Author : Boss Barture Category : Romantic Hausa Novels
ta nufeta suka rungume juna, kamar zasu koma mutun ɗaya, yau dai ta zama ranar tunawa a rayuwar su.
(Ni boss hada ƴar ƙwallata 😥)
"Sis kina lafiya? Meke damun ki? Ya cutar da ke ne um?"
adabarbarce take tambayarta..
Da kyar ta iya buɗe baki muryarta ƙasa ƙasa ta ce, "Ba abun da ke damuna, lafiyana lou, bai yi mini komai, ina fata kema kina lafiya..."
jinjina mata kai Batool ta yi, "Nima ina lafiya sister, na ji dadi babu abun da ya faru da mu, Allah ya kare mu, bai cimma manufarsa ba." Ta fada tana dan sauke ajiyar zuciya.
"Sai dai ban iya tuna komai da ya faru ba."
"Batool, tunawar baida amfani, tun da ba alkhairi bane, idan ma akwai abun da ya kamata ki ji zaki ji, amma ba yanzu ba.."
Murmushi ta yi, "Na ji, amma kin yi min laifi, daga yanzu karki ƙara kira na Batool, ni ƴar uwarki ce, cousin dinki ce, kuma yayarki, sannan aminiyarki..."
Gaba ɗaya suka sanya dariyar farin ciki, musamman iyayensu farin ciki ne tsantsa tare da su .
"Kina nufin, ke ɗiyar Uncle ɗina ce Shureim? Jinin da ke yawo a jikina shine a jikin ki?" Ta tambaya kamar irin batasani ba..
Cike da jin dadi Batool ta jinjina mata kai,
"Ba mamaki, shiyasa farko da kika fara ganina a gidan kurkukun kaddara kika manne min kamar ciki ɗaya muka fito ashe jinina ce ke." Dariya suka yi..
"Ina taya ki murna Batool, Aunty Ummi, Uncle Shureim kuma ina taya ku murna, kamar yadda Batool ta yi dacen iyaye nagari, kuma haka kun yi dacen ƴa ta gari, saboda Batool ta dabance, samun irinta zai yi wuya, ni ta yi min hallacin da bazan iya biyanta ba, saboda ta ja ni a jiki a lokacin da sauran yan uwanmu suke guduna, a lokacin da nake tsaka da maraicin rashin wani nawa a kusa da ni, a kuma lokacin da na tsinci kaina a baƙon guri mai rikitarwa, duk yadda zan misalta maku ba lallai ku fahimta ba.."
ta fada tare da janyo Batool ta rungumeta.
kukan farin ciki suka kama yi.
gaba daya kowa dake a gurin saida ya zubda masu ƙwalla saboda sun ta6a zukatan su.
Saida suka gama koke koken farin cikin nasu, daga bisani Ummi ta janyo hannayensu, ta kawo su gaban Chief Owais wanda komai dake faruwa a kan idanun shi, ta kuma ruƙo hannun Benazir ta ce ma Taj ya matso kusa da ita, gaba daya suka kewaye Chief Owais.
"Bani da abun da zan iya saka maka da shi, bazan iya biyanka ba! illa iyaka in sanyaka a cikin addu'o'ina, Allah yasa silar kyautata mana da ka yi ya zama sanadin shigar ka Aljanna, Allah ya wanzar da farin ciki da lafiya mara yankewa a cikin rayuwarka, Allah ya yaye maka dukkan damuwarka, Allah ya lullu6eka da rahamominsa, Ya kare mana kai daga sharrin duk wani abun cutarwa da kai da ahalinka, Allah ya ci gaba da daukaku, Allah ya baku hakuri da juriyar cinye jarabawar da kuke fuskanta, Allah kuma ya baka mata tagari wadda zata zama cikamakon farin cikin rayuwarka..."
Tun da ta fara yi masa addu'oin ya lumshe idanunsa yana ɗan jinjina kanshi, gaba ɗayansu suke amsawa da Ameen Ameen, Chief ya yaba da addu'oin ta sun faranta ran shi.
"Abun da yasa na tara ku a gabansa, saboda ina so ku taya ni yi mashi godiya, saboda ba zan iya yi ni kadai ba."
ta fada tana duban kowan nansu, aikuwa gaba daya suka haɗu suna yi mashi godiya da addu'o'i duk da ya nuna basai sunyi ba, ya ce su gode ma Allah shine abun godiya, suka ce sun yi wannan amma yabon gwani ya zama dole.
Gaba ɗayan su suka fito daga headquarter din, suka nufi inda suka bar Motocin su, bayan kowan nan su ya shiga ciki, at same time motocin suka soma tafiya a hankali, har suka bar headquarter ɗin.
"Baby, ina kika samu waɗannan kayan na jikin ki? Tun dazu nake ta so in yi magana." Ummi ce ta faɗa tana kallon Batool, da sauri ta dubi kayan, shirt ce fara, da coat din da aka daure mata qugunta da shi, daga gaban rigar an rubuta Dg.
Zare idanu ta yi kafin ta yi magana Ummi ta riga ta cewa, "Kamar kayan Chief ne ko? Na ga sunan rank dinsa a jiki."
"Bansan lokacin da ya sanya min rigar ba, bazan iya tunawa ba.."
ta fada tana dan girgiza kan ta.
Dr shureim da ke driving dinsu, a hankali yake satar kallon su ta mirror, sai faman sakin murmushi ya ke yi yana kallon family ɗinsa.
"Wani kaya ne last a jikin ki?"
"Overroll ce, irin ta jikin Unaisah, sai coat da muka ɗaura a sama, bansan ya akai na rasa kayana ba." Kwanto mata da kai Ummi tayi kan kafadarta, ta lumshe idanunta tana sauke a jiyar zuciya..
Wow 😍😂
_______________________Ex-Prisoners🔥🔥🔥🔥🔥🔥
"Naufal! ! Haris! Javed! Mubeen! Ku tashi na samo mana hanyar da zamu fita" can cikin bacci suka tsinkayi muryar Sajeed dake ta kiran sunayensu cikin muryar raɗa.
Bubbuga kafafunsu ya yi, "Dalla ku tashi, idan ba haka ba zan tafi in barku."
At same time suka farka tare da yaye bargunan su, idanunsu biji biji suke ganin shi, sai miƙa suke yi da hamma alamar bacci bai ishe su ba, a saman wata ƙatuwar mattress suke a kwance lallausar gaske, mai tudu kamar gado.
Hasken dakin ya kunna hakan yasa suka samu damar ganin shi da kyau, yana a tsaye gaban katifar hannun shi ruƙe da nannaɗaɗɗiyar igiya mai kauri, zaro idanu waje suka yi a ruɗe har suna hada baki gurin furta, "Sajeed me zaka yi da igiya?"
Harara ya watsa masu, "Bana ce maku ina ta nema mana hanyar da zamu fita ba? Ko baku so ku koma sashen Chief?"
Haris da ya fi su hankali ya ce, "Sajeed kana da gajan hakuri, kuskure ne wannan mu yi gaban kanmu ba tare da izinin daddy Taj ko Chief ba! Ransu zai baci idan suka ji, tun da sun ce mu ƙara hakuri why ba zaka hakura ba?" Harara Sajeed Ya watsa mashi tare da tamke fuskarsa.
Naufal ya ce, "Ni abun da bangane ba, ta wani kofa ne zamu fitan? Me kuma zamu yi da igiya?"
"Haƙurina ya ƙare, ni bazan ci gaba da jira ba, wallahi babu wanda ya isa ya hanani in fita, na gaji na gaji, ku baku gaji bane da zama a kulle? Baku tunanin akwai wani abu da ya faru wanda ba aso mu sani shiyasa aka garƙame mu anan?"
Kallon juna suka yi, kowan nan su da wannan tunanin a ranshi.
"Idan nan zamu ci gaba da zama meyasa ba za a dawo da su Unaisah nan din ba? Me kuma yasa mu ba za a mayar damu can ba? Meye amfanin kulle mu?"
"Sajeed, amma ai muna yin waya da su Unaisah ko? Kuma sun faɗa mana komai lafiya lou, sun je farmaki sun dawo lafiya."
Javed ne ya fada fuskarsa a yamutse..
"Baku tunanin sun faɗa mana hakanne don su kwantar mana da hankali? Ku yi tunani mana! Wani abu yana faruwa! Har yanzu ban yarda Danish yana lafiya ba, kawai suna boye mana ne, ƙwara mu je mu gane ma idon mu." Kallon kallo suke jefawa junan su.
Tunzura su ya dinga yi har saida ya shawo kansu suka amince zasu bishi, saukowa suka yi daga kan latifar, gaba dayansu pyjamas ne a jikin su, kowa da kalar nasa.
Sajeed ne jagoran su wato Master Planner, yana a gaba suna a biye da bayan shi cikin sanɗa suke yin tafiya, kamar 6arayi duk don kar a kama su.
Cikin muryar raɗa Naufal ya ce, "Mu kadai zamu tafi? Su parveen fa? Idan suka farka suka ga babu mu zasu shiga damuwa."
"Ƙwara karmu tafi da su, kasan halin Jemimah tsiwarta kaɗai ta isa ta tona mana asiri, in aunty Danejo tasan me muke ƙullawa zata kira ne ta fada.." Javed ne ya fada.
"Ku daina ɗaga murya, ku yi shiru." A cewar Sajeed.
A hankali suke tafiya suna yan waige waige sun jera layi, sai da suka kusan ƙarasawa ga stairs unexpected suka ji muryar mutane a cikin kunnan su..
"Banza ki sha a hankali kada ki ƙware, matsalata dake kin cika haɗama, wlh zan tona mana asiri muna satar abinci uban kowa ya ji." "Wai ke ina ruwanki da ni, ba cewa ta yi mu ci komai muke so ba..." Gabansu ne ya faɗi kusan a tare suka kai dubansu gare su, suna a zaune kan matakalar benen da suke tunkara, su biyu ne, Praveen ta tasa plate din chicken pepper soup, da duka hannayenta biyu ta ke duma loma, bakinta duk maiƙon mai.
Jemimah tana zaune a gefenta, saman cinyoyinta gwangwanin madara ne daga gani sabo ne ta fasa, ta buɗe shi sai sha take yi, duk ta yi buɗu buɗu da kumatunta, har saman gaban rigar baccin ta madararce ta 6are kamar farar kura.
"Mun masu wayo sunata bacci, mu kuma kullum sai mun farka tsakar dare mun saci abinci, da safe aita neman wanda ya kwashe ragowar abinci, mu yi shiru da bakinmu, wai Aunty Danejo sai tace 6era ne batasan mune 6erayen ba.." Jemima ce ta fada.
Parveen ta ce, "Ai ran nan ina jin ta tana tambayar waya sace naman miya, nasan kece munafuka." ƙyalƙyacewa suka yi da dariya, su kadai a tsakar dare ko tsoro basa ji.
"Ya zamu yi? Haris ne ya tambaya.
"Wallahi idan suka ganmu ba zasu bari mu fita ba," Naufal ne ya faɗa..
"Ku yi shiru, a hankali zamu bi ta ɗayan benan, kada ku yi wani motsi da zaisa su lura da mu!"
Sajeed ne ya faɗa cikin raɗa..
Cikin sanɗa suka fara hawa stairs din, suna tafiya suna waiwayon su Parveen...
Sai da ya rage saura Mubeen dake a bayansu yana gab da zai haura second floor tari ya kubce mashi.
Aikuwa a rikice Parveen da Jemimah suka zabura tare da mikewa tsaye gaba ɗaya suka saki abun da ke hannunsu ya 6are ƙasa, kafin su kai idanunsu tuni Haris ya ja wuyan rigar Mubeen sun karya kwana.
Kallon juna Jemimah da Parveen suka yi idanunsu azazzare..
"Jemimah kinji sautin tari?"
Jinjina mata kai ta yi, "ƙwara mu koma ɗaki, ni tsoro ya kama ni, dama Aunty Danejo ta ta6a bamu labarin fatalwar dare dake zuwa ma mutun in bai yi bacci ba ta cinye kurwarshi..."
A tsorace ta faɗa tana zare green eyes din ta.
"Dallah ƙarya take maki, babu wani fatalwa, tatsuniya ba gaskiya bace ƙirƙirarran labari ne.."
bata ƙare maganar ba idanunta suka sauka akan warin takalmin dake akan ɗayan stairs din gefen su.
Cikin sauri ta nufi takalmin, Jamimah na gani ta gargaɗe ta akan kada ta ɗauka na ɗan aljani ne, ta yi banza da ita.
Daukar takalmin tayi ta jujjuya shi nan take ta gane warin slippers din yan uwansu maza ne.
"Wani ya wuce ta wurin nan, Jemimah ki jira ni, bari na je na leƙa."
Ruƙe rigarta Jemimah ta yi"Ai wallahi ƙafata kafarki, Yo kawai ki barni fatalwa ta cinye kurwata."
Dungurin goshinta Parveen ta yi, "Shashasha, mu je." Upstars suka hau, duk inda Parveen tayi Jemimah tana a biye da bayanta kamar bindi, har suka 6ullo ta hanyar da su Sajeed suka bi, suna ƙarasowa suka hango ƙatuwar glass window dake a buɗe, ta cikinta suka dira ta baya akan wani floor, anan suka hango igiyar da suka ƙulla jikin ƙarfen da ke a kewaye da gurin da tagar take.
"Hakan na nufin su Sajeed sun fita!" Ta fada tana dan jinjina kanta, murmushin gefen fuska ta saki..
Ta soma kiciniyar kama igiyar don ta dira, ruƙo ƙafar wandonta Jemimah ta yi a tsorace ta ce, "Dan Allah kada ki tafi ki barni, bazan iya hawa ba."
Harara Parveen ta watsa mata, "Ya zan yi dake? Karki kuskura ma ki ce zaki hau, faɗowa zaki yi kanki ya fashe ki mutu.."
Kuka ta saka mata, bata saurareta ba ta buge hannunta, ta ruƙe igiyar ta bi jikinta, ko leƙenta Jemimah bata iya yi saboda gajartarta.
Watsawa ta yi da gudu ta koma cikin gidan ta nufi dakin sauran yan uwan nasu.
A lokacin suna a kwance kan mattress dinsu kusan su shida sun kudundune cikin duvet ɗinsu.
Abun ka ga mai ƙarancin hankali tana shiga ta daka suka ta dira a samansu, aikuwa a firgice suka farka tare da yaye bargon, suna ganinta suka fasa ƙara saboda razanar da suka yi.
Ganin yadda suka ruɗe ne yasa ta yi saurin cewa, "Ni ne fa Jemimah.." Ta faɗa tana goge garin madarar dake akan fuskarta, lokaci ɗaya suka sauke ajiyar zuciya.
"Uban me ya kawo ki dakinmu?"
"Kawai muna baccinmu kin wani zo kin tada mu! Me ma ya farkar dake a irin wannan lokacin.."
Idanunta cike tab da ƙwalla ta ce, "Pravin ta fita, nayi nayi da ita ta tafi da ni ta ƙi."
waro idanu waje suka yi cike da mamaki jin abun da ta ce, "Ina ta je?"
"Ku zo in nuna maku, har takalmin su Mubeen muka tsinta suma sun fita, na je ɗakinsu ban gansu ba."
Da shagwa6a ta ƙare maganar,..
Kusan a tare suka sauko daga kan katifar, in ka cire mutun ɗaya da bata farka ba, saboda nauyin bacci ne da ita sai sharar baccinta ta ke yi.
Gaba Jemima ta yi suka bi bayanta, bayan da suka ƙarasa gaba ɗaya sun yi mamakin ganin igiyar da aka ɗaura.
"Abun da za'ai, tun da mun samu hanyar fita, mu bi su kawai." A cewar Sarah.
"Ɗaya bayan ɗaya zamu hau."
"Ni fa wa zai goya ni?"
Wani kallon rainin wayou su ka yi mata, "Ki koma ki kwanta, ba za ki iya hawa ba, zaki iya faɗuwa ki mutu." Fashewa ta yi da kuka, "Wlh saina tona maku asiri gurin aunty Danejo, tun da ba zaku hau da ni ba."
Da jin hakan suka fara lallashinta, Hawwa ta ce, "Abun da za'ai yanzu, Jemimah ki je ki kira Azeeza da Deeja, su zo mu tafi, kada mu barsu Su kadai," Amsawa tayi da toh, sai bayan da ta tafi Sarah ta ce, "Meyasa zaki aike ta ta kira su?"
"Saboda mu samu mu tafi, in ba haka ba ba zata ƙyale mu ba."
Hannah ta ce,"Deeja bata da hankali, akwai matsala idan Jemimah ta gaya mata, Azeeza kuma bazata iya fitowa ba saboda tsoro."
Hibba ta ce, "Yanzu ya zamu yi? Ga samu ga rashi, don wlh idan muka tafi risky ne su zo gurin nan," ta faɗa da damuwa..
Hanna ta ce, "Idan kuma muka dira muka je can, baku tunanin zamu ja ma kanmu wata matsalar?"
"Yanzu me kuke nufi mu hakura mu koma?" Yasmin ce ta fada tana dubansu..
Rubina ta ce, "Kun manta nauyin baccin Deeja? Wlh ba zata farka ba ko Jemimah zata watsa mata ruwa ne a jikinta, ita kuma Azeeza tsoro gareta, ba zata iya hawa igiya ba, dole su haƙura da bin mu..."
da jin wannan maganar ta Rubina nan fa suka samu kwarin gwiwar aiwatar da abun da ke ransu.
Sarah ce ta fara hawan igiyar saida ta dira ƙasa, sannan Hawwa ta haura itama..
Ɗaya bayan daya suka dira gaba daya.
Baiwar Allah Jemimah sun mata wayou, a gajiye ta koma dakin su ta je ta taso Deeja, ta dinga bubbuga kafadarta, cikin magagin bacci Deeja ta dinga zaginta, da ta saka naci aikuwa ta sanya ƙafa ta ingizata, gaba daya ta kundumo ƙasa daga kan katifar, cikin shesshekar kuka ta ce, "Allah Ya isa banza, don kin samu na zo tada ki, kuma wlh tafiya zamu yi mu barki, kuma saina rama." Ta faɗa tare da mikewa ta hau kan gadon, ta saita cinyar Deeja ta gartsa mata cizon da ya yi silar farkawarta ta fasa ƙara, kafin ta dawo hayyacin ta, Jemimah ta watsa a guje ta nufi ɗakin Danejo dake a upstairs, ta buɗe ƙofa ta shiga cike da zullumin kar Deeja ta biyo bayan ta.
Cikin sanɗa take tafiya, ɗan hasken bedside lamps ne kadai ya haskaka dakin.
Hawa ta yi kan gadon ta rarrafa ta nufi Azeeza dake a kwance gefen Danejo, saitin kunnanta takai bakinta, "Azeeza! Azeeza! Ki tashi ki ji wani abu." Takura mata ta yi da ƙyar ta farka, toshe mata baki Jemimah ta yi da tafinta, abun ka da matsoraciya ta zazzare eyes dinta kwata kwata bata iya ganin wanene ya toshe mata bakinta, saboda ƙarancin hasken ɗakin duk da ta samu lafiyar idanunta amma har yanzu in haske bai wadatu ba bata iya gani da kyau, sa6anin da ko da akwai haske sosai in dai dare ne bata gani.
"Ni ce fa, Jemimah, ki taso mu tafi, su Parveen sun samu wata kofa a baya sun fuce daga gidan nan..." Ajiyar zuciya ta sauke jin muryar Jemimah dake mata raɗa.
Buge hannunta ta yi, "Ba inda zan je, ki kyale ni in ci gaba da yin baccina pls,"
"Dan Allah ki taso mu tafi, suna jiranmu, su suka ce in kira ki mu tafi." Da jin wannan maganar yasa ta miƙe, ruƙo hannunta Jemimah ta yi, ko mayafi babu akanta sai zallar sumar kanta da ta rufe bayanta.
da taimakon Jemimah take iya ganin hanya, cikin sanɗa suka fuce daga ɗakin.
~________________________________🌹💋~
A bangaren su Owais, bayan da suka fito daga motocin su suka nufi main falo, fuskokin su ɗauke da murmushi.
Officers suna ganin Unaisah da Batool suka fara sauke ajiyar zuciya tare da godewa Allah da ya dawo da su lafiya..
Chief yana jiyo muryar wani officer yana fadin, "Allah ya ku6utar da mu da ya dawo masa da hurul aininsa, don wlh ba raga mana zai yi ba, yadda yake ji da yaran nan kamar ransa akan su har kurkuku zai iya sawa a kulle mu."
Murmushi Chief Owais ya yi tare da ɗan girgiza kan shi.
Ummi da Shureim ne a gaba sun saka Batool a tsakiyarsu, yadda kasan wadanda suka ɗauko kwai a cokali sai tattalinta suke, ko tari ta yi sai sun tambayi is she okay.
Haka Unaisah ma tana a tsakiyar Taj da Benazir, sun saka ta tsakiya, hannayensu tallabe da bayanta, Anila tana a gefen su.
Sheikh Imam da Chief Owais suna a biye da bayan su.
A hankali Ƙofar falon ta zuge, suna shiga Unexpected suka yi arba da Chefs kewaye da ƙofar, a tare suka hada baki gurin furta, "Muna yi maku barka da dawowa gida lafiya, Unaisah and Batool, mun yi murnar ganinku