Author : Boss Barture Category : Romantic Hausa Novels
Hajiya Sarah na Imam Estate, yana da girma da faɗi, side by side duplex ne, bangare ɗaya na Hajiya Sarah da ƴa'yanta, ɗayan bangaren na su Hajiya Layla ne, babu abun da suka nema suka rasa a gidan, sun ji daɗi sosai tsakanin su da ahalin Obie sai godiya da addu'a.
Alhaji Ubaid gaba ɗaya ya siyar da kadarorinsa na Jos, da kuɗaɗen yake amfani gurin tafiyar da iyalinsa da na Alhaji Musa, yanzu shi ke ɗawainiya da su, don ma Hajiya Sarah tana da arziƙinta, dama can mace ce mai zafin nema babbar ƴar kasuwa ce, daga baya ne ma da gwamnati ta ƙwace kadarorin Alhaji Musa itama ta rasa aikin da take yi a companyn sa.
Amma Alhamdulillah yanzu gaba ɗaya waɗanda suka rasa ayyukan su cikin family ɗin Elders sakamakon abun da ya faru Sharafudeen ya ɗauke su aiki a babban companynsa, babu mai zaman banza, Kowa ya na ƙoƙarin neman na kansa.
Gaba ɗaya dai Ahlin Elders sun zama tsintsiya ɗaya maɗaurinta ɗaya, wata irin shaƙuwa da zumunci mai ƙarfi ne atsakanin su.
Shin ya labarin Zeenatu? tun bayan da tayi doguwar suma sai da ta shafe makonni bata dawo hayyacinta ba, tana a ƙarƙashin kulawar docs, bayan shari'ar Elders da sati ɗaya, Zeenatu ta farfaɗo cikin hayyacinta, mommynta da ƴan uwanta sun yi murna sosai, har kukan farin ciki suka yi duk da a lokacin bata magana sai dai idanunta da ke tsiyayar da hawaye, sun fahimci har yanzu da damuwar abun a ranta, bayan doc ya sallame ta suka dawo gida da ita, tsantsar kulawa suke bata, kwata kwata bata tambayi ina daddynta ba, saboda tsanar da ta yi mashi ko sunan shi bata son ji, kuma wani iko na Allah Zeenatu ta daina son Yaya Shureim da aure, babu soyayya a ranta, da suna ta zullumin tayaya zasu faɗa mata game da soyayyar Shureim da Aisha amma da suka lura babu son shi a ranta, yanzu kallon ɗan uwa kuma Yaya take yi masa sai suka godewa Allah da ya kawo masu mafita, bakomai ne ya faranta ran Zeenatu ba, face ganin tagwayen da mommynta ke ruƙo, har tambayarta ta yi su wanene? Nan Hajiya Sarah ta labarta mata komai game da su, ta tausaya ma rayuwarsu, ta kuma ji daɗi da ya kasance mommynta ne zata ci gaba da ruƙon su, da kallo ɗaya ta ji ta kamu da ƙaunar su, suma haka suka ji, yanzu ta samu tsararrakinta a gidan duk da sun girme ta da shekara ɗaya.
Batare da 6ata lokaci ba, Alhaji Ubaid ya mayar da su school, daga jami'a suka fara shi ya yi masu ƙoƙari gurin sama masu takardun secondary da kuma admission na shiga jami'a da taimakon Owais.
A baya kafin zuwan su twins kurkukun ƙaddara sun yi karatu harma sun kammala secondary, shiyasa karatun su ya zo musu da sauƙi, gaba ɗayan su yanzu suna a jami'a, sajeed Yana karantar Cybersecurity, yayin da Zeenatu da Sajeeda suke karantar Human Rights, su suka za6a da kansu saboda suna da burin su bada gudummuwa gurin kare hakkin ɗan adam.
bayan haka kuma suna zuwa islamiya wadda ke a cikin estate ɗin neman ilimin addini sun bada himma sosai.
Hajiya Sarah ta yi namijin ƙoƙari gurin tafiyar da rayuwar su, babu abun da suka nema suka rasa da arziƙinta ta ke kula da su, ba zaka ta6a gane ba ita ta haifi twins ba sai in an faɗa maka, haka zalika Alhaji Ubaid da Hajiya Layla suna bada gudummuwa gurin tallafa mata akan kula da yaran, Shureim da Benazir da Omar ma ba abar su a baya ba, suna ƙoƙari gurin koya masu abun da basu iya ba, sun zama yayye nagari a gare su.
A zahirin gaskiya rayuwar Prisoners a gurin iyayen su sai son barka, wata irin soyayya suke nuna masu, tsantsar gatanci, kulawa da tarairaya kamar jinjirai, sai abun da suke so iyayen su suke yi masu, gaba ɗaya sun sanya su a school ɗin cikin estate ɗin su bayan private teachers ɗin da ke zuwa yi masu lessons na boko dana islamiya a cikin home classroom din su.
Yara fa sun zama ƴa'yan mommy da daddy, hutu ya zauna masu, babu tashin hankali babu damuwa, sai zallar farin ciki da jin daɗin rayuwa, in ka gansu ba zaka ta6a yarda sun yi rayuwar ƙunci a gidan kurkukun ƙaddara ba, su kan su mantawa suke yi da sun ta6a shan wahala a rayuwar su, Yanzu sun waye, ilimin boko da na addini ya shiga kan su, halayan su da ɗabi'un su sun sauya, lamarin Ubangiji kenan, gwanin hikima, mai yin yadda ya so, mai jujjuya al'amurra, godiya ta tabbata ga Allah maɗaukakin Sarki 👑🌹
Bayan da ƙura ta lafa, kwanciyar hankali da farin ciki suka wanzu a zukatansu, bayan shekara ɗaya da rabi Dr Shureim ya auri Aisha, yayin da Taj ya mayar da Benazir ɗakinta, Owais ya auri Nazli, A canada aka yi shagalin bikin su na gani na faɗa, ya so ya haɗa da Unaisah ya aure su a rana ɗaya amma ta nuna bata shirya ba, tafi so ta kammala karatunta, bai musa mata ba, shima ya goyi bayan ta yi karatu, da taimakonsa ya yi mata hanya ta zana jarabawar ssce batare da ta shiga ss one ba, dama a baya kafin ƙaddara ta kaita kurkukun ƙaddara ta kammala junior secondary, shiyasa karatun nata ya zo mata da sauƙi, tana a jami'ar da su Sajeed suke, anan take karantar Computer Science, Owais ya yi masu alƙawarin in har suka kammala karatunsu zasu ɗauke su aiki a hukumar su ta Isod saboda suna buƙatar irin su.
Tun farko abun da ya sa Unaisah ta ƙi yarda ya aure su a rana ɗaya ita da Nazli saboda tana jin shakkar ta zama kishiyar Nazli wayayyar ƴar gayu, tafi son ta ƙara wayewa ta yi zurfi a ilimi sannan ta koyi abubuwan da bata iya ba don kada Nazli ta raina ta, a yanzu ta dage damtse gurin koyon girki a wurin mommynta, kuma ta bada himma sosai gurin karatunta, bata wasa da yake Allah ya yi ta da brain she's gifted, tana da baiwar haddace karatu da saurin koyo shiyasa bata jin wahalar komai.
Bayan da ya auri Nazli sai da ya yi hutun wata biyu a gidansa na Canada tare da amaryarsa Nazli, gaba ɗaya suka sauke girman kai da izzar su suka nuna ma juna soyayya, tun a first night ɗinsu suka raya daren su, daga bisani suka tafi honeymoon.
Owais bai tashi dawowa Nigeria ba, sai lokacin bikin Omar da Salsabeel, kuma shi ya haɗa Omar da matar da zai aura, bakowa bace face ƙanwarsa Hindu, yayin da Momma ta haɗa Auran Salsabeel da Yusra ƴar gidan his excellency Abdul razak, kuma cikin sa'a jinin su ya haɗu, duk da a lokacin da momma ta zo mashi da maganar Yusra, ya ji shakkar haɗa shi da ita saboda yasan tafi ƙarfin shi, gata dai ɗiyar gwamna, wayayya, kyakkyawar budurwa, jinin shuwa, a da kafin yanzu tana da girman kai da izza, amma tun bayan faruwar lamarin nan ta sauya hali, ta zama mutuniyar kirki, koda momma ta faɗa mata game da Salsabeel ta kuma nuna mata hoton shi a waya, nan take ta ce ta amince in har yana sonta, zata aure shi, amma tana son bayan sun yi aure ya koma makaranta ya nemi ilimi, itama zata taimaka mashi, Salsabeel ya yi farin ciki mara misaltuwa a lokacin da momma ta faɗa mashi yadda suka yi da Yusra, har sujjada ya yi don nuna godiyar sa ga Allah, Auran gata Momma ta yi ma Salsabeel, ko sisin shi bai kashe ba, tun daga lefensa har sadaki ita ta bayar, har kuka saida ya yi mata saboda farin ciki, A ranar bikin su anyi gagarumin shagali a Imam Estate, amare sun tare a gidajen mazajen su, abun sai son barka.
Idan muka koma bangaren Faryat, reshe ne ya juye da mujiya, yanzu ita ke son Jazz shi kuma yana ja mata aji, ta sauya hali ta nutsu ta koma tagari, ta daina duk wani abu mara kyau da take yi, amma Jazz ya ƙi sauraron ta, wahalar da ita yake yi, kusan kullum sai ta yi kuka saboda azabtuwar da ta ke yi da son shi, idan ta kira wayarsa baya picking, ko saƙo ta tura mashi baya mata reply, a ƙarshe ma ya yi blocking duk wata hanya da zata haɗa su, har gidansu ta zo gaban mommynsa ta zuƙunna kan gwiwowinta tana kuka sha6e sha6e ta dinga roƙonta akan ta sasanta tsakaninta da Jazz in har bata aure sa ba mutuwa zata yi, shi kaɗai take so, ta yi danasanin komai da ta yi masa, ta tuba.
Turai ta tausaya mata musamman da ta ga ta gyara rayuwarta, ko shigar banza ta dai na yi, kullum cikin hijabi da jan cazbaha take, ta ce mata ta yi haƙuri zata yi magana da shi, amma ta ɗan ɗaga ƙafa saboda a yanzu jazz fushi ya ke yi da ita, ta bari sai lokacin da ya huce in sha Allah zata ci gaba da lallashin shi, da ƙyar ta shawo kan Faryat har ta samu ta koma gida, sai da ta kai ga kullum da zazza6i take kwana duk don saboda Jazz, Hajiya Saratu tasan komai da ke faruwa tsakanin Jazz da Faryat, amma bata sanya baki ba, saboda tana jin kunyar Jazz da Mahaifiyarsa, tsakaninta da Faryat addu'a ne da ta ke yi mata da kuma lallashinta.
Shi kan shi Jazz ɗin ba don ya daina sonta ba yake share ta, sai don yana son ta ji irin raɗaɗin da shima ya ji a lokacin da ta ke yi masa wulaƙanci saboda ta ga ya mutu akan ƙaunar ta, amma har lokacin bai daina sonta ba, yana da burin auranta.... 💔
A bangaren Zayn ya yi nadama tun bayan afkuwar lamarin, ya shiryu ya sauya halayensa daga munana zuwa kyawawa, ya zama mutumin kirki, ya daina biyewa matan banza daga shi har Zaid yanzu basu wasa da ibadar su ko a masallaci sune a sahun gaba, sa6anin da ko masallacin basu zuwa sai an tasa ƙeyar su suke zuwa yin sallah.
Soyayyar Zahra kullum ƙara nunkuwa take yi a cikin zuciyarsa, sai dai ya kasa tunkararta da maganar saboda kunyar wulaƙancin da ya yi mata a baya, duk da itama yasan hada mahaifinta a cikin elders, ƙaddarar su iri ɗaya, amma yana jin shakkun ya je gareta, gudun kada ta juya masa baya ko ta kore shi, da damuwa ta ishe shi ya kasa dannewa ya faɗa ma Zaid halin da yake a ciki, Zaid ya shawarce shi da ya shirya su je gidan su Zahran ya nemi yafiyarta yasan zata yafe mashi saboda yasan Zahra tana son shi.
A ranar da su ka je gidan su Zahra, bayan sun yi parking suka kasa fitowa su shiga ciki saboda zullumi, har sai da Abie ya fito daga gidan zai tafi Office ya hango baƙuwar mota a harabar gidan, suna ganin shi suka fito tare da nufar shi cikin girmamawa suka gaishe shi ya amsa masu da fara'a ya ce baigane su wanene ba kamar ƴan'uwan Owais, har suna haɗa baki gurin cewa eh ƴan uwansa ne su, ƴa'yan Hajiya Saratu sun zo ne suna son ganin Zahra, murmushi Abie ya yi ya ce su shiga daga ciki, godiya suka yi mashi tare da wucewa cikin gidan.
Sallamar su ce ta katse karatun ƙur'anin da Mahboob ya ke yi, sai da ya kai ƙarshen ayar da ya janyo, tukunna ya dube su yayin da yake akan kujera ruƙe da kur'ani, da murmushi ya amsa masu sallamar, sun ji daɗin sakin fuskar da ya yi musu.
Mahboob kenan bawan Allah tun bayan mutuwar Ana ya canza, yanzu gudun abun duniya ya ke yi, baya son kuɗi tun da ya ga yadda suke kai mutun ga halaka ya ji sun fita a ran shi.
A yanzu daka bashi kyautar kuɗi tsurar su ƙwara ka siya masa wani abu ka bashi saboda baya kar6ar kuɗi, har kawo wannan lokacin bai daina yiwa Ana addu'a ba, tana a ran shi, a duk lokacin da ya tuna zaluncin da mahaifinsu ya yi mata sai ya ji ɗaci a ran shi.
Bayan sun shiga cikin falon ya nuna masu sofas suka zauna, ya miƙa masu hannu suka yi musabaha, daga bisani Zaid Ya tambayesa ina mutanan gidan? ya ce su Umminsu basa nan sun tafi anguwa, amma Zahra tana a ɗaki tana bacci.
Sun ji daɗin jin tana nan, Zaid ya ce ya kira masu ita in ba damuwa, miƙewa ya yi ya nufi ɗakin Zahra ya yi sallama daga ciki ta amsa mashi, farkawar ta kenan daga bacci, bayan da ya faɗa mata baƙin da ke neman ta, ta yi mamakin jin zuwan Zayn, mutumin da ta sani da girman kai, tana kokwanton in shine! Me ma ya kawo shi gidansu nemanta bayan baya son ta? A ranta ta faɗa, har tambayar Mahboob ta yi ta ce ya kuwa tabbatar shi ɗinne ya zo? Yana murmushi ya ce mata da gaske shine ya zo tare da twin brother ɗinsa Zaid.
Cikin sauri ta sauko daga kan gadon ta shiga toilet, kafin fitowarta Mahboob ya wuce bedroom ɗinsa don ya basu guri su zanta.
Bayan ta fito daga toilet shaf shaf ta shirya kanta cikin abaya, ta fito ta nufi falon, tunkan ta ƙarasa ta hango su, har saida gabanta ya ɗan faɗi ganin abun da bata zata ba..
Zama ta yi kan sofa ɗin dake fuskantar su, ta yi masu barka da zuwa, bayan sun gaisa kowannansu ya yi shiru, sam Zayn ya kasa haɗa idanunshi da nata saboda nauyinta da yake ji amma ganinta da ya yi ya sanyaya zuciyar sa sosai, yana jin in har ya mallaketa zata sama masa farin cikin da ya rasa a rayuwarsa.
Jin sunyi shiru sun kasa magana yasa Zaid yanke shawarar fara gabatar mata da abun da ya kawo su..
Cikin nutsuwa ya fayyace mata komai ya ce yasan ɗan uwansa bai kyauta mata ba, ya yi mata wulaƙanci a baya, amma a yanzu ya yi nadama tun bayan fallasuwar sirrin grandpa ɗinsu da daddyn su sun sauya halinsu, koda can Zayn yana sonta, shi shaida ne saboda baida hira da ta wuce tata, amma a lokacin girman kai ne yasa bai nuna mata so ba.
Tun da ya fara yin maganar Zahra ta zare idanunta cike da mamaki take sauraron Zaid..
Bai ƙare maganar ba, Zayn ya kar6e da cewa, "Wallahi na shiryu Zahra, na gyara halayena, Ki tausaya ma rayuwana, nasan kin daina sona a yanzu amma ki yi haƙuri ki yafe min abun da na yi maki a baya, na yi danasani kuma wallahi ina son ki, in har kika bani dama zan nuna maki irin ƙaunar da na ke maki.
Tsantsar farin ciki ne ya lullu6e zuciyarta tsabar murna kamar ta zuba ruwa ƙasa ta sha amma kwata kwata bata bari ya gane ba, baiwar Allah tun bayan abun kunyar da ubansu ya aikata bata ƙara samun farin ciki irin na yau ba.
Da suka ga ta yi shiru babu fara'a akan fuskarta sai suka yi tunanin bata ji daɗin zuwan su bane, Zaid ya ce ta yi haƙuri idan kalamansu sun 6ata mata rai, za su tafi amma ta zauna tayi tunani idan ta yanke shawara ta sanar da su..
Ya ƙarashe maganar cikin sanyin murya tare da ruƙo hannun Zayn da ya tsareta da idanunshi, shi kaɗai yasan me yake ji a game da ita, baya jin zai iya haƙura su koma gida batare da Zahra ta faɗa masa ra'ayinta akan shi ba.
Zame hannunsa ya yi daga na Zaid ya miƙe daga kan kujerar ya je gaban sofa din da take a zaune ya yi kneeling a gaban ta, wani yanayi ta ji mara misaltuwa, ta kasa haɗa idanunta da nashi, cikin karyayyar murya ya ce, "Bazan iya tafiya batare da kin yafe min ba, nasan har yanzu kina fushi da ni, amma ki yi haƙuri Zahra! ki taimaki rayuwana, ki rufa min asiri, a halin yanzu zan iya haƙura da komai amma banda ke! Wallahi ban zo don na 6ata maki lokaci ba, Auren ki nake so na yi.. "
idanunsa cike tab da ƙwalla ya ƙarashe maganar, ji tayi kamar ta fashe da kuka saboda tausayin shi, cikin sauri ta ce ya tashi ya zauna, ya girgiza mata kai tare da cewa in har tana son ya miƙe toh ta faɗa masa me ta yanke akan shi.
Shiru ta yi tana tunani, a ranta ta ayyana Allah ne ya kar6i addu'arta, ta daɗe tana roƙon Allah ya karkato da hankalin Zayn akanta in alkhairi ne shi a rayuwarta, saboda tana son shi tana son ya zama mijin ta, sai gashi ya zo mata a lokacin da take buƙatar wanda zai rufa mata asiri, saboda samarin da take da su duk sun juya mata baya saboda abun kunyar da ubansu ya aikata amma yanzu ta yi farin ciki da zuwan Zayn saboda tasan ƙaddararsu ɗaya ce idan suka yi aure zasu rufawa kansu asiri, babu wanda zai goranta ma wani..
Numfasawa ta yi da ɗan murmushi akan fuskarta ta ce, "Ni ban fara son ka don in daina ba, har yanzu ina son ka, zan iya cewa na fi kowa farin ciki da ka gyara halayen ka, kuma na yi murnar ganin ka, sannan shawarar da na yanke na amince zan aure ka Zayn.. "
Bata ƙarashe maganar ba, ta ga ya yi sujjada yana kukan farin ciki, batasan sa'adda ta ji hawaye sun wanke fuskarta ba saboda daɗin da ta ji..
Hatta Zaid dake kallon su saida ya ji ƙwalla ta cika idanunshi, ya tausaya musu ya kuma ji daɗin nasarar da ɗan uwansa ya yi akan Zahra..
Tun a wannan lokacin shaƙuwa ta shiga tsakanin su, daga bisani da kanta ta kawo masu abinci da abun sha ta ce suyi haƙuri mamakin ganinsu ne ya mantar da ita bata kawo masu komai ba.
Duk da ba abincin ya kawo su ba, amma saida suka ci saboda ta matsa lamba akan su ci girkinta, aikuwa Zaid ya yi ta santi yana faɗin Zayn ya yi