ka kira min matata da ya'yana su zo suga halin da nake a ciki..."


"Su yi maka uban me idan sun zo? Ka yi tunanin kana da wani dangi ne da ya rage maka? Matarka da ya'yanka sun ji komai da ya faru, sun tsanake saboda ka ja masu abun kunya, ka bar masu mummunan tabo a matsayin gadonsu, wulaƙantacce! ....."

Alkalamina bazai misalta tashin hankalin da Ɗan iya yake a ciki ba, wata irin wutar baƙin ciki ce ke ci a cikin zuciyar shi.



"Ban zo don na sawwaƙe maka radadin da kake ji ba, na zo ne don in tambayeka menene alaƙarka da Abdallah Muhammad Buzu, kuma su wanene ƴa'ƴansa daka sadaukar a kurkukun ƙaddara? Kada ka ce zaka yi min ƙarya! na riga dana san komai, kaine mugun da ya damfare sa ya kar6e masa jarirai har biyu!"


(Abun ka ga jami'i mai kaifin basira, bai nuna hasashe yake yi akan shi ba, saboda yasan ɗan iya shine leader na bangaren safarar ya'yan mutane na nan Nigeria zuwa kurkukun ƙaddara. Bayan haka salon yadda yake damfarar mutane ya 6oye fuskarsa da mask ya yi shige da mutumin da malam Jazuli ya bada labarinsa, uwa uba sunan da Abdallah ya faɗa a matsayin sunan sa wato Ja'afar Dila, toh Ja'afar din asalin sunan shi ne da ba kowa ya sanshi da shi ba, saboda nickname ɗinsa ya boye asalin sunan sa, ta haka Owais ya gane shine ya damfari Uncle Abdallah, bayan da Taj ya labarta masa komai."



Mugu da yake shaiɗaniyar zuciyar na nan, yana huci yace, "Banshan wa kake magana akai ba, ni banshan wani Abdallah Muhamamd buzu ba, babu wasu ya'ya nashi dana sadaukar, duka ƴa'yan nawa ne."

"Kada ka yi min ƙarya, ka duba halin da kake a ciki, wlh in baka faɗamin gaskiya ba zansa a shafa maka ruwan attarugu a jikin ka.."

Yawu ya haɗiya yana faman zare na mazurai ya ce, "Na san shi, shima member ne na kurkukun ƙaddara, shi ya sadaukar da ya'yan shi da kan shi, bani na sadaukar mashi da ya'ya ba, na rantse maka da Allah ban damfare sa ba..."


Cikin fushi Owais ya ce, "Ba zaka daina yi min karya ba? Ko so kake in aiwatar da abun da na fada?"

Ya ƙarashe maganar tare da kanga wayarsa a kunne, "Ku shigo min da ruwan attarugu cikin cell din Ɗan Iya..." Tunkan ya ƙarashe maganar ɗan iya ya dabarbarce cikin razana ya shiga zayyana mashi komai.


"Ka sadaukar da ya'ya talatin, na ga sunayen su, amma tayaya zan iya gane su wanene ya'yan Abdallah Buzu a cikin su? Ya ce min su biyu ne ya baka? Suna a raye ko sun mutu?"


Yana faman sakin tusa ya ce, "Haris da Deeja..."



Ajiyar zuciya Chief Owais ya sauke, dama saida ranshi ya bashi sune saboda akwai kamannin Abdallah a tare da su.



"Ka taimaki kanka Ɗan Iya.." Yana faɗa ya miƙe ya fuce daga Cell din.


*~_______________________________~Flashback 🥺*



*BARI MU KOMA BAYA MU JI MEYA FARU A TSAKANIN DAN IYA DA ANA A RANAR DA AKA NEME TA AKA RASA❗❓*



Bayan tafiyar su gidan hajiya Adama, ya rage saura Ana kaɗai a cikin gidan, gyara gidan ta fara yi goge goge da share share, bayan da ta kammala bata huta ba, gashi ta gaji sosai, amma a haka ta koma kitchen ta ɗaurawa Baby Junaid Cherie don tasan da ya dawo zai fara neman abinci..


Ta kuma ɗaura girkin abincin rana, tsawon awanni tana zarya zuwa kitchen gurin duba girkin da ta ɗaura..

Idan ta ga komai daidai saita koma falo ta ɗan huta, dama da wayarta a hannunta da take chatting da sisters din ta, hakan yasa kaɗaicinta ya ragu. Hankalinta ya fi kwanciya ganin babu mai takura mata a gidan, mutumin da ta tsana fiye da mutuwarta, ko gifcinsa bata son gani saboda cin zarafin da yake yi mata, ya addabeta, shine silar damuwarta, kullum cikin fargaban shi ta ke..


A lokacin bata kawo komai a ranta ba, bayan da ta gama girkin lunch din ta kashe gas ta nufi bedroom din ta, ganin ɗaya ta yi yasa ta shiga toilet ta ɗauro alwala, ta ɗauko hijab dinta da take ta 6oyonta don kar a ganta a gane ta musulunta ta zura ta a jikinta, kafin ta kabbara sallar a tsanake, da ta kammala ta zauna ta fara kai kokenta gurin Allah.


Cikin ƙanƙan da kai take cewa, "Ya Allah, Ka fidda ni a halin da nake a ciki! Ka fi kowa sanin halin da baiwar nan taka take a ciki, ni bazan iya da shi ba, amma nasan kai zaka iya da shi, Ya Allah, ka kare ni daga sharrin Ɗan Iya, na tsani abun da yake yi mini, na tsane sa, ina jin zafin najasar da yake goga min a jikina! Ya Allah Ka raba ni da shi, Ya Allah ka tona masa asiri..."


Kuka ne ya 6alle mata, tana jin ciwon abun, yadda yake nuna mata fin ƙarfi, ya ci zarafinta, kuma ta kasa tona masa asiri, saboda tasan kota faɗa ba yarda za'a yi da ita ba, bayan haka a duk lokacin da ta yi gigin tona masa asiri sai ta ji kamar an shaƙe makoshinta, bayan haka ya yi mata barazanar zai kasheta in har ta faɗa ma wani abun da yake yi mata..

Addu'o'inta duka akan ɗan iya ne..


Ciwon kai ta fara ji, A hankali ta kwantar da kanta saman darduma, bacci mai daɗi ya yi awon gaba da ita..

Almost 1 hour tana sharar baccinta, kwatsam knocking din kofa ya farkar da ita, a dan firgice ta farka, gabanta na faɗuwa ta miƙe, ta yi zaton ɗan iya ne shiyasa duk ta sha jinin jikin ta, cike da zullumi ta furta, "Wanene?"

"Your husband to be..."


Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke jin muryar Mahboob..

Da sauri ta cire hijab din jikinta ta daura kan gado, kafin ta je ta buɗe masa ƙofar..

Idanunsu na shiga cikin na juna, ta yi saurin sakar mashi murmushi, tare da mayar da idanunta akan j
Junaid da ya goyo a bayansa ya yi nisa a baccinsa.

"Me ya ke damunki ki ne? Na ga idanunki sun yi ja?"

"Wataƙil don na yi bacci ne" Ta bashi amsa da fara'arta.

"Ina mutanan gidan suke ne ko har sun tafi ne?"

"Sun tafi tun ɗazu, ni kaɗai ce a gidan... " ..

"Okay, ya faɗa tare da janyo Junaid daga bayan shi ya miƙa mata, "Take care of his excellency, ki kwantar da shi, idan ya tashi daga bacci pls ki yi mashi wanka, ki bashi abinci..." Murmushi ta yi shima ya yi mata murmushin.

wani kallon ƙauna suke jefawa junansu.

Bayan ta kar6i Junaid ta rungume shi a ƙirjin ta..

"Your command is my wish, amma kai ba zaka ci abincin ba? Ko baka jin yunwa..."


Girgiza kai ya yi, "Sauri nake yi zan tafi kallon match, bana so na yi missing, idan na fita zan biya gidan abokina zan ci abincin acan..."

Har ta buɗe baki zata ƙara furta kalma, ya yi saurin ruƙo yatsanta me sanye da zoben da ya bata ya manna mata kiss, ta saki baki cike da mamaki, ya ɗago tare da kashe mata ido ɗaya, "Take care of your self." Ya faɗa tare da juyawa cikin sauri, har ya kusa fucewa daga falon ya ji ta ƙwala masa kira,

"MAHBOOB" Faɗuwar gaba ya ji, a hankali ya waiwayo tare da daura idanunsa akanta, murmushi ya ga tana sakar mashi, "Lafiya ? Ya tambaya"ko akwai wani abu da ki ke son faɗa min"? Ya faɗa yanayi mata murmushi.

Girgiza kai tayi, "No, ka yi min kyau ne." Bai furta kalma ba, ya ɗaga mata hannu tare da sakar mata murmushi ya fuce.


Ji ta yi kamar tabi shi ko ta roƙe shi ya dawo ya zauna saboda faɗuwar gaban da take ji.


Fitowa ta yi daga dakin, ta nufi ɗakin Anila, tana kokarin kwantar da Junaid kan gado ya farka da rigimarsa yana ambaton sunan Mommy, koda ya ji muryar Ana sa'ilin da take lallashinsa nan fa ya fara kuka yana fadin shi mommy yake son gani, gurinta zai je,.


Lallashin shi ta yi da wayou da dubara ta ce, "In har kana son ganin mommy, ka yi shiru ka daina kuka, zan kawo maka abinci ka ci ka ƙoshi, idan na yi maka wanka sai mu bi su anguwa.." Yana faman yamutsa fuska da shagwaba ya ce, "To ina suka je, shine ma ta tafi ta barni.."


"Suna a gidan mommy Adama" tur6une baki ya yi..
Dakyar ta shawo kanshi ya yi shiru,

Ta miƙe da sauri ta je kitchen ta zubo masa cherie a plate, ta haɗo masa da juice ta kawo masa, da kanta ta zauna tana bashi yana ci, bayan da ya gama ta mayar da kayan abincin kitchen..

Ta dawo dakin, cire masa uniform dinsa ta yi, ta ɗauke sa suka shiga toilet, bayan ta gama masa wankan, ta fito da shi, jikinshi ɗaure da towel,
tana ta tunanin ya zata yi da shi? Gudun kar ya saka mata kuka in ya ga ta ƙi kai shi gurin mommynsa. cikin sa'a taga ya kama bacci, murmushi ta yi tare da kwantar da shi kan gado.

"Baby Junaid, asha bacci lafiya, ni ma bari na je na yi wanka, don nasan idan ka farka ba zaka barni in yi ba.."

Juyawa ta yi da sauri ta fuce daga ɗakin ta koma nata ɗakin ta shiga bathroom don ta yi wanka.

Bayan da ta shiga ciki, fara tu6e kayan jikinta ta yi ta ɗaura towel ta kunna shower, har zata zame towel din ta tuna da mahboob, murmushi ta yi tana tuna murmushin da ya yi mata kafin ya tafi, shagala ta yi da tunaninsa, har ta manta da abun da ya kawota toilet ɗin.

Kwatsam! Yanayin bugun zuciyarta ya sauya, ta dinga jin kamar wani abu zai faru da ita, fasa wankan ta yi ta mayar da kayanta ta fito da sauri don ta dubo baby Junaid, cikin sauri take tafiya, har ta kusa ƙarasawa ga bedroom din Anila kwatsam ta ji motsin mutun a cikin kunnanta, kwata kwata bata ga lokacin da ya shigo ba, ga dukkan alamu bata ƙofa ya shigo ba, ya yi tsafinsa ne, wata razana ta yi gabanta ya shiga faɗuwa, kwata kwata Allah bai nuna masa ita ba, ya wuce ya nufi bedroom ɗinta, Hankalinta idan ya yi dubu toh ya tashi, tun da ta ga ya nufi bedroom dinta tasan cewa ita yake nema, akan idon ta ya fito ya nufi kitchen ya ga babu ita, ya shige can ciki yana bin ɗakuna tare da kwaɗa mata kira da buɗaɗɗiyar muryarsa Ana, Ana


cikin sanɗa ta lalla6a ta shige ɗakinta ta datse kofar, ta ɗauko wayarta jikinta na kerma kaf kaf ta shiga camera, ta saita fuskarta.

Daurewa ta yi cikin ƙarfin hali ta fashe da kuka mai tsuma zuciya tasan ba lallai ta rayu ba.

_Na yi maku wannan video don in bayyana maku halin da nake a ciki, ina ji araina kamar wannan ce dama ta ƙarshe, nasan kun kyautata mun a rayuwa, kuna so na, mun shaƙu da juna, amma ba lallai kowan nan ku ya yarda da abun da zan faɗa ba, nima bada son raina ba, bazan jure fasiƙanci da yake aikatawa da ni ba, in har ban tona masa asiri ba, zan haɗiyi zuciya ne na mutu saboda baƙin cikin shi, bakowa nake magana akai ba face Uncle Ɗan Iya, ya kasance yana kwanciya da ni a duk lokacin da nake tsaka da yin jinin al'ada, ban ta6a sani ba, sai dai in farka inji raɗaɗi a gabana, abun yana damuna amma saboda ban san meke faruwa da ni ba shiyasa ban kawo ma raina mutunne ke saduwa da ni ba, ina ganin abun kamar a mafarki ya ke faruwa, nama yi zaton aljanu ne, shiyasa a lokacin da damuwa ta mamaye zuciya ta, na yi duhu na rame, duk kuka nuna damuwa akaina na kasa fayyace maku komai saboda bansan amsar da zan baku ba. A ranar dana musulunta, a ranar na gano wanene ke yi min hakan, ina a kwance ya afka min da tsakar dare kamar yadda na saba gani a mafarkina, da ya ga na ganshi zan fasa ihu sai ya toshe min bakina ya hana ni yin magana, na yi kukan baƙin cikin da ba zai misaltu ba, ban ta6a zaton zai yi min haka ba. Ina ganin girmansa ina ganin mutuncin ahlinsa da suka zama majinginata, a lokacin na yi kokarin in fasa ihu ko in bangaje shi don in gudu amma ya sanya min ƙarfi, ya yi min sihirin da jikina ya mutu na kasa motsawa ya kwantar da ni kamar matatta ya biya buƙatarsa da ni, ban tashi farkawa ba, sai washe garin Allah, cikin mawuyacin hali na yi wanka na yi sallah, na kasa tunkararshi saboda ina kokwanton in shine ya yi min hakan a zatona jinni ne ya bayyana da suffarsa, amma daga baya na gano shine shaiɗanin da kan shi, batare da sanin kowa ba na je har ɗakinshi da niyar in zazzaga mashi masifa in kuma yi masa iyaka da kaina, amma koda na je na gama 6a6atun bakina na kuma ce zanto na masa asiri sai cewa ya yi, ina tunanin zan iya tona masa asiri? Idan ma na faɗa ma mutanan gidan wa nake ganin zai yarda da ni? Bayan ni ɗin bakowa bace, bare ce ƴar aiki ƙasƙantacciya mara galihu, zai fi in shiga taitayina shi mutunne mai haɗarin gaske yana da tsafi a jikin shi, komai nake yi yana kallona, in har na ƙara furta zan tona masa asiri, ko na yi gigin faɗama wani abun da ya ke yi min, da ni da wanda na faɗamawa zai haɗamu ya kashe. Bani da mafita, sarrafa ni yake yi da sihirinsa, ba irin magiyar da ban yi masa ba akan ya tausayawa rayuwata, ya daina aikata fasiƙanci da ni, shi fa musulmi ne kuma yasan babu kyau, namiji ya kusanci macen da ba muharramarsa ba! Haramun ne, ko don saboda mutuncinsa da na iyalinsa ya rufawa kansa asiri ya ƙyale ni, in ba haka ba zan gudu in bar masa gidan, bayan na tona masa asiri...

Ba irin barazanar da ban yi masa ba, amma ya ƙi saurare na.

70 / 107