L U'U L U'U BOOK COMPLETE HAUSA NOVELS BY HUGUMA.txt

Author :  Safiyya Abdullahi Huguma Category :  New Hausa Novels 2026

Chapter   7 / 21

18K to 21K   out of 62.7K words

rabo sa a Zuzeam ventures takuce πŸ₯°πŸ‘πŸΌ
Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah πŸ₯°πŸ‘ŒπŸ»
😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki
____________________________




Da kallo morsa safiyya ta bita,tana jin wani abu yana taba zuciyarta sosai,wani irin qaqqarfan abu me matuqar tasiri a zuciya.

"Allah ya tsare hanya......ya bada sa'a,ki kula da kanki,ki kula da mutuncinki..........ki kuma tsare martabar gidanku data mahafinki" Kusan kowanne lokaci wadannan sune kalamanta kuma maganganunta a kanta a duk sanda ta samu sukunin yi mata sallama. Bata ce komai da ita ba taci gaba da takawa tana fita......hakan kuma bai hana morsa safiyya binta da idanuwa ba har sai data bacewa ganinta.

Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana jin sassan jikinta suna yin wani irin sanyi. Koda wasa akace mata irin haka zai taba gwada faruwa tsakaninta da jinin safeena ba shakka zata qaryata. Da gaske rayuwa wani mafarki ne na daban. Wani mafarki ne da zuciyoyi da ruhi keyi ba tare da samun yaqinin tabbatuwarsu a sanda ake kan ginasu ba. Safeenarta.......halitta mafi soyuwa a ruhinta dama kafatanin rayuwarta gaba daya......yanzun dama akwai sanda lokaci zaizo da irin wannan yanayin tsakaninta da jinin SAFEENA?.

Taja siririn tsaki aqalla ya kusa sau biyar kafin ta isa sassan mammina. Tarin hadiman dake sassan suka shiga marabtarta cikin matsanancin ban girma,saidai ba wanda ta samu amsawa. Hakan ba baqon abu bane a wajensu,musamman idan tana jin 'yan izzarta a kusa,ko kuma 'yan miskilancin suka motsa mata. Ko baya ga haka kuma dama ita din muryarta kamar wani abune me daraja a tare da ita da ba kowanne guri take sakinta ba.

"Ki gafarceni.......uwar daki tana cikin muhimmiyar ganawa......bata kuma bada izinin shigar kowa ba har sai bayan ta kammala" . Bayanan tafisu ta yiwa akhnan kenan,wadda ta isa direct ga qofar kebantaccen parlor din hajiya zaitun da tasan a lokaci irin wannan anfi samunta a can.

Wani irin kallo akhnan ta dago ta watsawa tafisu,tana mata wani duba na qanqanci da kuma zallar mamaki.

"Hala wani abunne a kanki?.......kinsan dawa kike magana kuwa?" Akhnan ta furta cikin izzar nan tata dake bayyana cikin kowanne motsi nata.

Rawa jikin tafisu ya dauka,kwarjinin akhnan din sosai ya daketa,ya kuma tarwatsa duk wata juriya da takejin tana da ita na tsaida akhnan din.

"Zaki fuskanci hukunci.......tabbas zaki fuskanci hukuncin tsaidani da kuma batamin lokaci da kikayi" Ta qarasa maganar tana tura qofar,daidai sanda tafisu ta zube muryarta da jikinta dukka suna rawa.

"Tuba nake.......afuwa nake nema ki yafeni......kiyimin rai".

Bata ko saurareta ba ta sanya kai cikin parlor dake da qofofi biyu na musamman,ta cikin gidan da kuma wata qofar daban ta bayan ainihin ginin.

"Yaya sunanshi?......." Kalaman mammina kenan da taji wanda bata ko ta kansu ba ta motsa bakinta a izzace ta saki siririyar sallama tana sauke idanunta ga faffadan mutumin dake duqe a gabanta kamar me neman gafara.

"Sunan......." Ya buda baki da nufin bada amsa tambayar da akayi masa,saidai amsa sallamar da yaji mammina tana yi ya dakatar dashi,ya kuma daga kansa da hanzari yana duban me shigowar. Sam baiji motsi ko sallamar kowa ba......don haka baisan da shigowar kowa din ba.

Idanu mammina ta kafeta dashi na sakannin da suka kusa biyar kafin ta sakar mata murmushi.

"Karkicemin sai tafiya?" Ta fadi tana marabtarta da hannayenta,abinda ya sanyata qarasowa cikin hanzari ta zauna jikin mammina din sosai tana aza kanta saman kafadarta.

"Maraba da isowa........tuba nake.... .Allah ya qara miki nisan kwana......ubangiji ya kauda maqiyanki daga duniyarn......"

"Ya isa haka" Mammina ta dakatar dashi tana sanya hannunta cikin na akhnan.

"Ka bamu guri haka nan......zan gana da diyata......zan nemaka wani lokaci"

"An gama Allah shi biya miki" Ya furta yana miqewa da dukka tsahonsa,sannan ya sanya kai yana fita ta qofar da zata fitar dashi ta bayan sassan mammina din.

Sai data tabbatar da gushewarsa a wajen,ba tare da wani motsi nasa ba sannan ta dubi akhnan.

"Tun daga yanzu na fara kewar wannan diyar tawa,daya daga cikin abinda ke jefani tunanin yadda rayuwa zata kasancemin bayan na kaita gidan mijinta". Wani murmushi ya subuce ma akhnan din,murmushi nan nata me tsadar da zai wahala kayi mu'amala da ita na wasu taqaitattun lokuta ka samu ganinsa. Koda yaushe fuskarta a tsuke take,zaka dauka kaf rayuwarta batasan wani abu waishi farinciki ba.

Hannunta ta zura ta bayan mammina ta rungumeta sosai.

"Kune kuka takura......ku kuka matsa mammina......me nake da buqata a rayuwata bayan kun yimin komai.....kun gama min komai......sannan kun mallakamin komai". Kai ta girgiza a hankali.

"Yaro yaro ne......yaro man kaza......baa nan gizo ke saqar ba.......amma na gaba kadan zaki fahimta......akwai wani abun da kike buqatar ki tafi dashi Niamey?.....bayi hadimai ma'aikata ko wani abu na buqatar rayuwa?". Manyan idanunta ta lumshe,tana jin dadin yadda take nuna damuwa da komai daya shafi rayuwarta,tana jin dadin yadda take kula da dukka buqatunta.......tasha banban da nisan tazara me tarin yawa tsakaninta da momma safiyya.........tazarar da bata jin a nan kusa akwai wani abu da zatayi wanda zai sanya ta taddota.

"Babu......babu komai mammina.......saidai zanyi kewarku" Ta qarasa fada tana sake dora kanta saman kafadarta.

"Muma zamuyi kewarki biftu.......amma zamu kasance ta cikin waya.........dole ne ya zame miki nauyi da kuma wajibi bawa kamfani kulawar da dukka ta dace........shine zuciyar duk wata kadara da dukiyarki akhnan........bake kadai ba.......hatta da me martaba ma". Kai ta jinjina,sannan a hankali ta zame kanta daga kafadar mammina din sannan ta miqe.

Da kanta ta bude mata seat din baya,mazauni na musamman dake gareta cikin lafiyayyar motar qirar BMW X5 fara qal wadda tasha banban da kalolin sauran motoci ukun dake dauke da masu tsaronta da kanyi mata rakiya zuwa Niamey,wasu su zauna a can,nacan din kuma su dawo nan agadez sai tayi wani zuwan sai a sake canza mata da wasu cikin amintattun hadiman da masarautar agadez ta aminta dasu.

"Allah ya tsaremin ke......ya kawar da dukkan wani abunqi"

"Ameen mammina". Ta fada a narke kaman yarinyar qarama. Matsawa mammina din tayi tayi kissing hannun akhnan din,sannan ta maida dubanta ga aisa.

" Aisa" Ta kirata kai tsaye da yanayin daba kasafai ta fiya kiranta ba.

"Naam mammina"

"Ki kulamin da diyata" Ta furta da yanayin dake nuna mata da gaske take. Kai kawai ta jinjinawa mammina din tana dauke kanta zuwa wani sashe na daban,kafin mammina ta matsa da baya ta rufe musu motar,suka fara motsawa kuma suna fara fita daga masarautar agadez. Duk inda zasu gifta da motocin tun daga cikin gidan har zuwa wajen gidan sai kowa ya bada hankalinsa,ya kuma matsa baya cikin girmamawa yana yi mata addu'ar sauka lafiya da wani irin ladabi tamkar tana ganinsu.

Shuru motar ta dauka sanda suke nufar mano dayak international airport(AJY),inda ta saba tashi a nan,sauran hadimanta kuma su juya subi ta hanya zuwa Niamey din.

Kowa da tunanin da yakeyi a ransa,saidai duk da haka waya ce a hannun aisa tana danne dannenta,wanda fiye da rabi chart takeyi ita da shehinaz da take bata tabbacin yau din ko gobe itama zata baro zinder ta shigo Niamey din. Akhnan kuwa idanunta nakan hanyoyi da shimfidaddun tituna kyawawa da suke wucewa. Cikin ranta take sake jinjinawa mahaifinta da mulkinsa,ya jawowa qasar agadez ci gaba masu tarin yawa,irin ci gaban da koda wadanda suka jima saman karagar mulkin basu samar da koda rabin rabin hakan ba.

Duk da wannan nazarin da takeyi hakan bai hana zuciyarta fadawa cikin tunani ba.....abubuwa da dama dake cunkushe a kwanyarta,tana kuma tunanin hanyar warwaresu.

Qaramin tsaki taja ciki ciki,a yanzu tana jin energy dinta dukka na aikinta......bata buqatar sulalar dashi da kwaranyar dashi akan wani abu can da bashi da cikakken muhimmanci ga rayuwarta,don haka saita fidda daya daga cikin wayoyinta tana jin bari ta duba sashen saqonnin email dinta ta rage yawan saqonnin da suke jiranta.

Saqo na farko na biyu......ana uku idanunta suka sauka ga adireshin saqon da ya sanyata jan wani qaqqarfan tsaki da yaja hankalin aisa. Daga kanta tayi tana duban akhnan da taqi koda duban sashen da aisa din take,har yanzun idanunta nakan wayar,don haka itama aisa din saita bagarar taci gaba dayin abinda take.

Tsaki na biyun data sake ja shi ya sanya aisa yin magana wannan karon,ta aje wayarta saman cinyarta ta soke yatsunta guri guda tana dubanta.

"Wanda bai kashe zomon ba.....kuma ko ratayar zomonma ba'a bashi ba......na meye zaa cika masa kunnuwa?" Tayi maganar tana tsuke fuskarta guri guda.

Sau daya tak ta daga kai ta kalli aisa da almond shape eyes dinnan nata dake gayawa aisa ta tara maganganu ne da yawa qasan ranta amma miskilanci ya hanata fada,sai tayi abinda aisa din tafi tsana wato maida kanta kan wayarta.

Mutum biyun nan dai..... Mutum biyun nan da har kullum suke hargitsa zaman lafiyar wayarta. Zai wahala ta dauki wayarta ta gama dukka shige da ficenta a waya ba tare da taci karo da saqon dayansu ba. Ta rasa mene ne hakan?,wai tamkar ita daya ce macen da tayi saura a duniya ne?.

"Babe........the pic was so hot......thanks to aisa". Cak ta tsaya tana sake maimaita karanta saqon da ya fito daga gurin naadir......haifaffen qasar nigeria da kasuwanci ya kawoshi niger din.

"Thanks to aisa?" Ta karanta maganarsa ta qarshe. Jikinta ne ya bata wani abu,sai kawai ta sauka ta koma zuwa account dinta ba IG. Private account ne da ba kowa yake da ikon ganin abinda kake aiwatarwa,sai wanda kayi accepting dinsa,wanda duka duka nata mutanen da tayi accepting basu da yawa,ciki kuwa harda aisa.

Kai tsaye ta wuce ga sunan aisa din,ta zarce kan abubuwan da tayi posting a dukka satin.

Babban hotonta yana daya daga cikin abubuwan data saka a satin.......hoton daya samu likes da comment me tarin yawa wanda kusan mafi rinjaye da harshen faransanci ne. Hotuna ne guda biyu,guda daya nata,dayan kuma ta da aisa ne a diori hamani international airport,ranar da suka baro Niamey kenan zasu shigo zinder. Tana sanye da wata doguwar riga cikin ire iren dogayen rigunanta navy blue. Sosai color din rigar ya amshi fatarta da take jazur kaman zaka latsa hannunka jini ya fito,hakanan eye glasses din da tayi amfani dashi me duhun kala ya sake ajiye mata wani kyau na musamman,hancinta da zagayayyar fuskarta sun sake fallasa sirrin kyanta. Bata taba zaton haka rigar tayi mata kyau ba sai a wannan hoton,sai wani abu yazo ya tokare mata a wuya tana bin comments din mazan dake qasan hoton nata tana dubansu a matsayin sakarkarin da basu san ciwon kansu ba. Tarin sakarkarun kuma data bawa damar kalle fuskar da ita karan kanta wadda Allah ya mallakawa ita darajarta take gani,wannan wanne irin aikin watsar da mutunci aisa ta jawo mata?.

"Me kika aikata kenan haka aisa?" Ta jefa tambayar kai tsaye ga aisa din tana haska mata fuskar wayartata me babban screen dake riqe a hannunta daidai sanda motarsu ke kutsa kai AJY.

Fuska aisa ta tsuke itama,tana dinke girar sama da qasa.

"Mene kuwa?,shikenan mutum bazaiyi nishadi ba?" Ta jefa mata tambayar itama tana rutsata da nata manyan idanun. Kallon aisa ta sakeyi sosai sannan ta janye wayar a tsakaninsu ba tare data janye daga dubanta ba.

"Supprime Γ§a(Delete it)"

"Baiyi niyya ba" Aisa ta fada hankalinta kwance tana maida dubanta ga qofar tana qoqarin budewa jin motar ta tsaya.

Bata ankara ba ta tsinci hannun akhnan saman cinyarta,ta dauke wayarta cak tana jefata cikin handbag dinta,daidai sanda aka bude mata side din da take,abinda ya hana aisa yunqurin amsar wayar kenan,don ita dinma sarautar na yawo a jininta,kuma tasan yin wani motsi ko yunquri zai iya zama abun kallo a tsakaninsu ko ya zubda musi kima.

"Karki yunqurin yin wani abu mara da wayata biftu.......mallakata ce".

" Idan banyi ba tabbas ban haifu ba cikin sultane" Ta amsa mata ba tare daya waiwayo ga aisa din ba.

First class take zama a duk sanda tahau jirgi komai qanqantar tafiyar. Tunda kuma suka shiga din ta karanci akwai wanda ke shirin takura mata.

Matashine da jin ke zagayawa a jikinsa tare da nuna zallar quruciya kudi da kuma wani sassanyan kyau. Yanayin kallon qurillarsa ya gama takurata kafin sannu a hankali ya qona mata rai,sai kawai ta fiddo eye glasses dinta masu duhu ta lullube qwayar idanunta dashi,sannan ta miqe bayanta jikin kujerar da take kai,ta kuma buda madame Bovary na marubucin nan dan qasar French Gustave Flaubert. Duk da novel din ya qunshi soyayya......amma jarumtar star din novel din,attitude nata da character nata sunyi mata sosai.

Sanda jirgi ya daidaita sararin samaniya da tafiyar da bata haura awa daya ba da mintuna ta rufe novel din,tana jin yadda shauqin labain ke dibanta,amma sai ta zabi ta bawa kwanyarta wani space nayin shuru ta zauna silent don bawa kwanyarta wata qaramar nutsuwa




zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*


*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer πŸ‡³πŸ‡ͺ*

*00239166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*MY NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261


*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITAπŸ‘‘*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
πŸ’Ž *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*πŸ’Ž


*H U G U M A*


PAGE 11



Matashine da jin ke zagayawa a jikinsa tare da nuna zallar quruciya kudi da kuma wani sassanyan kyau. Yanayin kallon qurillarsa ya gama takurata kafin sannu a hankali ya qona mata rai,sai kawai ta fiddo eye glasses dinta masu duhu ta lullube qwayar idanunta dashi,sannan ta miqe bayanta jikin kujerar da take kai,ta kuma buda madame Bovary na marubucin nan dan qasar French Gustave Flaubert. Duk da novel din ya qunshi soyayya......amma jarumtar star din novel din,attitude nata da character nata sunyi mata sosai.

Sanda jirgi ya daidaita sararin samaniya da tafiyar da bata haura awa daya ba da mintuna ta rufe novel din,tana jin yadda shauqin labain ke dibanta,amma sai ta zabi ta bawa kwanyarta wani space nayin shuru ta zauna silent don bawa kwanyarta wata qaramar nutsuwa.

Dan qaramin blanket da aka basu tayi amfani dashi ta qarasa lullube jikinta,sai fuskarta kawai dake a waje. Ta liqe idanunta da abun rufe idanu tana juyar da fuskarta window tana sauke sassanyar ajiyar zuciya.

"Biftu" Aisa ta kira sunanta a kausashe. Yi tayi kamar bata jita ba,abinda ya sake sanya aisa maimaita kiran nata har sau uku amma tayi burus da ita.

Hannu tasa ta zare abunda ta rufe idonta dashi,cikin hasala tana cewa.

"Don wulaqanci kina jina ina kiranki?.........ki bani wayata saikici gaba da kurmancinki ba damuwar aisa bane" Duk maganan da aisa din keyi idanu kawai akhnan ta zuba mata harta gama. Sai ta qarasa yaye blanket din kawai ta zauna sosai,ta dauki jakarta da sauran tarkacenta ta raba aisa din tana wuceta.

Da kallon harara aisa ta bita,jirgin ya dauki shuru kowa yana harkar gabansa,bataso kuma tayi abinda zaiyi kiran hankalin mutane a kansu,don haka taja qwafa qasa qasa,tana tunanin meye zata mata da zai zafafeta itama ta rama?.

Murmushi ya saki a hankali ganin ta koma can wani seat din daban ta narke cikin kujera tana maida blanket dinta,saidai yanzun bata lullube idanunta ba,a maimakon haka ma saita maida dubanta ga window tana ganin yadda suke keta gajimare.

A nutse ya miqe yana barin seat dinsa,ya taka a hankali zuwa inda take,wanda har ya isa din bataji motsinsa ba sai daya zauna kusa da ita.

"Hey cutie" Ya fada da siririyar muryarsa da kadan ya rage ta soma kamanceceniya data mata saboda zaqinta. Da hanzari ta waiwayo tana watsa masa blue eyes dinnan nata. Kallon daya saukar masa da wani irin matsanancin faduwar gaba.

"Tsarki ya tabbata ga ubangiji ya furta

7 / 21