Author : Boss Barture Category : Romantic Hausa Novels
masu addu'a kamata yayi mu bar ma Allah sauran, in sha Allah zai duba kokenmu kuma zai kawo mana mafita.." Kwantar mata da hankali ya yi har saida ya samu ya shawo kanta.
Shiru suka yi, idanunsu akan fararen agwagin dake yawo cikin garden pool din gaban su.
"Akwai abun da ban faɗa maki ba, saboda bana so kiji ba daɗi..." bai ƙare maganar ba, ta katse shi da cewa, "Ka auri yarinyar da ta ceci rayuwar Angel ɗina?" Da mamaki ya dubeta, "Tayaya akai kika sani?" murmushi ta yi, "Jiya bayan mun fita yawon shaƙatawa, lokacin da zamu dawo, da aka kira magrib ka shiga masallaci yin sallah ka barni a mota, an kira wayarka, dana duba screen din sai na ga suna ya bayyana My Danejo, na yi picking call din anan na ji tana faɗin ta ji shiru shiru har yau baka dawo gida ba, bayan ka faɗa mata kun dawo daga kai farmakin, dan Allah ka dawo ta yi missing ɗinka.
Ban ƙarasa sauraronta ba na yi rejecting call din saboda kishin da ya turnuke zuciyata, amma ko bayan daka dawo ban bari ka gane halin da nake a ciki ba.
Bayan na dawo gida, ko dinner ɗina ban ci ba, na ƙumshe a ɗaki na ci kuka na, saboda raina ya bani kana da aure ka boye min ne, jiyan nan kasa bacci na yi, ina jira washe gari ta yi don in kiraka in tuhume ka akanta, da damuwa ta ishe ni na fito daga ɗaki, kwatsam na ga Yaya Shureim yana ta sauri zai fuce daga falo na je na tare shi anan yake faɗa min Aisha ta kira tana neman shi..."
tun da ta fara magana yake kallon cikin idanunta, a jiya daka bamu labarin abun da ya faru da kai, anan ne na ji irin taimakon da bafullatanar dajin nan ta yi ma Unaisah, kuma na ji ka ambaci sunanta Danejo, duk da baka bamu labarin da ita ka dawo ba, ko kun yi aure amma ni na gane itace wadda ta kira ka a waya, saboda hausarta bata ƙware ba, ina ji na gane bafullatana ce, nan take na gane kuna a tare.
"Ummu Unaisah am sorry idan baki ji dadi ba, na aureta ne saboda ta so ni, kuma iyayenta ne suka damƙa mani amanarta saboda ta nuna bazata iya rayuwa batare da ni ba, bayan haka a lokacin bani da zabi, nima ina sonta saboda kyautatawar da ta yi ma ƴata da kuma ni, kuma nasa ma raina ba zaki ta6a dawowa cikin rayuwata ba..."
A taƙaice ya labarta mata komai da ya faru tun daga farkon haɗuwarsa da Danejo...
Ajiyar zuciya ta sauke, kwata kwata bata ji kishi ba tun da ta gane ita ce bafullatanar da ta taimaki Unaisah.
"Taj, ka yi abun da ya dace, in ma baka aureta ba ni zansa ka aureta ne, saboda ta hakane kaɗai zamu iya rama mata halaccin da ta yi mana, da ba don Allah ya ƙaddara faɗawarta cikin ruwa ba, da yanzu babu Unaisah. Inason me son ƴata, don haka, bazan yi kishi da Danejo ba, zan dauke ta kamar ƙanwata." Kalamanta sun faranta ran shi..
"Allah ya yi maki Albarka Ummu Unaisah, Allah ya bayyanar mana da ya'yan mu."
"Ameen..."
"Idan Allah Ya maido mana su Unaisah lafiya, ka kaini part din ka in ganta."
"In sha Allah" Daga haka suka yi shiru..
Yanzu dai gaba daya kowa jiran tsammani ya ke yi! Kusan sau hamsin Taj yana kiran Chief wayar bata shiga, ya ƙagara ya ji meke faruwa? Sun yi nasarar gano su ko kuwa har yanzu❓
Gaba ɗaya ko wani ahali daga cikin su haka suka wuni da fargaban a wani hali yaran nan suke a ciki, tun jiya da dare ba ci ba sha, ruwan tea din da suka sha lokacin da suka yi nafilfili ne kaɗai ya rage a cikin su..
Abu kamar wasa, har dare ya yi babu labari dangane da su, Hajiya Layla da Alhaji Ubaid da marece suka bar gidan Owais, sakamakon kiran da Hajiya Sarah take ta yi masu game da rashin dawowarsu gida, kuma sun barsu cikin fargaba.
Kusan gaba ɗayansu suna a falo cikin damuwa, kowa ka kalli fuskarshi babu annuri bacci suke ji amma damuwa ta hana baccin ya ɗauke su, sun kasa sun tsare sai sunga dawowar ya'yansu, sheikh Imam ne ke tausarsu da nasiha mai ratsa zuciya, Taj ne kaɗai baya a falon bai daɗe da fita ba ya je ya kwantar da baby Junaid.
Benazir da Aisha da Anila suna a zazzaune kan rug sun zabga tagumi suna sauraron Sheikh Imam, yayin da Dr Shureim ya ke a gefen shi, shi kanshi Imam malik din ba ƙoshin lafiya ne da shi ba, har yanzu yana jin ɗacin abun da Musa ya yi mashi a ranshi, ya yi masa abun da har abada ba zai manta da baƙin cikin nan ba, amma ya fawwalawa Allah, kuma baya son rauninsa yasa suma su shiga damuwa ko dan saboda alkawarin da ya yi ma Aisharsa.
~______________________________~
A bangaren gidan ɗan iya, bayan komawar su Abie, a falo suka iske mutanan gidan sun zabga tagumi, sunyi kukan har sun gaji sun godema Allah, baƙin ciki da damuwa sun hana su sukuni.
Zahra ma bata da lafiya, tun bayan da lamarin ya afku zazza6i ya lullu6eta, ta dinga amai har daga kwance..
Mahboob ma kamar baya a cikin hayyacinsa, firgita ya ke ta yi, haɗi da sambatu yana ambaton Ana ta mutu, daddynsu ya kashe Ana, shima mutuwa zai yi,.
Baiwar Allah Mami duk da halin bakin cikin da take a ciki ita ke ƙoƙarin lallashin su, sai dai duk da hakan ta gaza shawo kansu, sun ƙi cin abinci tun jiya har yau.
Lokacin sallamar Abie ta katse su, Mami ta shiga faɗa masu halin da suke a ciki, ta ce su taimaka mata ta shawo kansu, bata son ta rasa ƴa'ƴanta, abun zai yi mata yawa..." Wlh kasa magana suka yi saboda tausayin su, fargabansu ma kada su ji sauran miyagun ayyukan da ɗan iya yake aikatawa, watakil zaucewa za su yi..
Daƙyar suka lallashe su, Abie ya taimaka ma Mahboob ya yi wanka, itama Mami ta shiga da Zahra ɗaki tasa ta yi wanka,
daga bisani ummi ta shiga kitchen ta girka masu wani abincin, don wanda suka bari na jiya tuni ya lalace.
A tray ta shirya abincin ta kawo masu a falo, gaba ɗaya suka kasa cin shi, suka dinga tausarsu suna lallashinsu akan su yi hakuri da abun da ya faru don ya riga da ya faru, basu isa su canza abun da Allah ya ƙaddara faruwarsa ba, tsakaninsu da Ana addu'a ne Allah Ya jikanta da rahama, Allah Ya bi mata hakkinta. Cikin kuka Zahra ta ce da wannan baƙin cikin da ya ƙunsa masu ƙwara mutuwarsu, wai mahaifinsu ne yake aikata fasikancin nan? har ya iya kashe rai? Anya shi ya haife su? Ko dai musayar uba aka yi masu?
basu ta6a ganin 6acin ran Zahra irin na wannan lokacin ba, zuciyarta a wuya take.
Ummi ta ce,"Zahra, mu daina yaudarar kan mu, ni na dawo daga rakiyar ɗan-iya, wlh shi ya aikata, zai iya komai don ya samu duniya, Allah ya isa tsakaninmu da shi, wannan abun kunya har ina! Allah ya sa jami'ae su kama shi, su hukunta shi daidai da abun da ya aikata."
Da ƙyar suka shawo kanta har suka samu ta yi shiru, abincin ma basu iya cin shi da yawa ba, kaɗan suka ɗan tsaƙura.
Bayan sun gama Mami ta ɗauko mata maganin zazza6i ta sha, cikin sa'a bacci ya ɗauke su daga ita har mahboob din da ke ta sambatu.. 🥺
*SHIN INA ALHAJI MUSA YA GUDU DA UNAISAH DA BATOOL, SUNA INA❓*
~______🔥_______🔥_____🔥______~
A hankali ta soma dawowa cikin hayyacinta bayan gushewar da hankalinta ya yi na wucin gadi, bata san inda kanta yake ba sai yanzu da Allah ya farfaɗo da ita.
Wani irin zafi ne ya taso mata, zufa ta soma tsattsafowa ta saman fatarta, a wahalarce take jan numfashi saboda ƙarancin iskar da zata shaƙa, dukkan ilahin jikinta rawa yake yi ga wata irin matsananciyar kasala da ta haifar mata da rashin kuzari, tana ta ƙoƙarin buɗe idanunta sai dai ta kasa tsayar da su a buɗe saboda kasalar da take ji, cikin raunanniyar murya take sambatu tana ambaton sunan Batool, Batool saboda ita ce aranta.
Kwata kwata batasan a ina take ba, saboda bata iya tuna komai da ya faru a baya, kamar ta yi loosing memory ɗinta.
Ƙarar sarƙoƙi sun cika kunnuwanta, Kacacau! kacacau!! babu daɗin ji, ta rasa daga ina sautin ke fitowa, gaba ɗayanta a takure take cikin matsi, ta kasa motsawa.
"A ina nake ne? Meyasa bana iya ganin komai sai duhu? Waya kashe hasken ɗakin?" Sautin muryarta daƙyar yake fita a wahalce, kaɗan take iya buɗe idanunta tana gani biji biji.
ta shiga ruɗani sosai ga tsoro da ya mamaye zuciyarta, kwata kwata bata kawo ma ranta cewa ba a gida take ba..
"Ko mafarki nake yi? Ko na mutu ne ina a cikin ƙabari?" A cikin zuciyarta ta furta..
"Ya Allah ka kawo min dauki! Ka fiddani daga cikin duhun nan!"
Har saida ta fidda rai da za a tanka mata, ta yi shiru tana jan numfashi.
Kwatsam a lokacin da ba ta yi tsammani ba, sai ga wani siririn haske yana ƙoƙarin mamaye gurin da take, cikin ƙanƙanin lokaci hasken ya karaɗe ilahirin gurin, tamkar da rana, runtse idonta ta yi saboda hasken da ya kashe mata ganin ta.
Lokacin da ganinta ya washe ta buɗe idanun a hankali, kaitsaye suka sauka akan bangon da take fuskanta, wa'iyazubillah! Wata irin firgita ta yi jikinta ya hau yin kerma kamar wadda sanyi ya kama, ta yi matuƙar razana, tsigar jikinta ta dinga tashi, gabanta ya shiga faɗuwa kamar ana buga gangunan yaƙi..
A wani babban ɗaki take mai kama da mayanka, koma in ce mayankan ce, gaba ɗaya bangwayen ɗakin ƙugiyoyine na ƙarfe sargafe da sassan jiki, kamar na mutun kamar na dabba, kuma daga gani sabuwar yanka ce duba da yadda jinin ya wanke ƙasan ɗakin da jikin bangon jawur, kaitsaye yake bin wasu siraran hanyoyi izuwa cikin magudajinsa, wani abun tashin hankali da firgitarwa wasu gungun ƙosassun ƙwari ta gani dadda6e da naman sunata tsotse jinin da ke a jiki, ta ƙara zazzare idanunta cikin ruɗu da tashin hankali.
Daga tsaƙiyar ɗakin dogon teburin yanka ne na karfe duk jini a jikin shi har ɗiɗɗiga ya ke yi a ƙasa..
Bakomai bane a saman table din fa ce kayan aikin yanka, wuƙaƙe, gatari, adda da tsinken ƙarfe jikin su duk jini..
fashewa tayi da kuka tamkar ranta zai fita, ta tsorata sosai, hankalinta ya tashi matuƙa, ta rasa gane mafarki ne take yi ko a gaske ya ke faruwa.
Kwakwalwarta nema take ta zauce, cikin shesshekar kuka take ambaton sunayen su..
"My man, Chief, daddy! Aunty Ummi, Batool, wayyo Allahna na shiga uku, Meke shirin faruwa da ni? Wani zunubi na aikata dana tsinci kaina a cikin wannan mummunan mafarkin, idan bacci nake yi ya Allah ka farkar da ni! Bazan iya jure ganin tashin hankalin nan ba, mutuwa zan yi..."
bata ƙare maganar ba, ta tsinkayi kakkausar muryarsa a cikin kunnanta. "Welcome back to the Prison of Destiny."
Wani irin bugun barazana zuciyarta ta yi, ta shiga rarraba idanu tana jiran ganin wanene ya yi magana? ta ina zai 6ullo, sunan kurkukun ƙaddara da aka furta ya fi komai ɗaga hankalinta, Hasbunallah! ƙwaƙwalwarta ce ta fara kokarin tariyo mata komai da ya faru...
_"Ki yi bankwana da su, wannan ita ce ƴarku ke da Shureim, shine hallacin da zan iya yi maki na ƙarshe kafin rabuwar mu..."
bata ƙarashe tunanin nata ba, kwatsam ta ga mutun ya bayyana a tsakiyar ɗakin jikin shi sanye da alkyabba ja mai hula, bata iya ganin fuskarsa ba saboda ya bata baya.
"Wanene Kai?" Ta tambaya a tsananin tsorace.
"Mutuwar ki ce!"
Cikin ƙarfin hali ta ce, "Ba'a ganin mutuwa, ka faɗa min wanene kai, meyasa kuma ka kawo ni nan?"
Juyowa ya yi tare da fuskantarta, rabin fuskarsa a rufe yake da mask, jajayen idanunsa kaɗai take iya gani.
Bai tanka mata ba, har sai da ya matsa gaban ta, tukunna ya zuƙunna.
Cike da fargaba take duban shi, kwata kwata bata ji tsoron shi ba ta dai sha jinin jikin ta.
A hankali ya sanya hannu ya zame mask ɗin fuskarsa, wata zabura ta yi a gigice kamar zata shige ma bangon bayanta, ganin fuskar mutumin da take nema ruwa a jallo sai gashi yau Allah ya haɗa su, gata ga shi, face to face eyes to eyes nan take ta tuna da komai da ya faru, Ya Ilahi! nan take ta gane a cikin gidan kurkukun ƙaddara ta ke.
Cikin rawar murya ta shiga furta, "Allaziina iza asabat'hum museebatun ƙalu 'Inna lillahi Wa'inna ilaihirraji'un, A'uzu Billahi Minasshaidanin Rajim. La'haula Wala quwwata Illah billah,
Ƙarfin halinta ya bashi mamaki, baisan ya a kai ya tsinci kan shi da yin shu'umin murmushin nan nashi ba, ta ɗaure masa kai, ido cikin ido take furta addu'oin nan batare da jin shakkar shi ba.
"Ko ɗan jarida bai kai ki haɗari ba, yar mitsila dake kamar in matseki a hammatata, da nasan zaki zamar mana annoba da tun lokacin da Ubanki ya zo neman auran Uwarki ban goyi bayan kakan ki ya bashi auranta ba, komai da ya faru kece sila, fitinanniya..." Ya faɗa ransa a 6ace kamar zai rufe ta da bugu.
"Ya Allah, Ka raba ni da mugun ji da mugun gani, Ya Allah bazan tambayi meyasa ka jarabce ni da haduwa da wannan fasikin mutumin ba, wanda zuciyarsa babu imani da tausayi a cikin ta, sai zallar mugunta da zalunci, mutumin da ko maƙiyina bana masa fatan ya yi mafarkin haɗuwa da shi, bayyanarsa kamar bayyanar shaiɗan ce, kuma dodo, saboda baida bambanci da su, mutumin da idan ka ganshi a mafarki ka yi gaggawar tuba ka kuma kama yin istigfari don ba ƙaramin zunubi ka aikata ba..."
Kwata kwata babu alamun ya ji haushin kalamanta, sai dai akwai mamakin ta akan fuskarsa dake a murtuke, ya yi zaton jinta ya fi ganinta ashe ganinta ya fi jinta, shi ya sadaukar da ita amma bai ta6a haɗuwa da ita a zahiri ba, ya dai san komai game da rayuwarta ta hanyar ƴan leƙen asirinsa masu bibiyar rayuwarta, saninta da ya yi a madubin tsafin su ne inda suke ganin komai da ke faruwa a sashen fursinoni.
"Ina kokwanton kina da ta6in hankali, saboda mutum mai cikakken hankali ba zai ganni ido da ido ba, batare da ya tsorata ba saboda ƙwarjinin dake gare ni, yakamata ki shiga taitayin ki, ko baki ga inda kike ba ne..."
ya faɗa yana nuna mata ƙugiyoyin naman dake a sargafe jikin bango.
Gabanta ne ya fadi rass, sai dai bata bari ya gane ta tsorata ba.
"Na ji daɗi da Allah Ya haɗani da kai, Allah Ya amsa addu'ata, kawo ni da ka yi nan ba yin kanka bane, Allah ne ya kaddara haduwar mu saboda nemanka nake ruwa a jallo.." Out of confusion ya ke kallon ta..
"Kamar yadda kake kokwanton ko ina da hankali? Nima haka nake kokwanton anya kana da zuciya a ƙirjinka? Kai mutunne ko dabba...!" Bata ƙare maganar ba, ya kifa mata zazzafan marin da ya kusa sumar da ita, har saida kanta ya juye ta bugi bango.
"Ba a yi mini magana da tsawa.." Ya faɗa da gadara.
Juyowa ta yi tana huci, sumar kanta ta rufe gefe da gefen fuskarta, gefen lower lips dinta ya fashe har ya fara bleeding, ga shatun marinsa akan kuncin ta ya fito..
"Na je na yi Musa, ka maida gabana gabas ka yanka ni, na tsane ka fiye da yadda na tsani mutuwa, ƙyamarka nake ji, saboda kai ɗin najasa ne.."
ta faɗa muryarta na rawa tana zare mashi gray eyes dinta, tsantsar ruɗu ne akan fuskarsa.
"Tayaya zan ji tsoron mutum irin ka? Pls ka dinga tuna wanda ya halicce ka mana, na lura kana da izza da jiji da kai, halan ka manta tushen hallitarka daga ɗigon maniyi ne? Ko ka manta ta kofar da aka curo ka lokacin da za'a haifo ka ne? daga jikin mace mai rauni ka fito!"
Fuskarsa a ɗaure ya ke kallon ta. "Wanda mutuwa ta riske shi bai isa ya hana kanshi tafiya ba, Ni Allah kaɗai nake tsoro, bai haifa ba kuma ba a haife shi ba, kuma baya bacci, da shi kuma na dogara, wanene kai? Um? Ta faɗa tana ɗage masa gira.
"Mutanan da ka asirce ne suke jin shakkarka, amma ni baka isa ka sarrafa ni ba, na fi ƙarfinka wallahi, da Allah na dogara bada wani mahaukacin kare ba, mai taƙama da ƙarfin sihiri!"
Ta faɗa kamar zata doke sa, sarƙoƙin jikinta sai ƙara suke yi kacacau kacacau saboda girgiza jikinta da take yi, yanayin fuskarsa bai nuna damuwa ko kaɗan ba.
"Ki bini ta lalama mu rabu lafiya..."
"Ai bana so mu rabu lafiya, nafi so tsiya ta raba mu da kai, saboda nasan ba zaka ƙyale ni ba, ka kawo ni nan ne don ka azabtar da ni ko ka kashe ni, saboda kana baƙin cikin yadda na yi silar lalata komai naku, na ja maku bala'e da musiba, na sanya tsoro a cikin zukatanku shiyasa zama cikin gari ya gagare ka, shiyasa ka sato ni ka ka kawo ni nan! Maimakon ka farmake ni gaba da gaba a inda nake!"
bata ƙare maganar ba ya daka mata tsawa tare da sa hannu ya damƙi wuyanta ya matse shi kamar zai kasheta, nishi ta dinga saki numfashinta na fita a wahalce, tuni idanunta sun rune zuwa ja, har saida ta shaƙi ƙamshin mutuwa saboda tsabar raɗaɗin da ya ziyarci sassan jikinta.
"Ƙaramar yar iska mai kwana da wando, idan na kashe ki na kashe banza, na fahimci bakisan wanene Jan Wuya ba!.." Ya faɗa tare da sakin wuyanta, fatar gurin ta yi jawur kamar wadda hucin ruwan zafi ya daka, ta dinga tari tana nishi
Da ƙyar ta iya furta, "Ni kuwa nasan wanene kai, mugun uban da ya sadaukar da ƴarsa saboda neman abun duniyan da bazai amfanesa ba a ranar gobe alqiyama, kuma mugun mijin da ya raba ƴa da mahaifiyarta tuntana jinjira batare da sanin ta ba, ka raine ta batare daka bata tarbiya ba, da kai