Chapter 47 Reading KURKUKUN KADDARA FINAL STEP BY HAFSAT BATURE BOSS.txt Arewa Novels

KURKUKUN KADDARA FINAL STEP BY HAFSAT BATURE BOSS.txt

Author :  Boss Barture Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   47 / 107

138K to 141K   out of 319.4K words

ya lura da su.


A hankali ya ɗaura idanunshi akan fuskokinsu, Mutanan da har abada bazai ta6a mantawa da irin Butulcin da su ka yi masa ba, Tsantsar mamaki ne akan fuskokin kowan nan su daga shi har su din sun kasa motsawa.



Tun Lokacin da suka samu sa6ani Yau kimanin shekara goma sha takwas da zumuncin su Ya yanke basu kara haduwa ba kuma babu wanda ya nemi wani, sai yau da su ka yi haɗuwar bazata cikin ikon Allah agidan dg.


Wani irin nauyin shi da kunyarshi ne Ya lullu6e su,


Hajiya layla ji tayi kamar ta haƙa kasa ta binne kanta saboda kunyar Imam malik, duk tasha jinin jikinta, Saboda Kunya yasa ta dinga kare fuskarta da kasan hijab din ta.


Alhaji Ubaid kuwa Kasa jure hada idanunsa yayi dana sheikh Imam, wani irin kwarjini yayi masu.


A hankali Yake binsu da kallo mai wuyar fassaruwa..


Kamar yadda suke mamakin ganin shi haka shima Yake mamakin ganin su, komai daya faru arayuwar su suka soma tunanowa kamar a yanzu yake faruwa, ba zai ta6a mantawa da rashin mutuncin da sukayi mashi ba, ganin su da ya yi sai ya zamana kamar sun fama raunin dake a acikin zuciyarsa ne.


Kallon kallo su ke jefawa junan su, dr shureim da Benazir sun yi zuru da idanu kamar wadanda suka ma sarki Karya fadawa suka turke su.

Shureim ne yayi karfin halin tunkarar sa duk da shakkarshi da yake ji, zuƙunnawa ya yi daga gabansa cikin sanyin Murya ya gaishe da shi cike da fargaban martanin da zai mayar masa.

Kallonshi yayi kawai tare da juyawa ya haura kafarsa Ya nufi Ciki, Ransa Ya 6aci da ganinsu, Dayasan zai hadu da su da ba abunda zaisa Ya tako kafarsa Yazo gidan.


Kasa mikewa Dr shureim yayi, saboda karayar da zuciyarsa tayi, kwata kwata baiji haushin abun da baba Imam yayi masa ba, duk da baiji dadi ba, amma kome ya faru yafi ganin laifin iyayensa, saboda sune suka dasa masa ƙiyayyarsu a zuciyarshi..


"Ya shureim, ka yi haƙuri, Ka tashi mu shiga ciki" cikin sanyin Murya Benazir ta faɗa, yayin da take tunkararshi, Ta ruko hannunsa acikin nata, lokacin daya ɗago hawaye ne kwance a saman fuskarsa.


"Ba zan Iya shiga ciki ba, har yanzu baba Imam fushi yake damu, Nasan kona shiga bazai bari mu gana da Aisha ba, ku shiga zan jira ku a mota"

ya ƙarashe maganar kamar zai fashe da kuka.

Tsananin tausayinsa ne Ya kama su, iyayen nasa da yake sa ran zasu lallashe shi su taimaka masa ahalin da yake a ciki sam sun kasa magana saboda su kan su sun muzanta agaban Imam Malik, Gaba ɗaya sun sare har sun fara tunanin komawa Gida.


Basu Gama Yanke shawara ba, sai ga Motar Abie Ta kunno kai, daga Inda su ke suna iya hango su a cikin motar, mutum biyu ne agaban motar Abie da isod soldier.

Security Officers ne suka tsayar da su, amma daga baya suka ga Motar ta nufo ciki alamar sun samu iznin shigowa..

Yana tsayar da Motar, Anila ta fito daga back seat, fuskarta sharkaf da hawaye, ta goyo junaid abayanta, cikin sauri Ta nufi Benazir suka rungume Juna..

Daga Bisani Abie Da Mami suka fito Daga motar, kwata kwata babu walwala akan fuskokin su daga gani suna a cikin matsanancin Hali na damuwa.


Bayan sun gaggaysa da juna, Kafin daga bisani suka dunguma Izuwa Cikin gidan, Gaban kowan nan su na faduwa rass rass daram dararam saboda zullumin me zai biyo baya, gasu dai dukan su sun haɗu.


Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin kaninfari 1k Tsimin dabino 1k Gumba 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 4k
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 maganin Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki.


*Welcome, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan number din 08103884440*~_____💞______💗_____💘_____🌹______💋_____💫_____🫀___✍️~


Luxury-incense By Sapnah Borno.
Ta kawo muku turarukan wutan su Na maiduguri dana chad, turarukanta masu masifar dadi da kama waje harma da daukar hankali, indai kikayi kabbasa da turaren ta har wajen da kika zauna indai kika tashi sai kin bar kamshin ki, sannan Tana saida mayukan gashi irin nasu na shuwa Arab masu tasirin gaske, wajen gyaran Amare kuwa babu magana dan tazo muku da Chadian and Sudanese dilka Wanda zaki gyara jikinki da kanki, oga ya kasa ganeki, haka zalika akwai wata humrar ta mai suna hana bacci da kuma sirrin shuwa Abun ba magana, yar uwata ki jarraba turaren yar mutan borno nasan zata zame miki best turaren wuta plug. Tanada turarukan da zaki turara gida, toilet, bedsheets, curtains, kabbasa and hair incense ku jarraba kada ku bari ayi babu ku.
Wardrobe balls
Kabbasa spray
Chadian khumra
Hawee
Halud
Gabgab
Sandal sukkariya
Kajinguru
Dilka soap
Ready to use dilka
Karkar oil
Turaren tsuguno
Habil
Dorut
Dorot after period
Brown khumra
Dufr khumra
Body milk
Sudanese kuleccam
Chadian dufr kuleccam
Musk khumrah.

Maganin matan mu sunada inganci Wanda muke kawo su daga sudan, sannan munada maganin karin girman nono, Wanda basuda effects, ga masu bukatar maganin Matsi ko maganin mata Masu aiki garanti munada su, sannan muna zuwa gyaran jikin amarya a duk garin da take

Our Chadian aphrodisiacs are.
Beejay fire
Sata jagab honey
Wetness and sweetness combo
Daka
Great A sabaya
Breast engagement powder
Ciccibi
Gumbar madara
Gumbar dabino
Bita Zaizai

08093772168.




~____________________________________🍁🍁🍁~









*Me ya Faru Bayan shigar Sheikh Imam Malik*?





Ko sallama bai yi ba saboda 6acin ran da ya ke ciki, dakatawa ya yi yana tunanin meyasa Taj ya kira shi a irin wannan lokacin? Menene dalilin kiran nasa? Me kuma ya kawo Alhaji Ubaid da iyalinsa gidan?"



Yasan dai ba su da wata alaƙa da Chief Owais, zuciyarsa ce ta raya mashi ko dai sun kira sa ne saboda sun ji komai da ya faru tsakaninsa da ƴarsa, shiyasa suka kira su Alhaji Ubaid don su sasanta su.


Ƙunci ne ya mamaye shi, har ya juya zai fuce ya tsinkayi muryarta mai tattare da sautin kuka a cikin kunnanshi..

"Baba! Dan Allah kada ka tafi, ni nasa ya kira mini kai saboda ina son ganin ka, ina bukatarka a kusa da ni, ina so na yi magana da kai..."


Jin muryar gudan jininsa ya sa shi dakatawa da yin tafiya, ya manta when last ya ji muryar ƴarsa yayin da take kiran shi da sunan babanta.


Ganin bai da niyar juyowa ne yasa ta nufe shi tana kuka ta zube saman gwiwowinta a bayan shi, ta rurruƙe ƙafafunsa da hannayenta da ke kerma.


Ba zai iya misalta yanayin da ya shiga ba, ya ji wani irin abu da ba zai iya kwatanta shi ba, sam ya kasa magana.


Shesshekar kukan Aisha ya kashe mashi jiki, ya kuma fama masa raunin dake a cikin zuciyar shi, shekara goma sha takwas rabon da jikinsa ya haɗu dana gudan jininsa, ƴarsa ɗaya tilo da ya kora daga gidansa tare da jinjira a tsakar dare ba tare da ya yi tunanin wani hannu zasu faɗa ba, akan laifin da bata ji ba bata gani ba, wanda har yau idan ya tuna yana jin baƙin ciki mara misaltuwa.



Dakyar ta iya miƙewa ta rungume shi ta baya, tare da kwantar da kanta saman kafadarsa ta zagayo da hannayenta saman cikin shi.


Duk yadda zuciyarta ta kai ga tafarfasa da baƙin ciki sai da ta ji sanyi ya ratsa ta, jin ɗumin mahaifinta a jikin ta.

Hannayenta da ta ƙanƙame cikinsa da su ya bi da kallo, sai ya rinka tuna ranar da mahaifiyarta ta haife masa ita, ta damƙa masa amanarta tana atsaka da fuskantar ajalinta, hakika ya ci amanar malama Batool.


Hawayen da suka cika idanunsa ne suka fara zarya kan kuncinsa.


"Baba! meyasa baka ta6a nemana ba, tsawon shekara goma sha takwas, bakasan irin rayuwar da na yi ba, hankalinka a kwance ka ke gudanar da rayuwar ka, baka ta6a tunanin wani hali nake a ciki ba, ina lafiya ko bana lafiya, ina raye ko bana raye, duk da abun da ka yi min hakan bai hana zuciyata tunanin ka ba, kullum ina sa ran zaka neme ni, amma shiru har sai da na fidda rai da ina da uba a duniyar nan, ka yi min iyaka da kowa nawa, baba hankalinka a kwance kake rayuwarka bayan ƴarka ɗaya tilo da kake da ita tana rayuwa a wani wurin, ko har yanzu fushi ka ke da ni? Baba ka ta6a danasanin abun da ka yi mini? Ka kuwa san halin da kasa na jefa rayuwata?"



Maganganunta sun karya zuciyar shi, duk yadda ya kaiga jurewa saida kuka ya kubce masa, jikinsa na kerma ya ruko hannunta tare da zagayo da ita, ya rungume ta akan ƙirjinsa da hannayensa biyu ya tallabe bayanta.


Komai dake faruwa akan idanun Alhaji Ubaid da iyalinsa, haka zalika akan idanun Abie da iyalinsa, da kuma Taj wanda ke a tsaye gefe ɗaya.

Idanun kowan nan su ya cika tab da ƙwalla saboda tsantsar tausayin Aisha da mahaifinta, kamar sun samu tv haka suke ta kallon su.


Cikin shesshekar kuka da rauni ya furta, "Ki yafe mini Aisha, hakkinki ne ke bibiyar rayuwata, na ci amanar mahaifiyarki, na cuce ki na kuma cuci kaina..."

ya ɗan dakata yana mayar da numfashi, fuskarsa har kerma ta ke yi.


Daƙyar ya ɗaura da cewa, "Taya zan guji gudan jinina kuma in zauna lafiya? Allah shine shaidata, wallahi na yi danasani tun a daren ranar dana kore ki na gane kuskure na, bansan meyasa nayi maki haka ba Aisha! Bana a cikin hayyacina Aisha, bayin kaina bane, ina tsaka da bacci na farka da tsanarki a zuciyata, na ji kin fita araina, kawai bana son ganin ki, kamar ana tunzura ni, a lokacin ji nake in har ban kore ki ba zan iya rasa raina, na daɗe ina tambayar kaina meyasa na yanke maki ɗanyen hukunci! Bayan nafi kowa sanin wacece ƴata, Aisha, bazan iya misalta maki mawuyacin halin da na shiga ba bayan dana neme ki na rasa, na yi kukan da ban ta6a ƴinsa ba arayuwata, na tsani kaina, na ƙuntata rayuwata, na ji rayuwar duniyar ma ta sire mini, mutuwa nakes o kawai na yi, Aisha gidan mahaukata ne kawai ban je ba, amma na yi haukan rashin ki, har kulle kaina na yi tsawon kwanaki ba asan inda nake ba ba ci ba sha, na yi rashin lafiyar data yi silar kwantar da ni asibiti, na yi jinya kamar bazan rayu ba, bansan wa ke akaina ba, saida ta kai ga sunanki kaɗai nake fada a cikin sambatuna, Aisha yanzu haka da nake maki magana ina da ciwon zuciya, Allah ne bai ƙaddara zan mutu ba, shiyasa na kawo har wannan lokacin a raye..."


Shesshekar kukan Benazir da Anila ne ya cika kunnuwan kowan nan su.

"Aisha ban manta dake ba, da ke nake kwana da ke na ke tashi araina, addu'ar da nake maki kullum a cikin sallata ban daina ba, kamar yadda ki ke sa ran zan neme ki nima haka nayi ta sa ran wata rana zaki dawo ki neme ni, amma baki ta6a tunanin kiyi hakan ba, shiyasa zuciyata ta karaya na yi tunanin ko kin mutu ne ko kuwa abun da na yi maki ne yasa baki ta6a nema ba..." Ya ɗan dakata yana mayar da numfashi.


"Bani da kwanciyar hankali saboda zullumi da fargaban a wani hali kike a ciki, kullum saina kira layinki amma ban ta6a samun shi a kunne ba, kuma ban fidda rai ba, kullum addu'ata idan kina a raye keda jinjirarki Allah ya kare mun ku a duk inda ku ke, Ya zama gatan ku, Ya kuma haɗa ni da ku, idan kuma baku a raye Allah Ya jikanku da rahamarsa, ban ta6a gajiyawa ba da neman ku, saboda ku na sha zuwa aikin hajji don in yi maku addu'a..."


Kasa karasa maganar ya yi saboda raunin da zuciyarshi ta yi, baiwar Allah ta yi kuka kamar ranta zai fita, bata taba tunanin ya damu da ita har hakan ba, ta yi zaton yana sane ya yi watsi da ita shiyasa bata ta6a tunanin ta dawo gida ba tun da bai neme ta ba, ta yi zaton har yanzu fushi ya ke yi da ita.




Tallabo fuskarta ya yi da tafukan sa, idanunsu da ke tsiyayar da kwalla suka haɗu cikin na juna.


"Aisha, saboda ke na ajiye aikina na rabu da kowa nawa, a karshe ma da na yi jiran shiru baki dawo ba, sai na bar ƙasar ba tare da sanin kowa ba."


Numfasawa ya yi tare da girgiza kansa cike da danasani ya daura da cewa, "A ranar dana fara ganin ki a gidan nan, wani irin farin ciki mara misaltuwa na ji, kamar anyi min albishir da gidan aljanna, saboda na ji daɗin ganinki da ranki da lafiyarki, duk da na shiga tashin hankali saboda sauyin da na gani a tare dake, daga yanayin shigarki, na gane kin canza hali, har saida na yi kokwanton anya Aisha nane?"

Amma saboda jinina dake yawo a jikinki yasa ban musa ba, a lokacin dalilin da yasa ban yi ma ki magana ba, saboda ina jin kunyarki, kema kuma sai kika nuna kamar baki taba sanina ba, shiyasa jikina ya yi sanyi, amma bayan na koma gida saboda farin ciki ban iya runtsawa ba, kwana na yi ina nafilfili don nuna godiyata ga Allah da ya bayyanar min da ke, har so nake Chief ya gayyace ni don in zo gidan nan saboda kawai zumudin in ganki.. "

komai saida Imam ya fayyace mata na daga halin da ya shiga bayan rabuwar shi da ita.


Bai ƙare maganar ba, Ya saki fuskarta da ya tallabe, ya tattare ƙasan jallabiyar Jikin shi da niyar ya zuƙunna kan gwiwowinsa don ya nemi yafiyar ta.


Lura da hakan yasa ta yi saurin ƙanƙame shi tana rokonshi akan kada ya zuƙunna mata, ya bari, kada ya yi, idan ma akwai wanda ya cancanta ya nemi yafiyar wani atsakanin su toh ita yakamata ta nemi yafiyar sa, yana kuka ya ce mata ta barshi ya zukunna, idan har baiyi hakan ba bazai ta6a yafe ma kansa ba, koda ta yafe masa, saboda ya dade yana yi ma kanshi kallon mugun Uba, mara imani, saboda rashin adalcin da bai yi mata ba.
Ta fashe da wani sabon kukan ta ce, "Baba babu yafiya atsakanin mu, abun da ya faru bayin kanka bane, haka zalika abun da ya faru tsakanina da yaya Shureim bayin kan shi bane, a yau na ji komai baba. Na ji abun da ya ɗaga hankalina ya kuma karya zuciyata, Baba ashe dama makirci ne aka kulla min saboda a ɗauki fansa akanka?"

Kaitsaye maganar ta ratsa kunnuwansu, a ruɗe suke kallonta.


Muryarsa na rawa ya furta, "Bangane me kike nufi ba? ki yi min bayani yadda zan fahimta!"

Gajiya ta yi da tsayuwa, hakan yasa ta zauna shima ya zauna yana fuskantarta, yayin da sauran mutanan dake a falon suke atsaitsaye babu alamun gajiya a tare da su.



"Ke nake sauraro Aisha.." A ƙagare da son ji duk da yana fargaban abun da ya daɗe yana zargi ya zamana gaskiya.


"Baba, zan faɗa maka, amma zan roke ka, dan Allah ka yi min alkawarin zaka jure komai da za ka ji daga gare ni, kuma duk abun da zan faɗa maka ya riga da ya wuce, kuma anyi ne don a cusa maka baƙin cikin da zai yi silar mutuwarka, sannan kuma a lalata martabarka da ƙimarka, in har ka tada hankalinka akan abun da za ka ji toh zai yi nasara ne, shiyasa bana so ka sanya damuwa a ranka, nasan za ka ji raɗaɗin da yafi na ƙunar wuta zafi a cikin zuciyarka amma ina so ka tuna komai ya faru a rayuwar mu mukaddari ne daga Allah, ka ɗauki hakan a matsayin jarabawa da Allah ke yiwa bayinSa muminai, mu yi hakuri da cutarwar da aka yi mana, In sha Allah zamu ga ribar hakurin da muka yi, kuma Allah zai yi mana sakayya"



Cikin sanyin murya ta ƙarasa maganar tana kallon fuskar mahaifin nata dake kallonta da rinannun idanunsa.


Unexpectected ta ji ya furta, "Musa!"

kowa da ke a falon sai da gabansa ya faɗi da jin sunan da ya ambata.


Ba ta yi mamakin Jin ya canki sunan shi ba, dama tasan dole ya zo masa a rai tun da shine babban maƙiyinsa a duniyar nan.


"Ki faɗamin shine ko? Shine ya shiga tsakanina da ke ko?" Cike da damuwa ya tambaya,


Fargaban amsa mashi ta ke yi saboda zullum halin da zai shiga, tasan mahaifin nata da zuciya komai zai iya faruwa.



Daƙyar ta jinjina mashi kai cikin raunanniyar murya ta ce, "Shine baba, uncle Musa, ya daɗe yana ƙulla makirci atsakanin mu, ban ta6a ganin azzalumin mutun irinsa ba, ya karya mini zuciyata, ya ha'ince mu, wata shari'ar sai a lahira, amma ya cutar da rayuwar mu..."


kamar a mafarki suke sauraron maganar Aisha, gaba daya sun

47 / 107