DAFIN HARSHE BOOK ONE BY Maimunatu Iyam.txt

Author :  Maimuna Tijjani Iyam Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   28 / 32

81K to 84K   out of 95.1K words

isa kan munbarin ina karantu auziya da bismillah wajen ta kaure da kabbara na ci gaba da karatun suratul Maryam cikin sanyin murya wajen ya yi shuru ina cikin karanton na hango shigowar Umma da Umman Amira. Sai da na karance suran tas kana aka yi kabbara da alama hatta su Malam Suleiman sun ji daɗin karatun da na yi fiye da na sauran.

Aka bayyana ni a matsayin wacce ta yi na ɗaya. Aka ƙira wani basarake ya ba ni kyautata ya kuma ba ni wasu kuɗaɗen da ban san adadin yawansu, zan tafi aka ce na tsaya aka kara ayyana ni a mashin gwarzuwan shekara kuma ɗaliba mace ta farko ta yi sama iri wannan nasarar cikin shekaru goma da kafa islamiyyar. Sannan aka ayyana ni a matsayin ɗaliba mafi hazaƙa a cikin ajinmu. Malam Aminu ya ɗauko kyautar da za a ba ni ya ƙira sunan Sheikh Dawood a matsayin wanda zai karrama ni da kyauta ya taso cikin shirgar alfarma, tun da ya taso nake bin sa da kallo har ya iso wajen. Ya karɓa lasifikan ya soma jawabi.

"Yau na cika da murna da farin ciki ganin yadda aka yaye ɗalibai masu yawan gaske kuma duk sun haddace littafi mai tsarki. Ina jinjinawa malamanku ƙwarai da gaske da suka tsaya kai da fata wajen tabbatar da sun sama ilmi mai inganci. Wannan ɗalibar da ta yi na ɗaya kuma ina yi mata fatan alkhairi da addu'ar dacewa a cikin rayuwarta. Sannan idan mahaifi ko mahaifiyarta yana wajen wannan taron ina so a taso ya hau kan munbari domin na yi masa wani albishir".
Aka dinga kwarara kabbara har Abba ya iso wajen suka yi musaba kana Sheikh Dawood ya ci gaba da jawabinsa.

"Bawan Allah da farko ina taya ka murna domin Allah ya yi maka arzikin da ba kowa ne yake dacewa da irin sa. Wannan ɗiya taka zinariya ce a cikin zinaru, idan akwai wani karatun da take yi ko kuma za ta fara to na ɗauki ɗawainiyyarta daga yanzu har ta gama shi, idan kuma daga nan aure za ta yi to na ɗauki nauyin yi mata kayan ɗaki da duk wani abun da ake yi mace yayin bikinta. Zan karrama ta cikin alkyabba mafi daraja da tsada".

Wajen gabaɗaya ya ruɗe ya sa aka ɗauko wata alkyabba mai tsananin sheƙi da ƙyalle wanda ko da daga kallo guda ka san cewa mai tsada ce balle kuma ace ka murza jikinta. Ya ɗaura mini ita a kaina idanumu suka sarƙafe cikin na juna, take na ji raina yana tafasa sakamakon wani irin kallon da yake yi mini da na kasa gano ma'anarsa.
Abbana sai godiya yake zuba wa yana yi yana ƙarawa, ɗan takarar kansila da sarakuna duk suka gaisa da shi tare da yi mini kyaututtuka masu tsoka.

"Ina taya ki murna matuƙa kuma ina addu'ar Allah ya sanya albarka a karatunki".

Da sauri na ɗago kaina don tabbatar da mamallakin wannan muryar da ta kasa gogewa daga cikin kaina. Caraf idanuna suka sauƙa akan sa yana tsaye a gabana fuskar ɗauke da maɗaukaki murmushi. Hannunsa riƙe da alƙur'ani da aka yi ado da wasu irin zare masu jan hankali. Ya miƙo sai dai mamaki ya hana ni karɓa balle na ce da shi wani abu.
Sai da na ja dogon numfashi na fesar kafin na ce"Muhammad Taufik ko?". Ya sakar mini da murmushin yana faɗin"karɓi mana kin tsaya ki na ta kallo na". Jikina a sanyaye tamkar kazar da aka kwararawa ruwan zafi na kai hannu na amsa alƙur'anin.

"Ina taya ki murna Allah ya albarkacin karatun da aka yi. Kafin ku tafi zan neme ki". Kaina kawai na girgiza masa kafin na ce wani abu Malam Aminu ya iso wajen ya ƙira gefe.
"Amatullah mu je Sheikh yana son magana da ke". Take na ji ƙirjina ya buga ya yi gaba ina bin shi a baya har gaban Sheikh na durƙusa a ƙasa, ya ƙura mini idanu kamar zai cinye ni ɗanya ya ɗauko wasu littattafai ya miƙo mini na miƙa hannu zan karɓa caraf na ji ya riƙe hannuna gam. Babu shiri na ɗago idona ina kallonsa sai dai ko a jikinsa sai murza mini hannuwa da yake, sai da na sa ƙarfi kafin na kwace hannuna. Na yi zumbur zan tashi wani jiri ya ɗauke ni duk yadda na so tsayiwa akan ƙafata lamarin ya ci tura, Malam Aminu da yake kusa da ni ya yi saurin karɓan alƙur'anin da yake hannunsa da sauran kyaututtukan.

Luu na yi baya na faɗi a ƙasa ina jin kaina yana juyawa jikina gaba ya sake, mutane suka cika a kaina ina ganin su dishi-dishi.
"Amatullah lafiya kike kuwa?". Muryar Yaya Alhassan kenan da ya kasance abu na ƙarshe da na ji kafin hankalina ya gushe, aka ɗauke ni ridi-ridi sai asibiti. A hankali na soma buɗe idanuna da na ji sun yi mini matuƙar nauyi ina ƙarewa ɗakin da nake cikinsa kallo. Sai da na ƙarewa ɗakin kallo na tabbatar da cewar asibiti ne. Ummata, Umma Amira, Anty Sawwama da kuma Amira, Anty Zulaihatu su kenan a cikin ɗakin. Suka fara jeranta mini sannu wani na bin wani kafin na kai ga amsawa Abba, Yaya Alhassan, Umar da Malam Suleiman suka shigo cikin ɗakin cikin wani irin matsanancin firgici da tashin hankali, na lura idon Abba har da hawaye ya kafe ni da idanuna kamar ya ga wata sabuwar halitta.

Kafin na yi aune ko na ce wani abu tunin Abba ya wanke ni da mari, ina ɗagowa ya ƙara wanka mini wani marin. Su Umma duk suka tattaso suna tambayar ko lafiya.
[10/25, 8:15 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*

©️ Maimuna Tijjani Iyam

_______________________________________

Page 3️⃣6️⃣

"Munniru lafiya kuwa? Za ka ɗauke yarinya da mari alhalin tana gadon asibiti cikin jinya". Ta juya tana duban Yaya Alhassan da tun da suka shiga kansa yake ƙasa ya gaza ɗago ido balle ya kalli kowa.
"Alhassan wai me ye likitan ya shaida muku ne? Me yake faruwa da Amatullah ɗin?". Bai ɗago kansa ya kalle ta ba kamar yadda bai amsa mata ba.

"Ba fa zai yiyuwa a tisa min ɗiya a gaba da duka ba akan wani dalilin? Tana cikin jinya idan ba a lallashe ta ba ai ba za tada mata da hankali ba, wallahi ba za ta saɓu ba wai bindiga a ruwa".
"Hafsatu ki rufe min baki tun kafin na yi sassaɓa miki a nan wajen nan. Kin cuce ni kin cuci rayuwar ƴarki. Hafsatu kin wargaza min duk tanadi da shirin da na yi wa rayuwar Amatullah, kin jefa ni cikin kunya da tsoron haɗuwa da mutane balle har na shiga cikin su na yi mu'amala da su, tsakani na da ke Allah ya isa ban yafe miki". Gabaɗaya wajen ya ɗauki salati da sallallami Umma ta hau hayagaga ta inda ta shiga ba ta nan take fita ba, sai da Umman Amira ta taso ta riƙe ta tana ba ta haƙuri da tunatar da ita cewar a asibiti fa muke.
Kuka nake yi da dukkan ƙarfina jikina gabaɗaya yana rawa tamkar mazari haƙwarana suna karabɗiya da juna kamar jinriran kazar da ruwa ya yi wa ɗan banzan duka.
"Don Allah ku ba mu waje ina son ganawa da Amatullah ita kaɗai". Abba ya yi zancen cikin tsantsan tashin hankali da ruɗewan da ya bayyana har a cikin muryarsa.

"Ai ba kai kaɗai ka haifa yarinyar ba Manniru don haka babu inda zan je, komai a gaba na za ku tattaunawa. Ai ni ma ina da iko akanta kamar yadda kake jin kai ma kana da cikakken iko akan ta". Umma ta yi zancen cikin isa da izgilanci da ƙyar Umman Amira ta shawo kanta ta yarda ta fita daga cikin ɗakin, ya rage daga ni sai Abba a cikin ɗakin har zuwa lokacin kuka nake yi duk da ban san abin da yake faruwa ba amma na yi imanin duk abin da zai sanya Abba shiga makamancin irin wannan tashin gami da furta zafafan kalamai ba ƙaramin abu ba ne.

Ya zauna a kusa da ƙafafuna ya kafe ni da ido lamarin da ya ƙara sanya jikina yin sanyi ƙalau don bai taɓa yi mini irin wannan dogo kallon ba.
"Amatullah".

"Na'am Abba". Na amsa muryata a kashe tamkar wacce aka sanya igiyar kirtani aka shaƙewa wuya tamau.
"Amatullah ki na ɗaya daga cikin jerin matan da na yarda da su a cikin rayuwata kuma na yi imanin ba za su taɓa cin amanata ko su kunyata ni ba. Tun ranar da kika zo duniya aka cirewa mahaifiyarki mahaifa sakamakon irin wahala da azabar da ta sha tun daga rainon cikinki har izuwa lokacin haihuwarki. Ya tabbatar ba za ta sake haihuwa ba a duniya haka ni ma inda ba wata macen na aura to ba zan sake haihuwa ba tun da an raba ta da mahaifa, tun daga lokacin na yuƙurce a raina cewar zan tarbiyyartar da ke na ba ki kula na ba ki ilmin addini ta yadda za ki zame mini madadin ƴaƴa goma a gare ni, kuma alhamdulillah haƙiƙa na cika da farin cikin a yau ganin kin haddace littafin alƙur'ani akan ki babu abin da zan ce Allah sai dai godiya. Amma me yasa kika zaɓi ki jirkita min wannan ranar ta farin ciki zuwa ta baƙi ciki da kasance rana mafi muni a gare ni?".

Bai ba ni daman cewa wani abu ba ya ci gaba da cewa"Allah ne shaidana domin ba ya bacci yana ganin duk abin da yake na zahiri da na baɗili. Ya san na kula da amanarki da ya ba ni daidai da rana guda ban taɓa barin ki kin sauƙa daga tafarkin addinin da Manzon ya zo mana da shi ba. Amma Amatullah me yasa kika zaɓa ki saka min ta wannan hanyar? Me yasa kika zaɓa ki shayar da zuciyata raɗaɗin baƙin cikin da ba zai taɓa bari na yi rayuwa cikin farin ciki da walwala ba?". Na tuntsire da wani irin kuka mai ƙarfi numfashina har ɗaukewa yake yi.

"Amatullah likita ya tabbatar mana da cewar ki na ɗauke da ciki a jikinki na tsawon sati biyu, Uwata wa ya yi miki ciki?". Mutuwa zaune na yi don cak numfashina ya ɗauke na wucen gadi na dawo da ni da gawa ba mu da maraba. Na ji duniyar gabaɗaya tana juya mini ban dawo daidai ba sai na ji sauƙan wani abu mai zafi a fuska da ya ratsa dukkan sassan jikina wanda ina da tabbacin ruwa Abba ya watsa mini a fuska. Na ci gaba da wani irin kuka wanda ya yanayin da irin zafin da nake cikin a ƙirjina ba na jin akwai kalmomi da za su wadatar wajen fassaruwansa. Duk yadda na so na yu magana baki ya ƙi ba ni haɗin kaina furta abin da yake yi mini ƙaiƙayi a cikin raina. Hankalina ya kai ƙololuwan tashin ganin hawaye suna zuba daga idanun Abba ya sukunyar da kansa ƙasa ba tare da ya ƙara cewa da ni komai ba. Tun ina yin kukan idanuna suna zubar da ƙwalla har sai na da idanuna suka kafe tsiyayar da komai.

"Abba". Na furta cikin wani iriyar muryar mai cike da rauni haɗi da maɗaukakin tashin hankalin da ya jirkice da rashin nutsuwa, shuru bai tanka mini na ƙara ƙira a karo na biyu nan ma shuru ina jijjiga shi na ga ya faɗi a ƙasa idanunsa sun kakkafe bakinsa ya koma gefe guda.
Na ɗaura hannu aka na fasa ihun da ya sanya su Umma faɗowa cikin ɗakin tamkar an jefo shi.
"Innalillahi wa inna ilahirin alaihir raji'un! Me ya same shi?". Anty Sawwama ta jefa mini tambayar da na gaza amsa wa illa kukan da nake ji jikina yana rawa.

Yaya Alhassan da Malam Aminu suka ɗaga shi suka kwantar da shi akan gadon da na tashi, Umman Amira ta fita ta ƙira likita ya shigo ya umarce mu da duk mu fita. Sai dai ni kam na kasa motsa ƙafafuna daga inda nake tsaye duk da jan hannuna da Amira take yi kamar za ta fincike shi daga gangar jikina. Ganin halin da nake ciki ya san likitan da kansa cewa a ƙyale ni haka suka fita suka bar ni a wajen, na ja saƙararran gangar jikina na isa na durƙusa gaban gadon da Abba yake kwance na riƙe hannunsa ina murzawa a hankali. Likitoci suka rufu akan sa suna ta ƙoƙarin ceto rayuwarsa domin har jijjiga ya fara aka ɗauko wani abu kamar dutsin guga ana danna masa a ƙirjinsa.

Sun ɗau lokaci a haka har sai da komai ya daidaita aka maƙala masa roban numfashi.
"Ki yi haƙuri ki tashi ki fita waje, in sha Allah zai sama lafiya kamar yadda kike gani ma ai yanzu da sauƙi". Likitan ya furta cikin sanyin harshe da sassauta amonsa. Na cira kai ina kallonsa"don Allah zai tashi kuwa?".

"Me zai hana shi tashi? In sha Allah zai tashi ya sama lafiya ya ci gaba da gudanar da rayuwarsa tamkar babu wani abun da ya taɓa faruwa".

Ban ce da shi komai ba na kuma fashewa da wani kukan ina murza hannun Abba da yake cikin nawa. Lokacin guda har fuskarsa ta faɗa tafin hannunsa ya yi sanyi ƙalau kamar wanda aka ɗaurawa ƙanƙara.
Aka bankaɗo ƙofar ɗakin na waigo ina ganin Umma da ta faɗo cikin ɗakin a fusace tamkar kububuwa tsoro ya mamaye mini ƙalbina, kafin na yi wani yunƙuri na ji ta rufe ni da duka da ko'ina ana ƙoƙarin raba ni da numfashina. Ta buga kaina a jikin ƙarfe gadon take jini ya ce sallama Alaikum ya fara malala kamar da bakin ƙwarya. Da ƙyar likitotin suka ɓanɓare ta daga jikina duk da hakan bakinta bai fasa furta mini mungayen kalmomi ba.

"Allah ya isa tsakanina da ke Amatullah. Da haihuwarki irin ki gwara na rayu har na koma ga mahaliccina ba tare da na yi ko ɓatan wata ba, da na san haka za ki zame min annoba da tun ranar da kika zo duniya na murɗe miki wuya kin mutu kowa ya huta, na tsane ki na tsani kallon ki. Da wannan abun kunyar da kika ɗauko mana gwara a kawo min gawarki a gaba na hankalina sai ya fi kwanciya".

Na rarrafo na zo na riƙe ƙafafunta"don girman zatin Allah Umma ki yi haƙuri kar ki furta mini kalmar da za su jirkita tunanina. Umma ki ba ni dama na yi miki bayani wallahi ƙaddara ce ta faɗa mini...". Tun kafin na ƙarisa ta sa ƙafa ta yi bol da ni na faɗi gefe guda, babu shiri na saki ihu saboda zafin da na ji ya ratsa har cikin ƙoƙon kaina.
"Ke ba ki da hankali ne? Idan kika ji mata ciwo fa? Ko me ta yi ai kamata ya yi ki bari sai kun je gida ko kin manta cewa nan asibiti kuma a cikin ɗakin majinyaci kuke kike wannan hayaniyan. Ku tattara ku fita waje don ba ma buƙatar hayaniya da ɗaga murya a nan".

Likitan ya yi zancen cikin ƙololuwar ɓacin rai da takaicin abin da Umma ta aikata, Umman Amira da Anty Sawwama suka shigo suka fitar da Umma Amira ta ɗago ni likitan ya ce na fito a bar Abba ya huta muka je wani waje a cikin asibitin aka yi mini dressing ɗin goshina da yake zubar da jini. Ana gamawa Anty Sawwama ta ce mu tafi gida Yaya Alhassan zai zauna a wajen Abba kafin a ga abin da hali zai yi.

"Anty don Allah ku yi haƙuri ku bar ni a nan...". Kafin na rufe bakina ta katse ni"kar ki yi gardama da ni Amatullah ki wuce mu tafi". Ban ƙara cewa komai don ban ga fuskar hakan daga gare ta ba. Malam Aminu da Yaya Alhassan da Muhammad Taukif suka iso wajen a tare duk su ukun suka jefo mini wani matsanancin kallo. Ba kamar Malam Aminu da har cije baki yake yi, shi ya fara tafiya bayan Anty Sawwama ta zabga masa godiyar ɗawainiyyar da ya yi.

"Anty na ga kamar ku ma tafiya za ku yi ko zan sauƙo a gida. Daga nan ni ma sai na wuce". Muhammad Taufik ya yi zancen idanunsa akan Anty Sawwama.
"A'a ɗan nan tun da lamarin nan ya faru kake ɗawainiyya da mu, kai ka kawo mu asibitin nan mai tsada a cikin motarka sannan ka biya kuɗin komai da komai, ɗawainiyyar ai sai ta yi yawa ka yi tafiyarka kawai za mu hau motar hanya".

"Mahaifina ya umarce ni da na tsaya akan lamarin wannan baiwar Allahn nan har sai na tabbatar da cewar komai ya warware. Don haka ina roƙonki da ki taimaka mini wajen cika umarnin mahaifina". Shuru Anty Sawwama ta yi kawai tana jijjiga kanta kana ta ce"shikenan to mun gode". Suka yi sallama da Yaya Alhassan bayan sun yi musayar lambar wayan juna ya yi gaba muna biye da shi a bayan, a Umma da Umman Amira tunin sun tafi gida.
Kamar motar gawa tun da muka shiga babu wanda ko tari har muka isa gidan, Anty Sawwama da Amira suka yi masa godiya ni kam na kasa cewa komai illa kallon juna da muke yi ni da shi.

Muna sanya ƙafarmu a cikin filin tsakar gidan Umma ta tare mu tamkar daman jiran shigowarmu take yi.
"Kar ki sake ki nufo ɗakin nan shegiya tsinanniya kawai. Amatullah kin ja min abin magana da yamaɗiɗi a cikin gari ki jawo min abin kunya, kar ki matso inda don babu makawa matuƙar muka haɗa wajen zama da ke zuciya za ta iya ɗiba na na murɗe miki wuya".

"Subhanallahi! Haba Hafsatu idan hankali ya gushe ai hankali ake sawa a nemo shi. Ki yayyafawa zuciyarki ruwan sanyi sai a zauna a nemo yadda za a ɗinke wannan ɓarakar da ta same mu gabaɗaya".

Kalaman Anty Sawwama kamar aka fusata Umma suka yi ta cika ta yi fam.
"Maman Umar ki fitar da yarinyar nan daga cikin gidan duk kafin na biye zuciyata na aikata abin da daga ni har ke za mu zo muna cizon ɗan tsaya daga baya".
Anty Sawwama ta dafe kai"innalillahi wa inna

28 / 32