Author : Boss Barture Category : Romantic Hausa Novels
Iyalin Alhaji Musa mu ji meke faruwa da su?
Da farko sun 6oyewa Hajiya Sarah abun da ke faruwa, kwata kwata suka ƙi sanar da ita, tayi tayi da su su faɗa mata meke faruwa sun ƙiya, kowa fargaban sanar da ita yake yi saboda suna jin fargaban halin da zata shiga, ba irin magiyar da bata yi masu ba, har kuka ta yi masu akan su faɗa mata abun da suke 6oye mata, idan ma mutuwa Musan ya yi kada su ji shakkun sanar da ita, zata fahimce su kuma zata rungumi kaddara, still suka ki sanar da ita, tsawon kwanaki sun barta a duhu, damuwa ta hanata sukuni, ta riga da ta sa ma ranta cewa wani mummunan abu ne ya faru shiyasa suke shakkun su sanar da ita, tun lokacin da sojoji suka kewaye gidan da kuma fitar da suka yi da daddare batare da saninta ba, abun da ya fi damun ta rashin dawowar Alhaji Musa gidan, tsawon kwanaki bata ji ɗuriyarshi ba, layukan wayoyinsa duk a kashe kum baya nemanta, duk wanda ta kira cikin abokan huldarsa da ta sani don ta ji ko su ya tuntu6e su sai suce mata a'a basu ji daga gare shi ba.
Daga ita har Zeenatu sun damu, sai da ta kaiga ko abinci basu ci sosai, basu bacci, ko office ta daina zuwa komai nata ya tsaya cak..
Tsananin tausayin su ne kullum ya ke ƙaruwa a cikin zukatan su hajiya Layla, musamman da ta dinga bin su ɗaki ɗaya bayan ɗaya tana roƙon su akan su sanar da ita meke faruwa?
Ta je ɗakin Benazir tana kuka ta roƙe ta ta faɗa mata amma ta ce ta yi hakuri ba zata iya ba, saboda bata son ta zama silar da zata shiga mawuyacin hali.
Bayan ta fito daga dakin Benazir ta je dakin Dr Shureim shima ta roƙe shi akan ya faɗa mata, amsar da Benazir ta bata irinta shima ya bata, kamar sun haɗa baki.
Zuciyarta ta sosu, still bata yi fushi da su ba, ta je ɗakin hajiya Layla ta roke ta itama ta ce ta yi haƙuri sanin bashi da amfani, bazata iya fada mata ba..
Kowa ta tambaya amsa ɗaya suke bata.
Lokacin da haƙurinta ya ƙare, ta kira su dukan su a main falo ta ce kodai su faɗa mata abun da suke 6oye mata ko kuma ta tafi tabar ƙasar tare da Zeenatu, ba zasu sake ganinta ba har abada, zata koma gurin family ɗinta.
Hankalinsu ba ƙaramin tashi ya yi ba, saboda sun san muddin ta koma gurin danginta, daga ita har Zeenatun zasu iya canza addini su koma nasu, dama ta ta6a faɗa masu iyayenta sun yafe ta daga family dinsu saboda auran za6inta da ta yi, tun farko sun nuna basu son ta auri baƙar fata wanda ba ɗan addininsu ba amma ta bijire masu ta auri Musa ta baro kowa nata.
Wannan maganar da ta yi ne yasa suka yanke shawarar sanar da ita komai dake faruwa.
Gaba ɗaya suka haɗu wurin fayyace mata komai tun daga kan cin amanar da Musa ya yi mata ya rabata da jinjirarta da kuma munanan ayyukan da yake aikatawa.
Inna lillahi wa'inna ilaihirraji"un..."
Kalmar ƙarshe da suka ji ta furta nan take ta yanke jiki ta faɗi, gaba daya suka rufa akanta suna ambaton sunanta haɗi da bubbuga jikinta don ta farka.
Cikin sauri Dr. Shureim ya dauko ruwa suka yayafa mata shiru bata farfado ba, a ƙarshe suka yanke shawarar kaita asibiti, suna a wannan halin sai ga motar hajiya Laura ta shigo gidan, a haukace ta fito daga motar jikinta na 6ari ta nufi ciki don ta faɗa ma yayanta abun da ke faruwa, lokacin da ta shigo sun yi mamakin ganinta, matar da kwata kwata babu ruwanta da su saboda rashin jituwar ta da hajiya Layla yasa ta ɗauke ƙafarta da zuwa gidan, suna ganinta suka fara tambayarta meke damunta? Ganin babu takalma a ƙafafunta, ɗan kwalinta ma a hannu ta ruƙe shi, cikin shesshekar murya ta ce ina yaya Musa? Tana son ganin shi! akwai abun da zata faɗa masa.."
Kwata kwata bata a nutsuwarta, ilahirin jikinta kerma yake yi, bata ƙare maganar ba, ta hango Hajiya Sarah dake a kwance kan floor ba numfashi Benazir ta rungume kanta a saman laps dinta sai yayyafa mata ruwa ta ke yi tana ambaton sunanta ta ƙi ta farka.
A ruɗe Laura ta tambayi me ke faruwa, kamar jira hajiya Layla take yi ta tambayi ba'asi aikuwa ta shiga zayyana mata komai dake faruwa, Alhaji Ubaid yanata ƙoƙarin dakatar da ita amma ta ƙi sauraron shi.
Tashin hankali ne tsantsa kan fuskar Laura, ita da ta zo kawo ma yayanta labarin abun da Obinna ya aikata, ashe shima yana daga cikin Elders ɗin wa'iyazubillah! Ta gaza yarda da abun da kunnuwanta suke jiyo mata, cikin ruɗu da gushewar hankali ta watsa da gudu ta nufi part ɗin yayanta tana fadin ba zai ta6a yiwu ba, hajiya Layla ƙarya ta ke yi mata, yayanta baya da sa hannu! Baisan komai ba, ƙazafi take yi masa dama tasan ta tsane shi.."
bayan ta shiga part ɗinsa bata taras da kowa ba.
Ta zaro wayarta ta dinga kiran layukan wayarsa gaba ɗaya a kashe take samun su, nan fa jikin taƙaura ya yi la'asar saboda bata ta6a kiran sa ta ji wayarsa a kashe ba sai idan da dalili, zama tayi akan couch ɗin dakin, duk ta bi tasha jinin jikinta, gabanta ya shiga faɗuwa rass rass, tsoro da firgici suka cika zuciyarta.
Bakomai take ji ba fa ce tsoron kada maganar da hajiya Layla ta faɗa mata akan yayanta ta tabbata gaskiya ne, ya za ta yi? Bata da wani gata da ya wuce shi, da shi ta dogara, shine shaƙiƙinta abun tunƙahonta, bata tunanin zata jure tozarci da kunyar duniya. A ƙalla ta shafe awanni tana jiran dawowar yayanta don bata fidda ran zai shigo gidan ba..
Jin shiru bai dawo ba ya sa ta fito daga ɗakin, bata iske kowa ba, a bakin maids din gidan ta ji cewa sun tafi kai Hajiya Sarah asibiti.
Kwata kwata bata damu da halin da ta riski matar yayannata ba, ita kawai damuwar ta yayanta ya zo ta ji daga bakin shi in gaskiya ne abun da ta ji a bakin hajiya Layla.
Har dare ya yi Musa bai dawo ba, ƙarshe a gidan ta kwana washe gari ta dasa zaman jiran shi, ba ci ba sha tun jiya rabon da abinci ya gifta ta makoshinta.
Kwana ɗaya da wuni mutanan gidan basu dawo ba, a lokacin Hajiya Laura ta sare da jiran yayan nata, kwatsam ta risƙi labarin kurkukun ƙaddara dake ta trending a social media, a nan ta ji cewa hada Alhaji Musa cikin Elders, kuma shine Jan Wuya mugun uban da ya yaudari ɗiyarsa, har labarin Unaizah ta karanta ta kuma ga hotonta da ke yawo a social media.
Batasan sa'adda ta saki wayar ta fadi ƙasa ta fashe ba, ƙunci da baƙin ciki suka cika zuciyarta, ta dinga kuka tana tsine ma yayan nata da ya jefa su a cikin musiba, a ƙarshe komawa ta yi cikin part ɗinsa ta kulle kanta, ta hargitsa ɗakin ta dinga zaƙulo kayayyakinsa tana watsarwa a ƙasa tare da tattake su da kafafunta, kamar mahaukaciya sai sambatu ta ke yi tana ɗura masa ashariya, tana cikin halin kwatsam ta ji wani abu ya tokare ƙirjinta me raɗaɗin gaske, a gigice ta daddafe ƙirjinta da tafukanta, jikinta ya dinga kerma, cikin fitar hayyaci ta dinga zubda gumi nan take ta yanke jiki ta faɗi tana kakari still hannuwanta na dafe da kirjin nata, ga shi ba wani a kusa balle a yi gaggawar taimaka mata, bayan dan lokaci gaba daya ta daina motsi hannuwanta suka faɗi gefe 😳
A bangaren Hajiya Sarah tun ranar da suka kaita asibiti aka kwantar da ita, bayan gwaje gwajen da docs suka yi mata a ƙarshe sun gano abun da ke damunta, sakamakon mummunan labarin da suka gaya mata ne ya yi silar kamuwarta da anxiety attack, wanda silar hakan hawan jini da ciwon zuciya suka yi mata mugun kamu, wanda idan har likitoci basu iya ceton ta ba za su iya rasa ta ne.
Hankalinsu ya tashi matuƙa har sai da suka yi danasanin faɗa mata ganin mawuyacin halin da suka jefa rayuwarta, kwata kwata bata a hayyacin ta.
Basu tashi sanin suna a cikin tsaka mai wuya ba, sai da Tani ta kira Dr Shureim a waya ta faɗa masa sunga Laura a ɗakin Musa babu numfashi a jikinta, sun kuma je kiran Zeenatu don ta ci abinci, itama sun isketa kwance a ƙasa bata motsi, sai lokacin ne suka tuna da babu Zeenatu a tare da su sun barta a gida, tsawon kwana ɗaya suna asibiti gurin jinyar Hajiya Sarah.
A asibiti suka baro hajiya Sarah karkashin kulawar likitoci, Lokacin da suka dawo gidan cikin sauri Alhaji Ubaid da Hajiya layla suka nufi ɗakin Musa, Dr Shureim da Benazir suka nufi up ɗakin Zeenatu.
Shigar su ke da wuya, kwatsam suka hangota a kwance saman gadonta, maids ɗinne suka kwantar da ita bayan da suka taras da ita a ƙasa bata motsi.
Kallon juna suka yi cikin rudu da tashin hankali, sam sun kasa ta6a ta sun rasa gane meya faru? Tani da ta biyo bayansu tana kuka ta miƙa masu wasiƙar data gani akan gadon Zeenatu.
Yatsun hannun Dr Shureim na kerma ya kar6a tare da buɗe ta, suka haɗu shi da Benazir suna karantawa.
_Na ji komai da ya faru, daddyna ɗan kungiyar asiri ne, ya raba ni da twin sister ɗina, ya zalunce ta, ba zan ta6a yafe masa ba. Kamar yadda ya sadaukar da ita ya yi silar mutuwarta, nima ya rasa ni na har abada, bazan ci gaba da rayuwa ba, zan bi ƴar uwata Unaizah, mommy ki yi hakuri da hukuncin da zan yankewa kaina, Yaya Shureim, Aunty Benazir ku yafe min, bazan iya jure baƙin cikin da daddyna ya ƙunsa mini ba, ya yaudare mu. Yanzu na gane dalilin da yasa ya ke yi min kulle saboda baya son ina fita don kada wanda yasan Unaizah ya ganni asirinsa ya tonu, kuma na gane dalilin da ya sa Azeezaty ta ruɗe a ranar da ta fara ganina har ta kira ni da sunan Unaizah ashe yar uwata ce da su ka yi rayuwa da ita a gidan kurkukun ƙaddara, Allah Ya isa daddy! Bamu yafe maka ba, Allah Ya wulaƙanta rayuwarka, in sha Allah hakkin Unaizah ba zai barka ba!_
Abun da ya faru lokacin da suke ba Hajiya Sarah labari, ashe Zeenatu ta fito daga bedroom dinta, tana kokarin shiga falon ta tsinkayi maganganunsu a cikin kunnanta, ta ji komai da ya faru hakan yasa ta ɗimauce, dama mai haƙuri bai iya zuciyata ba, hankalinta ya tashi zuciyarta ta karaya da jin labarin twin sister ɗinta da bata san da ita ba, hakan yasa ta juya da gudu ta nufi ɗakinta, tana shiga ta fashe da kuka kamar ranta zai fita, babu wanda ya san me ya faru, har ta gama kukan ta rubuta wasiƙar da Tani ta tsinta a ɗakin.
Lokacin da suka kammala karanta wasikar, zubewa suka yi agabanta saman gwiwowinsu suka fashe da kuka suna fadin meyasa zata kashe kanta bayan tasan babu kyau! Meyasa zata yi masu haka?"
Idan muka koma bangaren Hajiya Layla da Alhaji Ubaid lokacin da suka shiga bedroom din Musa, a kan floor suka hango hajiya Laura a kwance babu numfashi.
Da suka tatta6a jikinta a sandare suka ji shi, sun rasa gane ta mutu ko tana a raye saboda ruɗu, Lami ce ta kawo masu ruwa suka yayyafa mata a jikinta, ko gizau bata yi ba, nan fa hankalinsu ya tashi gaban su ya shiga faɗuwa.
Suna a wannan halin suka soma jiyo muryoyin Benazir da Dr Shureim cikin tashin hankali suke ƙwala masu kira suna fadin, "Daddy, Mommy! Kuna ina! Ku zo ku gani! Zeenatu ta kashe kanta, ta mutu, babu zeenatu..."
Basu san sa'adda suka saki Laura ba, Jikinsu na 6ari suka nufi falon har suna bangazar juna ita da Alhaji Ubaid, a daidai Lokacin sun nufo su Dr Shureim ne ya ɗauko gawar Zeenatu a saman kafadar shi.
Wa'iyazubilla! bazan iya misalta maku tashin hankalin da iyalan Elders suka shiga ba, ƙuncin rayuwa da baƙin ciki ne ke addabarsu ta ko'ina ba sauƙi gaba daya sun sare da rayuwar duniya.
A bangaren iyalan Ɗan iya, suma sun fuskanci nasu ƙalubalen bayan da asirin mahaifinsu ya tonu, suma sun ji komai game da kurkukun kaddara sun kuma ji hadda mahaifin su cikin Elders..
Gaba ɗaya saida shiga mutane ya gagare su saboda tsangwamar su da ake yi, dole suka killace kansu a gida.
Duk wani mai hulɗa da su saida ya ja baya da su, kyara da tsangwama ba wanda basu fuskanta ba a gurin mutane, hatta shiga social media saida ya gagare su, saboda munanan maganganun da mutane suke yi akansu, ubanninsu sun ja masu abun kunya, bayin Allah, su da ba laifin su ba.
Jarabta ce daga Allah kuma da suka yi haƙuri suka jure, cikin ikon Allah sun fara samun maslaha, manyan malaman addini na ƙungiyar sheikh Imam Malik dama wasu manyan malaman duniya sun tsawatarwa mutanen dake cin zarafin su akan laifin da bana su ba, sun yi nasiha sun yi wa'azi akan halin da iyalan elders suke a ciki, kuma cikin ikon Allah sai gashi sun fara samun sassauci, mutane sun gane kuskuren su na ƙuntata masu da suke yi, musamman da suka ji labarin abun da ya faru da twin sister ɗin yarinyar da labarinta ya ta6a zuciyarsu, hankalin kowa ya tashi da jin Zeenatu ta kashe kanta, mahaifiyarsu kuma tana a kwance rai hannun Allah sakamakon abun da mijinta ya yi ma ƴarta, su kansu ƴan'uwan nata basu san ya akai labarin Zeenatu ya fita ba, hasalima basu son asani saboda abu biyu, na farko basu tabbatar da mutuwar Zeenatu ba! Bayan da suka kaita asibiti doc ya faɗa masu da yiyuwar doguwar suma ta yi saboda babu alamun ta sha poison ko lahani na ciki ko na waje a jikinta, abu na biyu saboda tsoron surutun mutane, amma sai dai suka ji labarin yana yawo a social media tare da hotunan Zeenatu. Sai daga baya suka gano cikin ƴan aikin gidanne suka fitar da labarin, aikuwa ransu ya 6aci matuƙa, har mataki suka ɗauka akan ƴar aikin da ta yaɗa labarin duk da ta janyo masu tausayar al'umma.💔
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin kaninfari 1k Tsimin dabino 1k Gumba 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 4k
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 maganin Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki.
*Welcome, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan number din 08103884440*~___________________________________💔🔥~
Luxury-incense By Sapnah Borno.
Ta kawo muku turarukan wutan su Na maiduguri dana chad, turarukanta masu masifar dadi da kama waje harma da daukar hankali, indai kikayi kabbasa da turaren ta har wajen da kika zauna indai kika tashi sai kin bar kamshin ki, sannan Tana saida mayukan gashi irin nasu na shuwa Arab masu tasirin gaske, wajen gyaran Amare kuwa babu magana dan tazo muku da Chadian and Sudanese dilka Wanda zaki gyara jikinki da kanki, oga ya kasa ganeki, haka zalika akwai wata humrar ta mai suna hana bacci da kuma sirrin shuwa Abun ba magana, yar uwata ki jarraba turaren yar mutan borno nasan zata zame miki best turaren wuta plug. Tanada turarukan da zaki turara gida, toilet, bedsheets, curtains, kabbasa and hair incense ku jarraba kada ku bari ayi babu ku.
Wardrobe balls
Kabbasa spray
Chadian khumra
Hawee
Halud
Gabgab
Sandal sukkariya
Kajinguru
Dilka soap
Ready to use dilka
Karkar oil
Turaren tsuguno
Habil
Dorut
Dorot after period
Brown khumra
Dufr khumra
Body milk
Sudanese kuleccam
Chadian dufr kuleccam
Musk khumrah.
Maganin matan mu sunada inganci Wanda muke kawo su daga sudan, sannan munada maganin karin girman nono, Wanda basuda effects, ga masu bukatar maganin Matsi ko maganin mata Masu aiki garanti munada su, sannan muna zuwa gyaran jikin amarya a duk garin da take
Our Chadian aphrodisiacs are.
Beejay fire
Sata jagab honey
Wetness and sweetness combo
Daka
Great A sabaya
Breast engagement powder
Ciccibi
Gumbar madara
Gumbar dabino
Bita Zaizai
08164570032.
~____________________________________Daga alƙalamin Hafsat Bature Boss✍️~
Kowan nan su yana a zaune kan kujera cikin Cell ɗin Isod, A hankali Chief Owais ke duban fuskar Praveen da ya sadda kanshi ƙasa cikin tsananin tashin hankali da fargaba, gaba ɗaya babu nutsuwa a tare da shi ga rashin koshin lafiya, la66ansa sun kumbura suntum, gefen idonshi na dama ya kumbura harda kwantsa a cikin su, gaba ɗaya jikinshi a kumbure yake ga tarin raunukan da ya ji sakamakon bugun da su Sir mubarak suka yi ma shi, har yau bai dawo